
Daada sai da tayi kwallah da Taga Zaratan ya”yanta nata agabanta Bata Zata ba sai dai ta gansu kwatsam Baffa Kabiru ya zube gabanta yana kuka yana Rokonta gafara Daman Wlh Aranar ta yafemai komai ita bata Rikesa ba Bacinrai ne ta Rumgume sa Tana Fadin ta yafemai Duniya da Lahira.
Da kansa ya Fadama Daada Hukuncin Daya Dauka kan Asma”u bai Fadamata Sa”insansu ba yadai Fadamata ta shigar da Complain Zatayi kararsu,Shiyasa ya Saketa Daada bata ji Dadi ba sosai tayi mai Fada ta kuma ce Maza maza ya maida Matarsa Dakinta nan yake Fada mata Zuwansu Abba da jiya da Abunda ya kawosu da yadda suka Shawo kansa ya Maidata Dakinta da Sharadin Daya Saka mata.
Daada taji Dadi Farinciki ya Cikata ya”yanta sun Hada kansu ta Dinga Saka Musu albarka su da Zuru”ansu Ta ce kuma Sharadin Baffa Kabiru yayi Daidai gwara ya Rabu da Asma”u Tayi Hankali da kanta ammh in yayi Saurin Dawowa da ita Zata ga ta isa ne kuma Mtsayinta yakaine.
Daada Ranar Tare da ya”yanta taci Abinci Cikin Soyayya da kauna Tana Sharan Kwallar Tunawa da Marigayi Hamisu Dukku Allah ya jikan Maza Domin Tabbas Mazaje sun kwanta Dama.
Kiran Sallar azahar ya tadasu Daga gaban Daada suka tafi masallaci su kai Sallah suka Dawo suka iske Daada na Sallah bata idar ba nan suka Zazzauna suna cigaba da Hiransu Cikin Hiran ne Baffa Kabiru ya kalli su Abba yana Fadin”Malami Mustpaha nace ba..?ina mganar Tarewan ya”yana ya aka kwana ne Imran da mai sunan Daada..!?
Ya fada yana kallonsu Daddy da Abba suka Kalli juna cikin jin Dadi Lalle Ya Kabiru ya Sauya..!
Abba yace”Mustpaha yacemin wai Mganata tana Hannun Imran..Ammh ai naga Daada ce Zata yanke Lokacin ko..?
Daada Data Shafa adduarta bayan ta idar da Sallah ta juyo Cikin Fara”a Tana Fadin”A”a mgana bata Hannuna ai na gama nawa Tun a wanchan karon na Sanar daku ku zaku Tsara Komai nace dai ayi Biki na al”ada na Fulani ku bama Kowani bangare Dama ni ina nan Dukku bana bukatar kowa sai dai aturomin ita Mai sunan Tawa kafin Tarewar ina son ganinta..!
Suka Jinjina kai Dukkansu kafin Daddy yace”Insha Allahu Daada Zata zo..Dayake Text suke yi a makaranta kuma ina jin da sun gama sai Jarabawar Second Semester..!
Abba yace”Eh hakane ma naji suna Fada ita da mai sunan Autan Daada Munari..!
Baffa Kabiru yace”To ai sai mu Tsaida Lokaci ko .?me ake jira ai anyi mai Wahalar tunda aka Daura auran gwara ayi komai Cikin Lokaci Ta tare Dakin Mijinta mun gama Dasu sai muji da Sauran yaran namu gama Babbansu nan Malami kaima aure Zan maka..!
Gabadayansu Dariya su ka saka Harda Daada Abba na shafa kansa yace””Haba dai Yaya ina ni ina aure Tsofai Tsofai dani ko Daada.?
Ai ma barma yaranmu..!
Baffa Kabiru yace”Ban yarda ba..Daada ki Zama Shaida in akwai Wacce Daga barayinki kika ga ta Dace muyi mgana zan Biya Sadaki da komai kabar cewa ka Tsufa yadda kake din nan sai ka auri yarinya Danya Sharaf da ita Wlh..!
Dariya suka kara sawa Gabadayansu Abba na Fadin”A”a Allah ya Rabani da abun kunyar auro Sa”ar Munari..!
