
After 10 days
Haka Rayuwar Auran Imu da Inteesar ya Cigaba da Gudana Kullum da Safe in Tare zasu fita Zata Dafa musu Ruwan Zafi su sha Tea kafin su Fita in kuma Batare zasu fita bata da Jarabawa da Safe shi kadai yake Fita Inteesar na kwance ma sai ya tasheta Wani Lokacin Har Yau da suke kwana Goma da aure Inteesar bata Fara Girki ba sai dai Tasha Tea taci kayan Snak,in Tana Gida domin in Ta shiga makaranta Munari take bi zuwa Gidan Chan take Wuni sai yammah Tayi in Imran ya Dawo shima nan yake Sauka sai Dare suke Dawowa Gida da sun Dawo sai barci kuma Har alokacin kowa Dakinsa yake kwana babu abunda ya Sauya.
In basu Fita tare ba Yana bar mata Kudi in Lokaci yayi sai ta Kulle Gidan ta Fita ta Hau adaidaita da Farko Har Biyama Munari Take yi Abba ya Hana yace Kada ya kara gani Imran bai ma Sani ba yana Wajem aikinsa.
Shi cin Abinci bai Damesa ba Barsa da Shan Tea da kayan Marmari Abinci sai yaga Dama yake ci shiyasa har yau bai Damu da rashin Fara Girkin Inteesar baisama san wai Ta Fara Girkin ba Ballatana yayi mata mgana Shi yana ganin akwai komai in Tana jin yunwa tasan yadda Zatayi Shiyasa bai Taba Damuwa da Rashin Fara Girkinta ba.
Kuma ba wanda ya kawo musu Ziyara ballatana yaga aikin da suke yi Daga Imran din Har Intee sai addu”a bamai Sauke Hakkin Dake kansa.
Ita bata komai sai Kwanciya in bataje makaranta sai Ciye ciye kayan snka da Shan Tea sai Tayi karatu in Tagaji Ta Danna Waya kayan kallonsu ba a Hada ba gogan Kallo bai Damesa ba…shidai barsa in ya Dawo aiki Tayi mai Sannu da zuwa ya amsa ya Shiga yayi wanka ya Sauya kaya zai Fito Falo ya zauna yana aiki Bisa Laptop aiki Dayasa yake sa ka Inteesar Wanke kayan Marmarin Dayakan Shigo dasu ta sakomai afilet da Fork karama yana aiki yana cin abunsa Hankalinsa kwance ita kuma Tana Gefe Tana Danna Waya tana Hadawa da Ciye Ciyenta ko ajikinta In Tagaji Tamai Sallama Ta Kwashi littafanta Zuwa Ciki,ko kuma Tayi waya dasu Umma wannan Kullum ta Dinga Kira kenan tana Musu Shagwaban sun ki zuwa ita da Daddy Umma tace Gotai Gotai da ita agidan yarta Daddy kuma yace Intees tasha Kuruminta in zai zo Tare zasu zo,Umma fa har hana Daddy take kiran Inteeear ammh shi ba Ruwansa Wani Lokacin suna Waje Daya da Imran in yace ina Mijinki sai ta mikamai su gaisa da Daddy Har su Taba Hira Umma sai dai ta Rike baki Tana kallon Wannan aikin.
Shidai Imran tunda dai Inteesar bata Rainasa ba Alhamdullilah..Kowa yayi abunda yaga Dama ba Takura.
Shiyasa bai Taba kallon hakan da sunan Wani abu ba yana ganin hakan Shine Daidai.
Inteesar bata Taba Zaton Imran bai daina shan Taba ba,Sai ranar Dataga yana shanta bayan ya Dawo yana Zaune yana aiki Bisa laptop dinsa Shi yama manta da ita Kakarinta yaji kawai ya Juyo yana kallonta yaga Tana Toshe Hanci Gira ya Dage mata yana Fadin”Ke nama manta Dake fa..a falon nan..Bari na bari sai na koma Ciki na kunna..,!
Yafada yana Kasheta saman Farantin Daya gama shan kayan Marmari..
Inteesar tace”nifa na Dauka ka Daina sha Kwatakwata Har ina Celerabration..!
Imran sai da yayi Dariya kafin yace”Su Celebration Manya.Haka Sagir yace min jiya daya ga ina sha..Daman ai bamu yi Dake Zan Daina Shafa ba Kuma ita shanta ai Lokaci ne kuma yanzu Lokacina Duka na gwannati ne Kalilan ne nawa..
Bata Fuska Tayi bata samu Damar Mgana ba ya Katseta da Fadin”Na Rage sha sosai..Fiye da baya..Kuma in kinsan kina jin Amai u better go to ur Room..Allah in ki kayi min amai anan Wajen kinsan Sauran..!
