GAMO DA KATAR Complete Hausa Novel

Advertisements
*”BISMILLAHI-RAHMANIR-RAHIM*”
*Page* 1⃣
Garin Abuja sanyi ake na fitar hankali mai tattare da hazo da hunturu wanda mutum ko na gaban shi baya gani asanadiyyar hazon da ake fama dashi agarin.
Tafe suke ahanya tana ta mita tana cewa “gaskiya Inna nina gaji tun qarfe bakwai muka fito gashi yanzu har tara tayi,amma bamu samu komai ba ni yunwa ma nake ji gashi sanyi ya shaman kai hanci na sai zuba yake da majina gashi kin hana na tsaya gidan Alhaji na samu sadakar koko, su maryam na can yanzu sun samu koko sun gasa hanjinsu kin barni nina nawa hanjin sun dunk’ule wuri d’aya”.
“Allah Inna daga nan ban matsawa ko’ina”.Tana rufe bakinta aikam ta saki sandar Inna qasa ta dafe ciki ta k’wala qara tana cewa “wayyo cikin uwar hanjina ta dunk’ule!”.
Inna tace “haba Narim
tashi mu koma gidan Alhajin ki samo sadakar kunu kinji Narim d’ita tashi mu koma ki samu kokon kinji”.Inna ta k’arashe maganarta cikeda matuk’ar tausayinta. Narim ta zumb’ura baki tace”ni wallahi ko munje ya riga ya qare nifa Inna ban ma iya tafiya uwar hanjina ta qulle, kuma wallahi ko mun koma sai dai cikin kud’in barar jiya kibani na siyo shayi”.Ta ida maganarta cikeda matuk’ar rakin yunwa.
Sannan ta sake fad’ar “dama Ammar d’an Alhaji shi keban shayi idan ban samu koko ba yanzu kuma yau ya tafi makaranta kuma sai da malam yace karmu tafi bara mu bari ya gama sak’a kabarsa ya saido yau mu zauna mu huta kikace sai munzo bara gashi yanzu sanyi ya laqumeni sai hancina ke zuba wayyo cikina! “.Inna tace” tashi ki kama sandar”.Ta rik’e sandar tana riqe ciki haka dai suka cigaba da tafiya suka kama hanyar zuwa gida….
_Tofa tirqash koya zata kaya atsakaninsu wannan labarin labari ne mai ban tausayi, al’ajabi tun tana yarinya take fama da mutanen b’oye gashi mahaifanta makafii_
_Ku biyo golden girl kuji yanda zata kasance vote& comments shi zaisa inji k’arfin yi maku typingggg_
*GAMO DA KATAR*
(yar makahi)
*Na*
*Yar mutan jibiya*
(AMMYN KHAIRAT)
*Dedicated to my sarauniya beelat*
(¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯)
тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя’s αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.
INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/
FACEBOOK: https://mobile.facebook.com/groups/2455147078097572/
TWITTER: https://twitter.com/pro__writers?s=09
*BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM*
*Page* 2⃣
NARIM dafe da ciki take tafiya dan magana ta gaskiya tanajin yuwa bata da jimirin yunwa, sandar ma dak’yar take kamawa Inna ita.
Abinka da makaho sai mita Inna keyi tana cewa” da nasan haka zaki man NARIM yau da bamu fito bara ba! Daman nasan tunda Malam yace karmu je ba yau mu tsaya mu huta nasan haka zaki man,gashi yanzu mun sha sanyi abanza ko naira bamu samu bah!”.
NARIM tace”ni wallahi Inna muyi sauri dan ninan bama jinki nake ki bari cikina ya d’auka sannan ki fad’i duk abinda zaki fad’a.. “.
Inna naji ta buga tsawa tace”ni rufe man baki acici kawai”
NARIM ta fashe da kuka tana diddire k’afafunta tsakar k’asa wai dan me inna zata ce mata Acici?
Sai kuka take tana fad’in” wayyo Allah Inna kin sani bana son ana ce man acici ke kuma sai kita ce man acici ,
wa yaqi ci Inna kema yanzu muna tafiya inajin hanjinki na cewa k’uuuuuu”.
“Ni wallahi ki daina ce man acici kinga su Maryam har sun fara ce man acici suma, da ace man acici qara aita ce man ‘yar makahi”.
“Shima bawai so nake ba aman da ace man acici qara ace man ‘yar makahi aida mani ‘yar makahin ce”.
Tunda ta fara tijararta Inna tai tsaye da sanda tareda hangame baki tana jinta dan tasan tijarar NARIM in ta fara to sai ta dasa aya.
