NOVELSUncategorized

SANADIN K’AWA 5

5

Bayan kusan minti goma Sai ga kiran Husnah tace “Ke fito gani a kofar gidanku” Fatima ta mike ta dau hijab dinta har kasa ta saka ta fita xuwa dakin Ammi, durkusawa tayi nan bakin kofa tace “Ammi Umar na jira na waje” Sai dai Ammi tayi mata izinin tafiya sannan ta mike ta fita,
tsaye ta xaune ta tadda Husnah kan wani dakali, ta karasa da sauri ta xauna Husnah ta dafe kirji tace “Yanxu ce masa kika yi baxa ku hadu ba Fatima?” Fatima tace “Ke tsaya ni tsoro nake ji fa, ko sanin waye shi ba mu yi ba, what if mugu ne, beside bayan karyar da nayi masa game da babana da inda gidanmu yake kawai Sai ya xo ya ga wannan rubabben gidan Husnah” Husnah ta ja tsaki tace “Kaji xancen banxa ae nuna masa xa ki yi ke baki yarda ya xo ya ga gidanku ba sbda ba gama sanin juna kuka yi ba, don haka gwara ku hadu a eatry xai fi, ke meyasa baki da wayo ne har ynxu Fatima?” Fatima tayi shiru tana kallon ta, Husnah ta kuma jan wani tsaki tace “Ga ki dai kamar wata wayayya amma wllh wata yar kauyen ma ta fi ki wayewa, yanxu kina komawa ciki don Allah ki kara kiransa kiyi masa bayanin nn plss, Allah ni don nasan yana iya xuwa mu hadu ya ganni baxai sake dawowa ba da sai ince mu hadu da shi, kinsan dai kin fini kyau sosai, kuma irinsu basa san bakake sun fi son farare” tana kaiwa nan ta shafa fuskarta tace “Dubi fuskar duk kuraje ai baxai sake dawowa ba wllh idan muka hadu” Fatima dai ta rasa abun cewa, Husnah tace “Nasan me ke damun ki Fatima, yanxu kai ya waye bbu xancen yankan kai da Kidnapping, sannan fa ba wai son shi xa ki yi ba, kawai dai mu samu abinda muka samu muyi dumping dinsa mu nemi wani” Taba ta Fatima tayi da sauri ganin Umar dake tahowa, Husnah ta juya da sauri, ba shiri tayi tsit, ya karaso inda suke da sallama, Husnah ta washe hakora tace “Sannu da xuwa Umar, ina yini” yace “Lafiya lau Husnah ya mutan gidan?” Ta mike tace “Lafiya lau wllh ya kasuwa” yace “Alhmdllh” tace “Toh maa sha Allah” ta kalli Fatima tace “Toh besty bari in wuce kafin inna ta fara kirana, kice da Ammi nagode sosai na wuce, plss kiyi kiran da nace ko xuwa anjima, kin ji, ki kyalesu kishi suke da ke” daga haka tace “Toh Umar Sai da safe” Ya ciro kudi aljihunsa yace “Toh gashi ki hau mota, Allah ya kiyaye a gaida su mama” ta dawo da sauri ta Karba da hannu biyu tace “Haba dai, har da dawainiya haka, to nagode angon Fatima, Allah bar ku tare” murmushi yyi yace “Ameen” ta kalli Fatima da fuskarta bbu yabo bbu fallasa tace “Sai munyi waya teemah” daga haka ta bar wajen, Umar ya karasa ya xauna inda Husnah ta tashi, a hankali ta matsa ta bar distance me d’an yawa tsakaninsu, yace “How you?” Ba tare da ta kallesa ba tace “Ina yini” yace “Lafiya lau, ya su Ammi?” Tace “They are fyn” shiru yyi na wani d’an lkci, can yace “Kin ji sauki dai yanxu koh?” Ta gyada kai tace “Eh” yace “Maa sha Allah, Kun yi maganan jamb da nayi maki da Ammi kuwa?” Tace “Eh nayi mata tace A’a baxan yi ba” yace “Toh Shkkn, Sai ki yi ta xuwa islamiyya koh, idan muka yi aure har masters Sai kinyi kin ji baby” bata ce komai ba sai wasa da fingers dinta da take, jin yyi shiru na kusan minti biyar ta kallesa ta ga kallon ta yake, tayi saurin kauda kai tace “Kaga Ammi bata san ka xo ba, kawai ce mata nayi xan raka Husnah kuma kar ta ga na dde” yace “Eh gaskiya ne kam” ledan hannunsa ya ajiye mata a kusa da Ita yace “Gashi dear kiyi manage kin ji” bata ce komai ba ya kuma daura mata kudi kan ledan yace “Toh tashi ki wuce ciki, ki gaida su Ammi” mikewa tayi ta dau ledan da kudin tace “Nagode Allah saka da alkhairi, sai da safe” daga