Tura baki Tayi batayi mgana ba Shi kuma sai ya kauda kai yana Danne Dariyansa yarinyar nan in ya biyemata Tabaranta Zata Rika yimai kala kala.
Ranar da suka Cika Sati Biyu da Tarewa Baffa Kabiru yazo Kano, Saboda Imran da Inteesar bai Kwana ba Aranar ya Juya bayan ya Taka har Gidan ya Cikasu da Tarin Nasihu da Fatan Alheri Imran bai Taba jin Nadamar abunda ya aikata ba Sai Ranar yaji kunya Baffa Kabiru Rana ta Farko ta kamasa anya ya Chanchanci Wannan Kyautatawar ga Baffa Kabiru..?shida ya Sakarmai ya..?
Bai Rikeka ba sai m karin kyautatawa Daya Biyo ba Imran yaji kunya saai Dai Ya yi Fuska kamar babu Abunda ya Faru Tare da Abba suka zo suka kara ganin Waje suka saka albarka.
Baffa Kabiru duk ya Rame yayi wani Iri kawai Karfin Hali ke tafe Dashi,Ga Damuwar Dayake Ciki ba Asma”u Tare dshi,Ga Khamis ba”a Samun Wayaarsa kwata kwata Ga Sajida Tana makaranta cikin Damuwa duk da bata Fito ta Fadamai ba shi ya sani wannan Raunin nata bamai Cike mata shi Sai Imran shi kuma ya Riga Yayi mata Nisa har Abada.
Wadandan Damuwan suna Ransa Kawai Karfin Hali ne da Tsabar Jaruma ke tafe Dashi yake kuma Tsaye da Kafafunsa alkawari ya Daukar ma Kansa bazai nemi Asma”u ba sai in itace ta Nemesa ba shima din Sai ya yarda da Nadamarta,ko yace bai azabtu da rashinta ba yayi karya Asma”u ai Soyayyah Ta Hadasu ba Kiyayyah ba kuma basu Taba Samun Irin wannan Babban Mtsalan ba sai wannan karom ya sani kamar yadda yake Cikin Wani Hali itama Tana Cikinsa Har kuma zuwa Lokacin bai ji Daga Justice Tafida ba Daman yasan bazai Nemesa ba Ko shi ya Nemess zai ce abunda suka yanke ma kansu Daidai ne shi bazai ce komai ba Tunda Ra”ayinsa ne.
Daga shi sai Umaima sai yan aiki suke Rayuwa Sajida basu gama Exam ba ammh yace mata da Zarar sun gama Ta dawo gida kada ma Tace Zata Zauna a makaranta ita kuma taso ta Cigaba da Zamanta a makaranta Tana Jinyar kanta ba wanda yasan Halin Datake Ciki.suna Waya da Mami Lokaci Bayan Lokaci itama Hawan ajini Duk ya Fadar da ita Karfin Halinta kawai an fa ta Fara Sarewa an Kwarari Wata na Biyu bataji Daga Kabiru ba ta Fara Saki ta Fara Zama Tana yima kanta Tunanin Ina Mafita.?shin ta ina ta Kuskure..?
Shin Tana da Son kai kamar yadda aka Fada..?tana so ta Fahimci kanta da kanta kafin ta yanke ma kanta Hakunci.
Washegarin Ranar da Baffa Kabiru yazo Ranar Monday Daga makaranta Munari ta matsama Inteesar suka Dawo Gidanta Munari ta yi mamaki Data shiga Kitchen din Inteesar ta Bude Fridge Taga Nama da Kifi har sun kankare ga abubuwan amfani nan duk bata taba amfani Dashi ba ai Batama gama mamaki ba sai da inteesar tace mata bata Fara aiki ba Daga dafa Tea shikenan take yi Munari ta Rike baki Tana Fadin”Baki Fara Girki ba..?
Inteesar ta gyadamata kai Tana Fadin”Eh ya imu bai ce na Fara ba kinsan baya cin abinci..Ni kuma kinga Gida muke wuni..,!
Munari ta Girgizakai Tana Fadin”Wlh sai yau na kara yarda kina son ya Imu ammh bakisan Halinsa ba..Shine zai ce ki Fara girki sannan ki Fara..?
Inteesar ta daga mata Kai Tana Fadin”Eh mana kawai bai ba in na Fara ina asara ga bansan kowa anguwan ba Shuru ko almajirai babu kuma Kinsan ba kyau Zubar da abinci..!
