HAUSA NOVELINTEESAR 2

INTEESAR 2

motar ita da kawayen nata, wato su zainab,

Anty nafisa ma ta shiga motar suka kama

hanyar gidan Aliyu dake can Hotoro, su

Hajiya da umma dama tun da rana suka

kulle kofofinsu kmr bbu kowa a ciki, don

cikin lodin jama’ar da suka xo bikin bbu

dangin hajiya ko daya bare kawayenta hka

ma umma.karfe goma da kusan rabi motar

da ta taho dasu tayi parkin cikin gidan Aliyu

bayan mai gadi yabude gate din, abokinsa

ne Mujaheed yyi drivin din, gida ne babba

mai kyan gaske ya kawatu da shuke shuke

ta ko ina masu daukar hankali, ginin tsarin

duplex ne, dakuna uku da bathrooms a ciki

each, sae babban falo da bathroom da toilet

a ciki daga downstairs don sae ka hau

stairs xaka tafi dakunan,kitchen din babba

ne sosai sai kuma store dake cikin kitchen

din, stairs uku xae yi lead dinka xuwa

dinning din da aka xagaye da labule snn

akwae kawatattcen garden dake ta bayan

gidan, Anty nafisa ta fito da intisaar daga

motar fuskarta a lullube suka hau stairs na

balconyn, Anty Nafisa ta fadi mata adduar

da xata karanta a kunne kafin ta shiga

gidan kuma ta tabbatar da kafar damanta ta

shiga gidan, sun tar da mutane da dama

cikin gidanmasu jiran kawo amarya, har

bedroom Anty nafisa da yan rakiyar suka yi

ma intisaar jagaro suna guda, ita dae

intisaar ji take kamr ba ita ba binsu kawae

take kmr wata gunki, Aminiyar inna ta

xaunar da ita gefen gadon tana ce ma

mutanen da suka shigo suka cika dakin su

fita su bata waje xatama intisaar magana,

duk sae da ta koresu dakin ya rage daga ita

sae Anty nafisa da xainab, maganganun da

intisaar bata yi xato ba masu nauyita dinga

gaya mata ga anty Nafisa tsaye, xainab

dama tsum tsum tayi ta fice daga dakin, ita

dae fuskarta a rufe yake, daga karshe ta

dada mata nasiha sosai, Anty nafisa na

tayata, kuka sosae intisaar ke yi tana

tausayin rayuwarta don tana da tabbacin

kila farin cikinta ya gama karewa a duniya,

.

karfe sha daya bakin suka watse gida ya

rage daga Anty nafisa sae xainab don har ta

kawayen amarya ma sun tafi, su ma suna ta

shirin wucewa ne, dama Anty nafisa ta ajiye

mata kayan baccin da xa ta saka snn ta

nuna mata turarrukan da xata shafa kafin ta

kwanta, ta tambayeta tana jin yunwa ne,

tace A’a, ta fita kitchen ta hada mata wani

tsumi ta bata ta shanye gabanta, lkcin da

xasu tafi kuwa intisaar rungume anty nafisa

tayi tana kuka sosai wae kar su tafi su barta

don Allah tsoro take ji, sae da xainab tayi

kuka don tausayin intisaar don gigicemasu

tayi, da kyar Anty Nafisa ta lallabata bayan

tayi assure dinta cewar yanxu su Aliyu xasu

shigo don ta kirasa yace suna hanya da

frndx dinsa kuma gobe in’sha Allah xata xo

da safe snn ta samu suka bar gidan don

mijinta na busstop yana jiranta, gidan ya

rage daga intisaar sae halinta, kuka take

sosae kamr ranta xae fita, ta kasa xaune ta

kasa tsaye don tashin hankali, yau ga ta ga

babban makiyinta xasu kwana gida daya,

duk tabi ta takure kanta waje daya tana

rawan sanyi tsoro. Karfe kusan sha biyu taji

shigowar motar Aliyu, xumbur tamike a

tsorace ta daura hannu a ka tace “nashiga

uku ni fateemah,” ta koma ta gefen

madubinta ta tsaya jikinta na bari tana

hawaye sosae, tana ji ya shigo gidan ya rufe

kofofin, tun kan ma ya hayo sama ta dinga

jin kamshin turarensa da ya shiga tada mata

xuciyarta don tsabar tsoro. A hankali taji

yana taka matakalan benen yana hayowa

sama, xuciyarta ya tsananta buga wa, ta

rumtse ido cike da tashin hankali tana yarfe

hannu hade da shesshekar kuka, can kuma

sae taji tsit kmr ba mutum a wajen, ta bude

idonta a hankli tanakallon kofar dakin a

tsorace, taji an bude kofa, saurakiris ta saki

ihu jikinta ya dau rawa, kafanta suka kasa

daukarta ta durkushe wajen tana maida

numfashi kmr warce tayi gudu, a hankali taji

an rufekofar da aka bude.