Daada dai Dariya Kawai take yi Ranta Kamar Farar Takarda Saboda Farinciki.
Baffa Kabiru ne ya kauda mganar da Cewa”Ina jinku..Ya kuke ganin Za”ayi..?
Daddy yace”Ni mun yi mgana da Ya Malami nace mgana tana Hannun Imran ya tambayesa yaushe yake son Tarewar? Tunda shine Mijin kuma Dukkan Hakki na kansa ne ni ina da a Shawaratace da an Bari nan da Wata Hudu zuwa Biyar Tunda bai dade da Fara aiki ba yanzu kan Lokacin komai ya Daidaita sai a Shirya Bikin Tariya ga Ya Malami ma Monday zai Fara shiga office shima kan Lokaci abubuwa sun Daidaita itama Inteesar sun gama Jarabawa sun shiga Level 2..!
Daada Nadaga gefe tace”Mustapah yayi Tsawo..nifa so nake kafin na Mutu na Fara goyan ya”yan Jikokina abayana..!
Baffa Kabiru yace”Zaki goya da yardan Allah Daada ba Mtsala indai kan Kudi kake wannan mganar Mustapha ba Ruwanka kaida Malami ni nine nan Uban ango kuma Uban Amarya na Daukin Nauyin Siyama Imran Gidan da zai zauna da Kayan lefe ita kuma Inteesar Kamfanin Marhaba Zata zo ta kawata mata Gidanta da yardan Allah ni nawa Bangaran kenan a Mtsayina na Uba..!
Ai Abba da Daddy sun kasa mgana Daada ce tace”Allahu akbar..Allah ya jikan Mahaifinku..Allah yasa ya Huta..Ka kyauta kabiru..Sai yau ka Nuna min ko bayan Raina kai Uba ne ga Duka kannenka da ya”yansu Allah yayi muku albarka..!
Suka amsa da Ameen dukkansu.
Abba yace”Imran nada gida Bankin Daya Fara aiki dasu sun basa Gida Da Mota Kyauta..Ya kabiru Abubuwan zasu maka yawa..!
Baffa Kabiru yace”Bakomai kada na karajin wani cikin ku yace wai Abun zai min yawa don Uba yayi ma ya”yansa Wani abu Laifi ne..?
Ko kuwa ku in kumma Sajida ko Umaima wani abu a Mtsayinku na Iyayensu zan ce wani abu ne..?
Gabadayansu suka girgizamai kai.
Shi kuma sai ya Kada kai yana Fadin”To kada ku kara Cewa komai..Yanzu abunda Za”ayi kai Malami kiramana Imran din muji yaushe yake son Tarewar..?
Abba bai yi gaddama ya Fito da Wayarsa ya Lalubo Lambar Imran ya Kirasa sai da ta gama Ringing bai Dauka ba kana ya Biyo bayan Kiran Abba din..
Abba ya saka a wayar a amsa kuwwa Suka gaisa da Imran Dake Cikin Office dinsa yana Tsaka da aiki duk da ya Kusa tashi Karfe 3pm na Rana zai koma Gida.
Abba yace”Imran yaushe ne kake Tunanin ya kamata Inteesar ta tare a Dakinta..?
Imran ya Dakata da Latsa Computer Dake gabansa kafin yace”Abba meyasa kowa ke Tambayana ne..?Haka itama yaran nan su Munari suka Turo ta Tana min mgana na Dauka ku zaku yanke Lokacin..!
Abba yace”Eh duk da haka kaima aji Ra”ayinka da Lokacin Daka ke so..!
Imran yayi Shuru yana wani Tunani kafin yace”Abba Kuna Tare da Daddy ne..?
Abba yace”Eh Harda Baffanka Kabiru muna Dukku gaban Daada..!
Imran ya karkace kai aransa yace na gano komai wato su Abba sun je Daidaita Daada da Baffa Kabiru ne
Yamutsa Fuska yayi kafin yace”Ni fa Abba bani da ta cewa..I think ba wani abu ko duk abunda kuka yanke is ok..!
Abba yace”Kada ka damu ka Dai Fadi Lokacin..Ga ma Baffanku nan yace shine Uban ango da Amarya Hatta Lefe ya Dauke maka..!
