HALIN GIRMA COMPLETE HAUSA NOVEL

HALIN GIRMA 1

 

*HALIN GIRMA!*©️®️Hafsat Rano.

FREE PAGES!

(1)

*_WAIWAYE……ADON TAFIYA inji masu salon iya magana_*

*ZAFAFANKU BIYAR ????????????????sune suka sake dawo muku da wasu nau’in QAWATATTU kuma TSARARRUN LABARAN,masu dauke da SABBIN JIGO na MABANBANTAN LABARAI masu tsuma ZUCIYA*

*_SANIN HALI…..yafi sanin kama,indai kasan TAFIYAR ZAFAFA babu dana sani ko nadama cikin zuba kudi wajen siyan litattafansu,koda jin sunan ma kasan cewa tafiyar ta dabance_*

*GWADA IDAN BAKI TABA BA!!!,HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKAN SAN NA ƘWARAI,burinmu kowa ya shigo cikin tafiyar a dama dashi*

*JERIN SABABBIN LITATTAFAN NASU NA WANNAN KARON SUNE*

*_DEEN MARSHALL???????? Mamuhghee_*

*_HALIN GIRMA????????hafsat rano_*

*_TAKUN SAƘA????????billyn abdul_*

*_SO DA ZUCIYA????????miss xoxo_*

*_ƊABI’AR ZUCIYA????????huguma_*

*DUKKAN WADAN NAN LITATTAFAN ƊAI ƊAI HAR BIYAR…ZAKU SAMESU AKAN KUDI NAIRA 1K KACAL*

2????????400

3????????500

4????????700

5????????1000

*Zaku saka kudinku ta wannan asusun bankin*

6019473875

MUSAA ABDULLAHI SAFIYA

keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number

08184017082

*IDAN KATIN WAYA NE KO VTU,SAIKU TURA ZUWA GA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANKU*

09134848107

*_HAR KULLUM MUNA MARABA DA ALFAHARI DA MASOYANMU_*????????????????????????????????????????

#team zafafa biyar

(1)

***Komai na rayuwa na tafiya ne bisa tsari da kudurar ubangiji, komai ya faru da bawa dama tun fil azal hakan na cikin kaddarar sa, Wala kaddara mai kyau ko kuma akasin ta. Yarda da Kaddara me kyau ko mara kyau na cikin Imani! 

   A tsaye take gaban sink din cikin toilet din tana wanke kananan kayan da ya kasance mallakin Maama da Zeenat, lokaci zuwa lokaci tana cire hannun ta tana yarfe shi saboda sanyin da ake zugawa kasancewar karshen December ne a lokacin da ake zuga sanyi. Dauraye kayan tayi ta yi saurin fitowa ganin haske ya hudo ta window din toilet din. Karfe shida da rabi agogon falon ya nuna, tayi saurin karasawa kitchen din domin dora abin karin kumallo kafin ahalin gidan su tashi.

  Tun kafin asubah take fara ayyukan gidan wani lokacin har karfe tara na safe bata kamalla wa, duk kuwa da tana iyakar kokarin ganin bata wuce taran ba saboda karatun ta na islamiya da take zuwa duk weekend, tana ganin shine kadai gatan da zata yi wa rayuwar ta a halin da take ciki a gidan mahaifin ta. Bata fatan wani ya shiga irin rayuwar da take ta kunci da tsantsar makirci, babu wanda ya san halin da take ciki balle ya kawo mata dauki, bata isa ta bud’e baki ba saboda kowa ganin kirki da karamcin Maman yake, mace ce me masifar kirki, me haba haba da saka duk wani abu nata gaba da na duk sauran yayanta a idon ahalin gidan,a badini kuwa bata da maraba da bola.

   Kowa kallon mara dadin zama yake mata ko kuma mara godiyar Allah saboda rashin walwalar da take fama da har ya shafi kaso mafi rinjaye na rayuwar ta, zaka dauka bata dariya ko doguwar magana sai dai bata da sukunin yin kamar sauran yan matan gidan nasu.

  Kowa kallon wadda tayi sa’ar uwar riko yake mata, ayi ta sakawa Maman albarka da yabo a gabanta tana amshewa amma a bayan idon mutane! Bakar wahalar da take sha ba zata misaltu ba.

   Da tunanin ta kammala aikin ta dauraye hannayen ta sannan ta fito ta jera musu a saman dining ta dauko nata a dan plate ta wuce zuwa dakin su.

   Bude kofar da tayi ya farkar da Zeenat, a zafafe ta dago ta watsa mata kallon banza gami da jan d’an karamin tsaki tana sake rufe kanta da katon duvet din da take kanannade a cikin sa. Cikin nutsuwarta ta karasa shigowa d’akin tana dora plate din saman d’an madaidaicin mudubin dake cike da kayan shafe-shafe ta soma gyara wajen data tashi. Katifar ta fara daukewa ta kaita chan store sannan ta dawo ta share dakin a hankali gudun magana taci abincin a tsaitsaye ganin lokaci na neman kurewa tayi saurin watsa ruwa a gaggauce ta fito.