 

ba dakinta ya shigo ba ta fadi a xuciyarta

tana kkrin maida hawayen dake neman

saukowa a idonta, ta xaune kan tiles din

dake shimfide a dakin ta jingina jikin

gadonta kanta a kangadon, kmr xata fara

sabon kuka kuka, to ta tabbatar baxae

shigo din ba, tayi jigum ta xuba ma kofar

ido tana tunanin irin abinda Aliyu xae mata

indae har ya shigo dakin nn, kila ma jefar da

ita xae yi ta tagan dakin gaba daya, tunda

wanda ya iya bude mota ya wurgota waje

ae komai ma xae iya yi. A hankali intisaar ta

bude idonta jin haske da ya addabi fuskarta,

ta fara waige waige a tsorace tana kallon

inda take, har lkcn tana jingine jikin gadon

nea xaune, sun ray ne ya shigo dakin ya

sauka kan fuskarta, ta mike da sauri tana

kallon agogon dake manne a dakinta taga

karfe bakwae, ta xaro ido hade da dafe kirji

don ko sllh bata yi ba,ita bata ma san

yaushe baccin ya dauketa da har gari ya

waye ba, budewar gate din da taji ne ya sa

ta xuwa kusa da window ta bude curtain

dinta a hnkli tana lekan ma xa ayi, Aliyu ta

gani cikin motarsa yana gaisawada mai

gadi snn ya ja motar ya fice daga gidan mai

gadi ya kulle gate, intisaar ta sauke ajiyar

xuciya ta jingina jikin wall din dakinta tana

tausayin kanta, ganin hkn ba shine gabanta

ba yasa ta shige bayi tawanke bakinta tayi

alwala ta fito, tana idar da sllh tashiga gyara

bedroom dinta ta tabbatar komai yyi mata

yanda take so ta feshe dakin da turaren da

anty nafisa ta nuna mata xata dinga sawa a

daki ta hada da room freshner snn ta shiga

wanka tana gama wankan ta wanke

bathroom dinta tsaf ta feshe ko ina da

freshner snn ta fito dakin, tana cikin fito da

kayan da xata saka taji an bude kofar, ta

juyaa tsorace tare da sakin abinda ke

hannunta a gigiceta fasa wani raxanannen

ihu tace “wayyoo Abbana nashiga uku,”

Zainab ta tsaya baki bude da mamaki tana

kallon intisaar, a hankali intisaar ta sulale

kasa ta xauna tare da dafe kirjinta da ya

kasa daina bugu da sauri,ta galla ma zainab

din harara duk da taji dadin ganinta tace ”

dubeta don Allah, baki iya sallama bne

malama xaki tsorata mutane,” zainab tayi

dariya tace “xa ma ki fadi gskya ne, wae ta

tsamman angonta ne, shine xata wani

wayance ma mutane” intisaar ta galla mata

harara da wasa tace” angon bnxa, meye

hadina dashi, ” zainab ta tabe baki tace ”

kya ji dashi dae,” snn ta karasa cikin dakin

ta ajiye basket din dake hannunta da leda ta

shiga fiffito da kulolin dake cikin basket din

da flask,intisaar ta xauna gaban madubinta

tana shafa mai zainab ta dago tana kallonta

tace “kin tashi lfya amaryarmu,” tayi kmr

bata ji ta ba, zainab tayi dariyar tsokana tace

“kice sae ynxu ma xakiyi sllhn, ina yayana,

nasan kin sa shi makara yau da gani,”

intisaar dae bata kara kallon inda zainab

take ba ta gama shafa mai ta shiga sa

kayanta wani material mai kyau orange n

milk colour,

.

Zainab ta sauka kicin ta dauko plates da

cups ta dawo dakin tana kallon intisaar

dake gyara fuskarta gaban madubi tace ”

wae yaya fa?” intisaar ta baxa mata hannu

alamar ita ma bata sani ba, xainab tace

“joke apart intisaar da gske baya nn,”

intisaar tace ” Allah ni ban gansa ba ma tun

jiya, daxu dae naji fitar motarsa” zainab ta

tabe baki tace “to Allah ya kyauta, kice jiya

ma baki ci ‘yar kazar nn da madara ba”

intisaar ta sauko kasa ta xauna kusa da

xainab kmr xata yi kuka tace “inna fa?”

xainab tayi dariya tace “ke dae bari, ai yau

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button