Imran ya Zaro ido Cikin Mamaki kafin yace”Ni din..!
Abba yace”Kwarai da gaske Haka yace..!
Imran bai samu Zarafin mgana ba Baffa Kabiru ya karbi wayar Hannun Abba yana Fadin”Son..Baffan ka ne Time kawai zaka Fadi Lokacin da ka ga yayi maka daidai..Baka da Mtsala ko Katin gayyata ban ce ka Bugo ba ni Dakaina zan yi komai Lokacin kawai muke son ji..!
Imran yayi kasake yana ganin abun mamaki kamar a mafarki sai dai bai yi Saurin Saki ba Saboda bai gama Tabbatar da abunda Zuciyarsa ke Fadamasa ba.
Cikin Dan Kaushinsa yace”Da ka barshi Zan yi komai da kaina Insha Allahu..!
Baffa Kabiru bai Damu ba Daman yasan Za”ayi haka shiyasa yayi Mirmishi kafin yace”Ba ruwanka Nauyin Uba Daya Rataya akaina zan Sauke Lokaci kawai nake so naji..!
Imran bai da ta tace illah ya Muskuta yana Fadin”Karshen wannan Watan a Think is ok..!
Baffa Kabiru yace”Is ok..Allah ya kaimu ya nuna mana Allah ya bada Zaman lafiya..!
A saman lebe Imran ya amsa kafin ya Katse wayar.
Shuru yayi yana wani Tunani kafin yace a fili”Su Baffa Kabiru an ji wuya..!
Yafada yana yar Dariya afili,Ko Dazu Sagir sai da yayi mai mgana da Safe kan mganar Lokacin Tarewar bai bashi amsa ba,Sagir din kuma Daman Munari ce tamai mgana ta Fadamai yadda Imu sukayi da Inteesar Sagir yace ai mganar banza ce zai mai mgana Dayayi mai sai bai wani bashi Amsa mai kyau ba.
Abba Kwana Daya sukayi a Dukku Ranar asabar kowa ya kamo Hanyar Gida,Baffa Kabiru Direbansa Daya kawosa ya Daukesa zuwa Abuja Bayan sun Tsaida lokacin da Imran din ya Fada nan da kwana Ashirin da Biyar Abba da Daddy Motar Haya suka Shiga suka koma Gidajensu,Su ka tafi suka bar Daada Cikin jin Dadi Tana saka musu albatka.
Zuwa Washegarin Ranar dasu Abba suka Dawo Mganar Lokacin Tarewar Inteesar da Imran ta yada Dangi da Abunda Baffa Kabiru yace Zai Dauki Nauyi,Kowa yaji sai yaji Dadi ana ta Fadin ai da haka yake yi da Ba asamu waniFada acikin Dangi ba.
Daddy ya Fadama Umma ita kuma ta Sanar da yan”uwanta su Munari abakin Anty Safiya sukaji Shima Abba ne ya Fadamai Ya yusuf Imran dai bai ce mai komai ba,Sagir kuma Mama ta Fadamai shima Imran bai Fadamai ba Shiyasa ya Sharesa.
Ranar Monday Abba ya Fara Shiga Office An samo mai Direba Musa wani Dan kasan Layinsu su Sagir ne Matashi ne mai mata Daya da yara Biyu,Zaratan Ya”yansa suka Rakasa Yusuf da Imran da Munari da Inteesar Harda Anty Safiya suka Raka Abba Har zuwa Babban Office dinsa na Department of Physhology.
Sukayi addu”a suka saka albarka kana Kowa ya wuce Wajen aikinsu Munari da Inteesar kuma Daman Gida suka zo suka wuce Department dinsu suka wuce suna da Test,Munari sai Rawan jiki take suna ta waya dasu Hafsah suna ta Tsara Event din da zasu gudanar tun jiya Munari ta Bude group a Manhajar WhatApps mai Suna IMSARâ¤ï¸ðŸ’« ta saka Hafsah,Da Nasara da Tasleem da Sagir.
Inteesar bata ce komai ba Gabadaya zullumi ya isheta Tana Tunanin Saura kwanaki kadan su Zama Miji da mata na Hakika Tsakaninta da Imran su Zauna agida Daya su kadai a mtsayin miji da mata.