INTEESAR 2

karfe 5 duk muka tashi a gidan nn wae xa
tayi maku waina kuma a murhu xatayi, snn
xata dama kunun gyada ta dafa muku
ruwan lipton hadadde, ae mun aikatu yau,
har da su farfesun kaxa da kayan ciki, duk
ga su nn” intisaar tayi dariya sosai tace
“Allah sarki innata, amma de ba yanxu xaki
tafi ba ko xainab?” xainab ta galla mata
harara tace “to uban me xan maki, ni de
daukokuloli ki juye abincin nn don dasu xan
wuce gida , kuma islamiyya xan wuce,”
intisaar ta kamo hannunxainab din hawaye
ya cika idonta tace “Zainab ni kadae ce a nn
tsoro nke ji wllh,” zainab tayi dariya tace
“xaki saba ne ai, kuma naga ai yaya na
dawowa da yamma,” intisaar ta goge
hawayen idonta tace ” aa ni dae ki bari
anjima ki tafi don Allah,” xainab tace to naji
je ki dauko abu na juye maki abubuwan nn,
intisaar tace “ni ban san ina ne kitchen din
ba ai,” xainab tayi dariya tace “yaya bai xaga
dake gidan ba knn,” intisaar ta harareta
tace”wnn yayan naki mutum ne,” xainab ta
dinga dariya ta ja ta suka sauka falo suka
xaga ko ina na gidan, intisaar dae bbu
abinda ya burgeta game da gidan hasali ma
ita tsanar gidan tayi, dakinsa kadae taki
shiga duk da irin tilasta mata da xainab ta
dinga yi tace baxata shiga ba, xainab din
dae ta shiga ta fito.sae kusan karfe goma
suka karya da xainab, ta dinga ji kmr xainab
ta dawo gidan da xama kwata kwata. Karfe
sha daya xainab ta tattara ina ta ina taxata
tafi gida intisaar ta dinga kuka wae don
Allah kar ta tafi, xainab tayi ta kwantar mata
da hankali tare da assure dinta ae xata
kawo mata abinci da yamma.
.
Da yammar kuwa Zainab ta kawo mata
tuwan shinkafa da cous-cous sae dan
fankasau da miya kusan kala uku, sae
farfesun naman rago, intisaar tace ” xainab
na safen da kika kawo fa na nn har ynxu, ya
xanyi da wa innan kuma” xainab ta harareta
tace “to shi kuma yayan fa, ai ba ke daya
inna ke yi ma ba, ke dashi ne,” intisaar ta
tabe baki tace “to ai sae ki jira randa ya
dawo sae ki kai masa,” xainab ta girgixa kai
tace “intisaar knn, baki san ke mace bace
kece xaki jawo hankalin mijin ki gare ki, duk
wani tsoro da fargaba ki ajiye sa gefe ki
daure…..” intisaar ta dakatar da ita a fusace
“kinga idan baxa ki min maganar arxiki ba
kiyi shiru, ni fa ban dauke ya Aliyu matsayin
mijina ba fa, yanda aka tilasta masa aurena
nima tilasta min akayi, wllhwllh bana sonsa,”
xainab ta mike tace “to ai yyi kyausae kuyi ta
xaune a hkan, kinga tafiya ta sae da safe.”
intisaar bata ce mata komai ba duk da bata
ji ddin tafiyartata ba har ta fita daga dakin,
karfe goma tana kwance kan gadonta rike
da littafin hisnul muslim tana dubawa taji
shigowar motar Aliyu, gabanta ya fadi ta
mike xaune ta kashe wutandakin gaba
daya, ta takure gefe daya xuciyarta na
mugun bugu, har taji ya hayo sama ya bude
dakinsaya shiga ya rufe. Ta sauke ajiyar
xuciya ta koma kangadon tayi kwanciyarta
ta lullube da blanket. Washegari tana kan
darduma tana tilawa bayan ta idar da slln
asuba taji fitan Aliyu da motarsa daga gidan,
a xuciyarta tace ae indae irin xaman da
xasuyi knn baxae dinga cin ubanta ba
Alhamdulillah.Yau kwanan intisaar hudu a
gidan Aliyu, amma ko sau daya basu taba
haduwa dashi ba, in ya fita tun bakwae na
safe baya sake waiwayo gidan sae
karfegoma wani lkcn ma har sha daya na
dare, ko kadan hkn bae taba damunta ba
don ita gaba ma ya kai ta, ita kam bata taba
tunanin Aliyu xae bar ta ta kai har wnn lkcn
a gidansa ba tare da ya cuceta ba, sae daefa
bai san cin ta da shan ta ba. Yanxu kam ta
fara kwantar da hankalinta a gidan ta fara
sabawa da xaman kadaici, dama yana fita
xata fito ta gyara ko ina na gidan ta share ta
goge snn tayi moppin, ta fito da kwanukan
da taci abinci a daki ta wanke a kitchen ta
gyara kitchin din ta tsaftace ko ina, ta kanyi
mamakin inda Aliyu ke cin abinci safe da
ranadon tasan shi ba gwanin cin abinci a
waje bane da daddare kuma yafi shan tea
ko coffee, indae ta shigo kitchen da safe ta
kan ga mug din da yasha coffee da daddare
sae ta wanke ta maida inda yake.
