GURBIN IDO

GURBIN IDO 51-56

Ran unaisa fes take takowa zuwa wajensa,har zata wuce parking lot ta sameshi,sai kuma ta tuna dazun bata shiga ta gaida ammansa ba,don haka ta juya akalarta zuwa sassan amman.

Tarba me kyau amman tasa aka mata a matsayinta na surukarta matar ja’afar dinta,wadda tayi zuwan farko cikin gidan tsahon aurensu shekara guda,saidai kuma gaisuwar ma a tsaitsaye tayi mata ita,ta gaya mata ja’afar din ke jiranta zasu wuce gida,bata wani tsawwala ba itama sukayi sallams ta fito tana duba agogonta,tasan tadsn bata masa lokaci,amma babu komai zata wanke kanta,wuyarta ta samu kansa daga yau gobe zuwa jibi.

“A’ah,badai har kun fito ba?” Muryar haj munubiya ta yiwa unaisa tsinke,ta waiwaya a hankali,hajiyar na biye da ita a baya kamar ma hanzari take ta cimmata,cikin murmushin yaqe kasancewarta ba wata meson jama’a ba tace

“Eh….”

“Shi yasa naga kinata sauri ai” ta sake fada tana jifanta da murmushi

“Eh,zai saukeni a gida ne”

“Ayyah,gashi kuma naga ya fita yanzu yanzu,dab da zaki fito daga gaida surukuwarki” idanu unaisa tadan fidda tana duban inda ya faka motarsa,wayam babu ita,ta dauke dubanta daga wajen,ranta na mata wata irin suya,da gaske tafiya yayi ya barta?.

“Indai ja’afar ne wannan ba komai bane a wajensa….amma kada ki damu,gidan surukan naki ai cike yake da direbobi” ta furta tana karantar fuskar unaisa.

   Unaisan batace komai ba,sai ta sauke jakarta ta fara qoqarin fiddo wayarta

“Ba matsala,zanyi waya a kawomin motata” ta fadi cikin zallar bacin rai,tunda ya tafi ya barta ba zata shiga motar gidansu ko daya ba,don indai motace wannan tafi qarfin duk wata mota

“Uhmmm,ai dama shiryawa hakan akayi,shi yasa ita dayar tace ba yanzu zata tafi ba ai,kekam Allah ya baki wuyan dauka” haj munubiya ta fada tana motsawa gaba kadan kamar zata bar wajen,duk da ba ainihin hakan bane a ranta,tayi hakanne don jan hankali,taa kuwa jaa hankalin unaisan,don daga kanta tayi ta dubeta

“Kamar yaya?” Tambayar tazo ma haj munubiya a dai dai,abinda takeson ji kenan

“Ba zakiji mutuwar sarki a bakina ba,kedai kije kiyita haquri” yadda tayi maganar tana niyyar wucewa sai hakan yaja hankalinta,da sauri ta dakatar da ita,ta jima tanason sanin wasu abubuwa game da gidan dama ja’afar dinta,to amma bata saki jiki ba bare ta saba da kowa ballantana ta samu wasu labaran,sai a yanzun da hajiyan ta tareta da kanta

“Karki tafi,don Allah ki gayan abinda ke faruwa” jimm tayi kamar batason cewa komai kafin tace

“Banyi niyyar cewa komai dake ba,to amma kuma mahaifiyarki hajiya Aayag ta tabamin wani alkhairi da bazan manta dashi ba,shi na tuna a yanzu, shine kuma kawai zai sanya na taimakeki na shiga lamarinki”

“Uhmmm,ina saurarenki” ta fada cikin zaquwa da son jin abinda haj munubiyan zata fada.

    Dan waiwaya tayi,tana duban gefe da gefanta,sannan ta maida idanunta ga unaisa

“Magana a nan ba zata yiwu ba,kizo gida ki sameni” kallon haj munubiya unaisa tayi,ta mance diyar wacece ita da zata ce taje gidanta?,lallai tayi araha da yawa,ya kamata ta dawo da girma martaba da izzarta da auren ja’afar yasa ta watsar,abinda yake ta yiwa mahaifiyarta haj Aayah ciwo kenan

“Saidai kizo ki sameni,bazan iya zuwa gidanki ba” murmushi hajiya munubiya ta saki,dama hakan takeso,batason karon farko tace zata je ne,kada ta zargi wani abu a ranta,ko kuma kimarta ta zube

“Karki damu,bana saka manta alkhairi ni din,zanzo in sha Allahu”

“Kamar gobe?,zan aiko da mota a daukoki?”

“A’ah,banason kowa ya zargi wani abu,mu barwa nan da kwanaki biyar ko zuwa rana ita yau,amma fa kafin sannan ki sanya idanu da dukka abinda zakiga ya faru,maganganuna zasu bayyana miki komai” kai kawai ta gyada,sannan ta buda jakarta ta ciro sababbin kudi masu dama ta miqa mata,da murmushi ta karba,ta lura kallon faqiriya take mata,batasan tafi qarfin dukka buqatunta ba,batajin cikin familyn khalid akko diyoyin anni akwai mabuqaci da baifinqarfi ci sha da suturarsa ba,gami da sauran buqatu na dan adam harda ra ra

“Bana buqatar komai a wajenki ‘yar nan,don Allah zan miki,da kuma qaunarki da Allah ya sakamin”

“Na gode” ta fada tana maida kudinta jaka.