Zuwa can ta qara fasa qara sakamakon cikinta daya qara murd’awa tace” wayyo cikina Inna!Inna!!Inna!!! Wai yau so kike yunwa ta kasheni kinja kinyi tsaye?”.
Inna tayi ???? dariya tace” NARIM ‘yar Inna in banda abinki taya bazan tsaya ba tunda ni ba gani nake ba balle intafi kece ‘yar jagora kuma kin tsaya kina abinda kika saba “.
“In kin gama sai mu tafi NARIM”.Cewar Inna Narim taja dogon numfashi tace”Inna kenan da baki ta qyaleni ba aida yanzu mun kai gida”.
Duk wanda yazo wucewa sai ya kalle su inda sabo sun saba ganin kullam fad’a da Inna da ‘yar jagora.
Ba ranar basu fad’a sai dai in basu fito ba wasu abin birge su yake yanda sukeyin abin sai kace kwamedi.
Dan in kana kusa suke abin dole sai ka dara ????.
Wani d’an unguwar su ne yazo wucewa ya tarar NARIM na ta kuka tanawa Inna tijara yace ” NARIM ‘yar makahi yau kuma me ya faru keda Innar taki? ”
NARIM tace”wallahi d’an masu ido Inna ce tace man acici kuma tasan banason ana ce man acici “.
“Dan Allah yanzu qarfe nawa?”. Sai yace” yanzu kusan goma da wani abu”.Afirgice Narim tace”goma”.???? NARIM ta zaro ido ta aza hannu akai tana fad’in” na shiga ukku Inna kin kasheni har qarfe goma yau ban karya ba shi yasa uwar hanjina ke quuuui kauuuu quluuluulu”.
Ta kalli fuskar saurayin tace”d’an masu idon yanzu kokon gidan Alhaji nasan ya qare shi daman nasan ban samun shi daka tafo wannan mai shayin yana nan?”. Sai saurayin yace mata ” eh yana nan na baroshi zai tashi”.Ta k’yalla ihu tace”na bani yau ko sai nayi zawon yunwa”. Taja sandar Inna k’erere suka tafi.
Shima yana dariya yayi gaba tare da karkad’a kai NARIM na birge shi gata yarinya qarama sai wayo shi kuma k’yau ba’a maganar shi.
k’yak’k’yawa ce sosai ina gata girma komai ya bayyana.
Inna sai cewa take” bini ahankali NARIM kinga ba gani nake ba sai jana kike yadda kika gadama dan Allah ki bini asannu kinji NARIM kar na fad’i”.
Narim tace”yo kema dai Inna in na biye maki yau saina yi zawon yunwa kuma kinga uwar hanjina in ba abu mai ruwa mai zafi nasa masa ba bata warwarewa”.
Inna kam tace “wannan yunwa Allah ya rabamu da ita wannan yarinya Allah ka shirya man ita .”Amin” inji NARIM.
Wurin sauri Inna tai tuntub’e data fad’i Inna sai cewa take” innalilahi NARIM so kike ki kadani wallahi inbaki bi hankali ba sai na kwad’a maki sandar nan”.Tace” yi haquri ” .Tebirin mai shayi suka yad’a zango yana ta had’a kayan shi zai tashi Narim tace “Aslm tsaya dan Allah ka taimakaman karka had’a kayanka “.
Wajen sauri ta aza Inna kan benci ashe bata azata daidai ba gefen bencin ta azata Inna ji kake ragwab ta fad’i ta bige kai ga bango!.
NARIM tace” wai Inna kema ga wurinan na azaki kan benchi shine kika matsa kika fad’o”.
Inna ta hasala sosai tace”na fad’o d’in gidanku ni gani nake baki azani dai dai ba yau dai so kike ki kasheni
dana bi maganar Malam da yace kar na fito baran nan da duk haka bata faru ba”.
Mai shayi yace ” Inna kiyi haquri inda sabo ai kun saba keda d’iyar taki”.Inna tace” hummm yaro nan ina ne ta kawoni?”.Yace mata”wajen mai shayi”.
Inna tace”kaine mai shayi ?”.Yace” Eh mana nine”.Inna ta k’ara cewa”to had’a mata na naira hamsin ” .
NARIM tace”ni wallahi na hamsin bai isata kai had’aman na d’ari da hamsin ka had’a man harda k’wai”.” D’ari da hamsin?”.Inji Inna”. ni ina naga d’ari da hamsin yanzu”.
NARIM tace”wallahi kinadasu kud’in baran jiya ba d’ari da hamsin bane kuma ba abinda kika siya dasu”.
Inna tace “tafd’ijam kud’in baran jiya sune zan baki kici k’wai da shayi dasu lallai NARIM “.