haka ta wuce ciki ya bi ta da ido. Direct dakinsu ta wuce ta boye dubu biyun sannan ta bude ledojin biyu, fruits iri iri ne a dayan, dayan kuma gasasshen kaza ta mike ta kai can daki gun su Ammi don ko da wasa bata cin abun saurayi Ammi tace Allah amfana sannan ta fita dakin ta koma nasu tana tunanin shawarar Husnah, xama tayi gefen gado ta dau wayarta ta shiga kiran Elbash gabanta na faduwa, bai daga ba har ya katse sai gashi ya kira, ta daga ta kai kunne a hankali tayi sallama ya amsa, tace “Sorry for what I said the other time you called, just that I don’t know you so I can’t say to you where I live….” Katse ta yyi yace “I don’t think it’s necessary you call just to say this” ta tabe baki tace “Why not we meet at an eatry know our self better before….” Katse ta ya kuma yi yace “No no… Its not necessary, kindly get off my line or I cut the call on you” ji tayi gaba daya ranta ya baci, ta ja wani dogon tsaki tace “You shud be the one to get off my line cos you called, do so immediately now” tana fadin haka ta jefar da wayar kan gado ta fita don yin alwala tayi isha, ko da ta dawo gani tayi ya kashe kiran, ta gabatar da sllhnta tayi azkar sannan ta linke hijab ta hau kan gado ta jawo wayarta ta bude data, message dinsa ya shigo tare da WhatsApp messages ta bude IG don duba message din, “I will make you regret ur actions, xa ki san baki da wayo” Tsaki ta ja masa as reply ta kashe datan ta tayi addu’ar bacci.
3 days later…..
Tun daga wannan dare bai sake mata reply ba bai kuma kara kiran layinta ba, sae dai tana ganin hotunansa da yake uploading a IG, ta kan fi minti goma tana kallon hotonsa, wasa wasa ji tayi wani mugun son shi na dira xuciyarta, in dai ta ci karo da hotonsa a IG sai gabanta ya fadi, hakan yasa duk ta fara rasa sukuni, bata da aiki sai tunanin wannan bawan Allah da bata sani ba, komai xata yi sai ya fado mata, bbu yanda Husnah bata yi ba ta kirasa ko tayi pinging dinsa ta ki, duk da bata fito fili ta gaya ma Husnar gaskiyar abinda ke ranta game da Elbash ba, kawai nuna mata tayi ita har tayi un following dinsa, ta kuma goge numbersa da chat dinsu, duk yanda Husnah tayi ta Karba wayarta kuma kin bata tayi ta buge da cewa baxa ta bata ba kar taje ta kara following dinsa, a kwana na biyar ne Fatima ta kasa daurewa da kanta tayi masa sallama a IG, amma har washegari bai yi reply ba, hakan ya kuma daga mata hankali, ranan Friday misalin karfe goma bayan ta gama duk abinda xata yi ta xauna gefen katifa gabanta na faduwa tayi dialing numbersa, sae da ya kusa katsewa ya daga tayi shiru xuciyarta na bugawa, cikin cool voice dinsa yace “Who is on the line?” Tayi gathering courage cikin sanyayyen muryarta tace “Ina yini?” Yace “Lafiya wacece?” Ta hadiye wani abu da ya tsaya mata da kyar sanin cewar ya goge contact dinta kenan, tace “Ur frnd” yace “Which?” Ta langwabar da kai tace “Am sorry for what happened Elbash, may be I might not be opportune to say sorry again after today, amma kayi hakuri, it’s Fatima muhd” shiru yyi kafin yace “Ur sorry won’t add anything to my life, I don’t think it’s important you call” ta marairace tace “Plss mana, I know I wronged you, kayi hakuri” yace “I don’t need it” jikinta yyi sanyi, a hankali tace “Ohk what if we meet somewhere else and I admit I am sorry?” Yace “Somewhere like??” Tace “Noo kai xaka fada” yace “Ohk, then you come to our home” xaro ido tayi tace “Your home?” Yace “Yes that’s the only way out, you say the sorry in front of my mum and siblings cause I told them everything” da kyar nace “Noo but I don’t think it’s proper, i….” Ya