Duk safe da yamma inna na ba xainab
abinci ta kawo mata wani lkcin zainab ta
dan tsaya taya ta hira wani lkcin kuma tace
sauri take duk da tafi tsayawa ma da
yamma, don da safe tana xuwa islamiyya,
intisaar ta sa zainab ta kawo mata novels na
turanci dayawa don ita bata fiye karanta
littafin Hausa ba kuma kallo ishenta yake
don wani lkcin sae ta yini bata kunna tvn
dakinta ba, karatun da take yi yana matukar
taimakonta don yana debe mata kewa
sosai, wani lkcin idan ta gaji da karatun ta
kan tafi garden tayi xamanta tana kallon
tsuntsaye, yau ma kmr kullum intisaar na
falo tana goge gogenta da ta saba, wajen
karfe karfe sha daya na safe ne don Zainab
duk ta bata mata lkci ta cika ta da surutu da
ta kawo mata abinci da safe bata barta tayi
aikinta ba don bata fi minti goma da barin
gidan ba intisaar ta fara gyare gyaren gidan
har lkcin kuma kayan barci ne jikinta,
muryar Aliyu taji bakin kofa yana waya duk
da bae shigo falon ba amma ya bude kofar,
gabanta yyi mugun faduwa ta mike a
tsorace tayi bayan kujera da gudu ta
durkushe a wajen tana xare ido, taji ya
karaso cikin falon tare da rufe kofar, bata
kara jin takunsa ba ko ina yyi tsit, ta rasa
inda ya shiga, a hankali xuciyarta na
bugawa ta dan leko daga bayan kujeran da
take ta gansa tsaye kmr mai naxari yanabin
ko ina na falon da kallo, ta maida kanta da
sauri tare da toshe bakinta gudun kar ta
fasa ihu jikinta ya dau rawa, can dai taji
yana hawa stairs har taji ya bude kofar
dakinsa ya shige, ta mike tsaye da sauri
jikinta na rawa tayi hanyar stairs da gudu
bata lura da ruwan dake cikin bucket da
take mopping ba tayi ball dashi ya kife a
wajen tsantsi ya kwasheta tun kan ta kai ga
fadawa kan centre table din dake gabanta
don kansa ta ga take shirin fadawa ta fasa
wani ihu, cikin ikon Allah bata wani buge
ba, amma taci wahala ledar da Aliyu ya ajiye
kan table dinma sae da ya fadi kasa, duk
kayan dake ciki su ka xube cikin ruwan da
ya malale ta ko ina a falon, intisaar duk ta
rude ta mike da sauri tana rike da cikinta ta
haye sama har tana tuntube ta bude dakinta
ta shige.Tana shiga daki taji ya bude kofar
dakinsa ya fito, takoma gefen gadonta da
sauri gabanta na faduwa ta rakube ta dinga
yarfe hannayenta tana hawaye, xuciyarta
kmr xae shige cikinta don tsoro, yau kam
tasan tata ta kare in ta shiga hannun Aliyu,
tayi kusan minti goma a hka amma bata ga
Aliyu ya banko kofar dakinta ba don ita
jiransa kawae take ya xo yaci ubanta kafin
hankalinta ya kwanta, ta mike tsaye da kyar
jikinta na rawa, taji an bude kofa
downstairs snn aka rufe, tayi kusa da
window dinta da sauri ta dan bude curtain
din tana lekan compound din,
.
tafiyar nn tasa yake ta kasaita yana sanye da
shadda fara yyi mugun masa kyau, har ya
isa kusa da motarsa dake ajiye a garage
don bae fiye fita da ita ba kuma da alamar
shigowarsa gidanaka wanke motar, taga
wani mutumi ya mika masa makullin motar
a ladabe snn ya juya ya bar gidan, ya bude
motar ya shiga ya tada ta maigadi ya bude
masa gate ya fice ta bi motar da kallo cike
da mamaki anya kuwa Aliyu ne wnn, sae a
lkcn ta tuna ashe ma ranar jumma’ah ce,