Munari ta Saki baki kawai kafin Tace”Uhm..Baki san Waye ya Imu ba..Zaki Shekara shekaruma ahaka Indai shi kike jira yace ki Fara Girki..?shi ina Ruwansa zai ma Taba Tunanin ya kamata ki Faran ne..!
Inteesar tace”Kingane..Allah kinsan bai cika Damuwa da abinci ba im na Dafa na Dinga asaransa kenan..!
Munari bata kara mgana ba Indomie ta Dafa da Hanta taci Ta hada da Lemo Bata yarda Takai Dare ba sanin Halin Imu Wlh bazai maidata Gida ba Dama Ya Yusuf ne zai ce kafarta Data kawota Ta maidata..
Munari na komawa Gida ta Kira Umma ta Fadamata Komai na Halin da Inter ke ciki Domin tasan Umma ce kadai Zata iya mata mgana taji.
Umma ta saka Salati ta Dire Wato Dai Inteesar ta auri miji Daidai da ita in Iskancin ne ya fita zaune kawai suke bamai ma wani Fada.
Ai bata bari Daddy yaji ba ta Kira Inteesar aranar ta mata Fada kaca Kaca Inteesar na Tura baki Tace ma Umma”Shifa Umma baya cin abinci Fruit yake sha kullum sai Tea kuma ai ina Dafamana..kuma bai ce min na Fara Girki ba ni..!
Umma kamar Inteesar na Kusa da ita ta kamata da Duka Zaginta Tayi kamar Tana ganinta Kafin tace”Ji Sakarci Jira Kike sai yace ki Fara..?ai kinsan Wanda kika aura Shine kike Zaune ya Kiraki yace ki Fara Girki kin Taba Dafamai kika mai Tayi yace A”a..!?
Ta girgizamata kai Tana Turl Baki Umma Tace”To banda Wawanci wai kina Zaune bakya girki ko to me kuke ci ko nace ke me kike ci..,?
Inteesar tace”Munari na ke bi zuwa Gida in mukaje Exams..Da Daddare ya Imu yaje ya Daukoni..!
Umma ta kara Saka Salati kafin ta koma Lallashi da ban baki Tana Fadin”Ki Daina zama haka Kin ji Intee yanzu kin Girma Nauyin Ciyar da Mijinki yana kanki..Duk da bayason cin Abinci in kika Girka kika Matsamai ko Saboda ke ai zai ci ko..?
Inteesar tace”Eh zai ci Umma in yaga Dama..!
Umma tace”Ki Fara Girkin ki bakomai Watarana sai Labari ai kina da komai na Cefane ko..!?
Inteesar tace akwai komai Ya Yusuf ya cika mata Fridge da Cefane,Umma aranta tace shima yasan halin kaninsa Inteesar taji Fadan Umma ta kuma Kiraa Mama tace Mata tazo ta kara jan kunnen Inteesar to bata zo ba ammh Ta mata Waya itama ta Kara mata Fada tace Insha Allahu Zata gyara sai dai ta Kira Munari ta Zageta ta ce mata Munafuka Tunda tasan ita ta Hadata da Umma Munari dai tana ta Dariya.
Washegari ta Fara Girki Ranar basu da Exams ana Saka musu Interval Sosai,Sai da Imran ya Dawo Wajen aiki ya iske tayi abinci jalop din Shinkafa da Kifi.
Mamaki ya kamashi yace waya sata girki Tana Shagwaba tace ba Umma bace ta Kirata tana mata Fadan wai bata fara Girki ba kuma ai shine bai ce ta Fara ba..!
Dariya yasha sosai ranar agaban Intee Wai Daman shi Take jira..!ai in ta barsa shifa ya manta da ma wani Girki bai kuma Taba Tunanin yace ta Fara ba sai da yaji Dadin mganar Umma ko Bakomai ai ita Macece Ranar yaci kadan dai Tunda ta Girka sai da yace ta Rika Girkawa Kadan iya Cikinta Tunda ba Lalle bane ya Rika ci kullum
Haka kuwa takeyi kadan Take Dafawa shima Ranar Datake gida in kuma ta shiga makaranta Munari take bi Gida Bata Girki Ranar Umma da kanta ta Kira Abba tace mai ya Faffataki Imran da Inteeear su daina Taremai a Gida ta kawomai Misalai Rashin Dacewar haka Harda na Rashin Girkinta tace Koda Imran yazo shi Namiji ne ita fa Mace ce kuma matarsa Saboda Haka Ta Zauna a Dakin Mijinta wannan Gantalin ta Daina shi Abba kuma ya Fahimceta yace yasan mganinsu ko Daady bata bari yaji Labarin ba tasan Halinsa ba Fahimtar komai zai yi ba