Kasancewar bata samu number da take kira ba,tilas ta shiga motar gidan driver ya maidata gida,don ta qagu ta isa gidan suyi magana da anty talatu,sannan kuma ta fara tsare tsare da shirye shiryenta.

*_ADAMAWA_*
_RIGAR UMMARU_

A matuqar rude zaninta a hannu,tana tafe tana qoqarin maida zanin nata ta daurashi dai dai yana sake qwace mata,duk da hakan bata saurara da uban saurin da take zambadawa ba zuwa makwantar sabbin,inda take jiyo muryar laulo yana qwala mata kira babu qaqqautawa,ta kuma tabbatar ba lafiya ba,don dama duka kwanakin musiba da jarrabawa take.

Daga nesa ta tsaya cak tana bin dabbobinta da kallo,wanda da kadan da kadan sun zaizaye sun rame,dukka wannan cikar tasu kyau da kuma qoshin lafiya babu ita a tare dasu,kamar wadanda ake suda,ko kuma annoba ta fadawa.

Gabanta dukan uku uku yahau,ganin nagge guda hudu manya runtuma runtuma aqas babu alamun rai tattare dasu,tun kafin ta qaraso wajen ta dora hannayenta aka idanunta suka tara ruwan hawaye

“Yauwa inna,gasunan,nidai bansan me ya faru ba,ba zagaya zan kama ruwa,dana dawo na tarar babu gajee a wajen,dana duba da kyau kuma sai na samu wannan naggen guda biyar a zube a bakin ruwa,to guda daya ce me sauran rai,na ruga na kira na lami ya yankata ya siya,yace zai aiko miki da kudinki” sulalewa kawai tayi a wajen,tahau taba naggen daya bayan daya,batayi aune ba qwalla ta qwace mata,ta soma sharbar hawaye

“Wadan nan ne sukayi dakon jawosu,tunda kinsan anyi doka an hana yarwa,yana taba amfanin gonar manoma,saiki biyasu” daga haka laulo yayi gaba abinsa ba tare daya tsaya bi takan inna furera ba.

Kamar zata fadi haka don baqinciki,haka ta nufi shiyyar dakunanta ta dauko.musu kudin,qarta qartan samarin fulani ne majiya qarfi sun zuba mata idanu,banda haka bataga abinda zai sanyata biyan wadannan kudaden ba bayan asarar data tafka goma da ashirin.

Da qyar tayi sallar magariba ta hadeta da isha’i,tana zaune a wajen,ita ba addu’a ba ita bata bar wajen ba,sai qiyasta girman asarar da take tafkawa takeyi,tunda maimunatu tabar hannunta komai ya sake tabarbare mata,tun bayan tafiyarta take qunzuge kudaden da anni ke aiko mata,taqi daukan mai mata kiwon,ta tilasta gajee fita kiwo ita da laulo,da sunan gajeen takewa tanadin kudin daki dama na biki gaba daya,don tace bata ga abinda ubanta yake dashi ba da zai kai mata gidan aure.

To gajen dai ba’a son ranta ya fara fita kiwon ba,don dama gaba daya bata saba ba,a sangarce ta tashi,uwa uba kuma ita aure kawai takeso da himu,wannan yasa gaba daya ita da dabbobin suka shiga wahala,babu kulawa me kyau,a hankali suka fara lalure lalure,sai kuma haka siddan suka fara mutuwa,yau wannan gobe waccan,kudaden da taketa tarun su ta dunga diba tana musu maganu tare da karbo taimako na kambun baka da maita,waiko mayu ke kadar mata da garke,ita kuwa gaje ba abinda ya shalleta,idan suka fita kiwon sai tayi batan dabo,shi dai laulo baisan ina take zuwa ba,amma dai bata dawowa yawanci sai gab da zasu koma gida,tun inna furera bata gane meke faruwa ba,har ta gane,qaura wambai ta fadi ina take zuwa amma ta qeqashe qasa taqi fada,har inna ta haqura ta zubawa sarautar Allah ido.

A hankali ta bayyana wani baqon bafullatani take bi su fice daga shiyyar abinsu,haruna kyakkyawan bafulatanine wanda yake ruwa biyu,wani irin kyau ne dashi don hatta qwayar idanunsa launinta daban yake,idanun haruna a bude suke,sabida sunyi yawon kiwo gari gari qasa qasa,don haka babu wuya ya yaudari yarinya ta fada soyayya dashi,da wannan kyan nashi yake amfani,ya yaudari ‘yammatan dashi kansa baisan iya yawan adadinsu ba,da haka ya yaudari gaje ta fada soyayyarshi da sunan aurenta zaiyi,tana da son abu me kyau,don soyayyar himu fiye da rabinta kyansa ne yake janta,sai gashi ta samu wanda ya fishi.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button