  Dogon hijabin ta ash colour daya kasance a matsayin uniform din islamiyar tasu ta saka bayan ta gama shiryawa ta dau yar madaidaiciyar jakarta me dauke da Al-kurani me girma da sauran littafan addini ta fito.

   Habib na zaune saman dining da alamun zaman sa kenan ta gaishe shi a nutse sannan tayi masa sallama ta wuce islamiyyar dake chan kasan layin su inda take zuwa duk asabar da lahadi da safe sai sauran ranakun da yamma amma banda juma’ah.

   

   

   *Babban gida ne irin wanda zaka kirashi da Family house, bangarori ne da dama a ciki wanda yake dauke da gidaje guda shida dake kunshe da mutane cikin su suna rayuwa irin wadda suka zaba ma kansu. Duk da kowanne bangare na da tsarin da yake tafiyar da rayuwar sa akai amma kuma suna tafiya ne da ra’ayoyin juna, daya baya taba zartar da hukunci be sanar da daya ba, sannan duk abinda suka zartar din dole ne ya samu amincewar mahaifiyar su Hajiya Fatima wadda suke kira da Gaji.

   Gidan ta ne a tsakiya in da sauran gidajen ke kewaye da ita, galibin yan matan family din suna tattare ne a shashen nata da ya zama tamkar matattarar su, yanayin haihuwa a family din na tafiya ne kusa da kusa, inda zaka samu yawanci sa’oin juna a kowanne gida.

  Duk da basu da tarin dukiya irin me yawan nan amma suna da rufin asiri daidai gwargwado, sannan ana damawa dasu a duk bangarorin ilimi na Islama dana bokon hakan ma bangaren kasuwanci da siyasa duk babu wanda basa tabawa.

   Zamu iya cewa kowanne a cikin yayan Gajin yayi sa’ar abokiyar zama ta kwarai dan babu wanda yake kuka da abokiyar zaman sa, daidai gwargwado suna zaman su lafiya suna kuma mutunta juna suna girmana Gaji da duk wata bukatar ta.

   Muguwar mace me kinibibi da kissa zai yi wuya ka gane alkiblar ta farat daya, komai su kayi daidai ne suna kuma da kokarin kyautatawa kowa, suna kokarin boye aibun su suyi amfani da hakan wajen muzgunawa wanda basu so, idan yayi korafi a bashi rashin gaskiya saboda kirkin su. 

   Alhaji Muktar shine Babban dan Hajiya Gaji bayan Babbar Yayar su mace da suke kira da Hajiya Babba dake zaune a Sheffield dake birnin London tare da family dinta , sai me bi masa Dr Ibrahim, sai Abba Usman sai Abba Musa sai dan auta Abba Kabir. 

   Dr Ibrahim dan boko ne sosai dan har ya kai matakin associate professor in da yake lecturing a halin yanzu. Matar sa daya ta aure Maama wanda zamu iya cewa kaf family din babu wanda baya kaunar ta saboda kirkin ta. Yaranta uku da Dr, Habib ne Babba, sai Zeenat sai karamin kanin su Marwan. Sai dai shi yana da ya daya daban wadda suke haifa da matar da ya aura a lokacin da yaje karatun sa na Masters a University of Michigan, anan suka hadu har sukayi aure suka haifi ya daya me sunan Gaji (Fatima-Iman) a lokacin ne kuma suka rabu saboda wata babbar matsala da ta taso tsakanin shi da family dinta, dan dama basa son auren, yana ji yana gani ya rabu da ita, ya dawo gida. Fatima na yin wayo suka kawo masa ita inda ya dauki rikon ta ya damka a hannun Maama wanda a lokacin take goyon Zeenat itama. Bata taba nuna masa komai ba ko a fuska kuma be taba ganin wani banbanci tsakanin Fatima da Zeenat ba, shiyasa ya kara bata mazauni me girma a zuciyar sa.

***Daidai layin su ta hangi Zeenat tsaye da Bashir, dan dam taji a zuciyar ta kasancewar ba wannan ne karo na farko ba, duk wanda yace yana son ta in sha Allah ba za’a dau lokaci ba zata same shi tare da Zeenat shikenan kuma ta ta maganar ta sha ruwa. Zeenat yar uwarta ce amma duk da haka tana jin babu dadi, sai dai bata bar hakan yayi tasiri a zuciyar ta ba, ta dau hakan a matsayin wata jarrabawar rayuwar ta. Daidai in da suke tsaye tazo zata wuce Zeenat din ta kira sunan ta

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button