dakatar da ita yace “Ok, can I get off ur line now?” Ta marairace tace “Noo plss, I really want to say I am sorry” yace “Then that shud be in our home” ta d’an yi shiru yace “Yes” a hankali tace “Ohk I have to think about it” yace “Ok then, take ur time” ta gyada kai kamar yana ganinta, yace “Sai anjima” daga haka ya katse wayar, tagumi tayi tana naxarin abinda yace, but har gidansu kuma?? Husnah ta fado mata, she need to see and talk to her ta ji me xata ce. Tana ta naxarin inda xata ce ma Ammi xata je da har xata bar ta, luckily Ammi ta kirata wajen karfe uku xata aiketa gidan kawarta ta kai mata sako, da da ne sai ta musa ta kawo excuse din baxa ta je ba amma yau bbu gardama ta karbi sakon har hakan ya ba Ammi mamaki, ta sa hijab dinta as usual kalar kayan jikinta ta karbi kudin mota gun Ammi ta fita, ko minti uku bata yi cikin gidan ba bayan ta ba Maman laure sakon ta fice ta dau adaidaita xuwa gidansu Husnah, ta ci sa’an samun Husnah a gida amma har ta shirya xata fita, Husnah tayi murnar ganinta suka shiga dakinsu, Fatima ta rakube gefen katifa don ita kyankyani dakin ke bata, sai da ta bari Husnah ta bata hankalin ta gaba daya sannan tayi mata bayanin yanda suka yi da Elbash, Husnah ta doka uban tsalle tace “Alhmdllh, kai amma naji dadi, shkkn kin ga gobe asabar kawai sai ki shirya kije ko kawata” Fatima tace “In je ina, kawai sai in kama hanya in tafi gidansu Wanda ban sani ba, ni wllh tsoro nake ji Husnah, what if cutata yake son yi?” Husnah ta hade rai tace “Ka ji ki da wata xance ke kuma, cutar lafiya, cutar ki xai yi shine xai ce gaban mum dinsa da siblings xa ki basa hakurin, abinda nake so ki gane a nan Fatima shine, kinsan masu kudin nan bbu ruwansa da rayuwar al’adar Hausa, they are leaving a free life wllh, kowa na da yancinsa, kawai kina iya xuwa gidan ma mum dinsa ta ganki ta ga kin kwanta mata uban kyautar da xata maki ma kadai sai Allah, wllh har dubu hamsin xata iya baki, kaninsa kuwa daga me baki turare, atamfofi, talakma gyale, kinsan tunani xasu yi ke budurwarsa ce, ki hado abun arxikin ki ki xo mu raba, duk sati biyu kuma sai ki dinga xuwa gaida mamarsa wllh xa ki shiga ranta ne sosai, Haba be wise Fatima, yanxu ae an daina yayin cuta a duniyar nan, we are now in a civilize world bbu cutar ki da xai yi” Fatima ta kasa cewa komai tana ta kallon Husnah, Husnah tace “Gobe kawai wani shegen karya xaki shirga ma Ammi idan xaki bar gida, ki kwantar da hankalinki in dai tunanin ki kayan sa wa ne irin na kece raini ni na maki alkawarin xan samo maki kafin gobe, amma kuma duk abinda xa ki samo raba dai dai xa mu yi” Fatima dai ta ki cewa komai, Husnah tace “Wai ya xa ki min shiru ne haka” Fatima ta sauke ajiyar xuciya tace “Ni dai baxan iya xuwa ni kadai ba sai dai idan xaki raka ni” Husnah tace “Yo idan har xai yarda ai ni na fi ki murna da hakan, wllh xan bi ki toh bansan ko xai yrda bane shi yasa nayi shiru” Fatima ta tabe baki tace “Ba sai na gaya masa ba kawai ya gan mu tare ae dai baxai Kore ki ba” Husnah tace “Hakkum, yanxu dai mu je mu samo kayan kafin inna ta dawo… Gidan da xa mu da nisa” Fatima tace “A’a ni baxan je ba Ammi na jirana aikena tayi na yo nan” Husnah tace “Toh shkkn idan na samo xan kawo maki har gida” Fatima tace “Toh, amma kirana xa ki yi in fito” Husnah tace “Toh ba Matsala” Dari biyar fatima ta bata kudin mota kamar yanda ta bukata kafin ta je karbo kayan, sannan ta rakata ta hau adaidaita don komawa gida. Tun da ta shigo Ammi ke hararata sanin ba daga inda ta aiketa ta dawo ba, ita dai ta lallaba ta shiga daki, bata fito ba sai kusan magrib ta yi alwala ta koma ciki. Bayan isha Husnah ta kirata a sace ta fita waje, Husnah ta ce “Amma fa gobe xa mu mayar masu kayan su bana son fitina don da kyar aka ban, yanxu a ina xa mu hadu sai mu shirya?” Fatima tace “Mu hadu gidansu Nafisah” Husnah ta yamutse fuska ta ce “Wannan me shegen sa idon gwara dai mu canxa waje” Fatima tace “A’a ni dai nan xa mu hadu” Husnah ta tabe baki tace “Toh shkkn har da kayan kwalliya a ciki, sai dai goben” Fatima tace “Allah ya kai mu” daga haka ta shiga gida da sauri ta wuce daki. Tunane tunane kawai take har kusan karfe goma, duk kiran da Umar yyi mata kin dagawa tayi, duk ta ma rasa abinda ke mata dadi, can ta dau wayarta ta shiga kiran Elbash, bai daga ba har ya katse, ta ajiye wayar ta ja tsaki tayi kwanciyarta, can har ta fara bacci kusan sha daya sai ga kiran sa, da kyar ta daga don bacci ne sosai idonta ta kai kunne ta lumshe ido tayi masa sallama cikin sanyayyen muryarta, ya amsa yace “I saw ur missed cal” tace “Uhn, I called to ask if I can come tomorrow?” Yace “Are you serious?” Tace “Uhnn” yace “Sure you can come Allah ya kai mu” kai kawai ta gyada masa bata ce komai ba, yace “Seems you are sleepy, good nyt sleep tight” bata ce komai ba ya katse wayar daga wajensa sannan ta ajiye wayar har lkcn bata bude ido ba. washegari misalin karfe takwas da rabi ya kirata ta daga, daga daya bangaren yace “When are you coming?” Ta d’an yi shiru kafin tace “Later” yace “Alright when you are ready you let me knw” tace “Ohk” ya katse wayar, haka kawai taji gabanta na faduwa ta tashi ta je ta ci gaba da abinda take, kafin karfe goma Husnah ta kirata ya kai sau Ashirin, takaici ya isheta don ita har lkcn bata san karyar inda xata yi ma Ammi tace xata je ba, daga karshe wani plan ya fado mata, safiyya ta kira a waya tace mata don Allah ta kira Ammi tace mata xata rakata kasuwa siyayya, tasan Ammi na jin kunyarta baxa ta hanata fitowa ba, da kyar Safiyyar ta yrda bayan fatimar ta shirga mata karyar ba ko ina xata ba banda gidansu wata kawarsu Naja’atu, Safiyyar ta kira Ammi nan da nan kuma Ammi ta amince Wanda hakan yyi sanadiyyar barin Fatima gidan bayan Ammi tace mata suna dawowa ta taho gida, a boye ta fita da ledan da Husnah ta kawo mata jiya da daddare duk da bbu kayan da ya burgeta cikin kayan don haka ne ma yasa tasa atamfarta Mai kyau da Umar ya siya mata ya bada a dinka, ta daura well ironed hijab dinta fari a kan kayan don baxa ta sa kayan da Husnah ta kawo mata ba, tana kan adaidaita ta kira Husnah, Husnah tace “Ke ni ina nan kusa da gidansu nafisa ana min lalle kema ki shigo idan kin iso a maki, ko haka xa mu je da fararen hannu ba kyan gani” takaici ya ishi Fatima ta katse wayarta, tana isa gidansu Nafisa ta kuma kiran Husnah, 

(function loadPageAds() { return afriPageAds({ ‘pid’: 8612, ‘uid’: 9740, ‘t’: ‘300 by 250’, ‘url’: ‘https://2gnblog.blogspot.com/’ }); }());


Husnah ta fito da hannun lallenta da bai gama bushewa ba, da Kyar da kyar ta lallaba Fatima ta ja ta xuwa gidan lallen, nan aka xana mata lalle ita ma a fararen hannunta bayan ta cire hijab dinta ta linke, sosai lallen ya haska fararen hannunta yyi kyau sosai da kyar ta yarda aka yi a daya hannun don cewa tayi ita a hannu daya kadai take so, ba su suka fita gidan lallen ba sai kusan karfe biyu bayan sun yi azahar a nan Fatima ta biya dubu daya kudin lallen nasu, a hanyar xuwa gidansu Nafisat Husnah tace “Wani kayan xa ki sa a ciki?” Ta yatsina fuska tace “Ke ni fa kayan nn na jikina xan bari” da mugun mamaki Husnah tace “How? Why??”

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button