HAUSA NOVELINTEESAR 2

INTEESAR 2

kayan da xata saka taji an bude kofar, ta

juyaa tsorace tare da sakin abinda ke

hannunta a gigiceta fasa wani raxanannen

ihu tace “wayyoo Abbana nashiga uku,”

Zainab ta tsaya baki bude da mamaki tana

kallon intisaar, a hankali intisaar ta sulale

kasa ta xauna tare da dafe kirjinta da ya

kasa daina bugu da sauri,ta galla ma zainab

din harara duk da taji dadin ganinta tace ”

dubeta don Allah, baki iya sallama bne

malama xaki tsorata mutane,” zainab tayi

dariya tace “xa ma ki fadi gskya ne, wae ta

tsamman angonta ne, shine xata wani

wayance ma mutane” intisaar ta galla mata

harara da wasa tace” angon bnxa, meye

hadina dashi, ” zainab ta tabe baki tace ”

kya ji dashi dae,” snn ta karasa cikin dakin

ta ajiye basket din dake hannunta da leda ta

shiga fiffito da kulolin dake cikin basket din

da flask,intisaar ta xauna gaban madubinta

tana shafa mai zainab ta dago tana kallonta

tace “kin tashi lfya amaryarmu,” tayi kmr

bata ji ta ba, zainab tayi dariyar tsokana tace

“kice sae ynxu ma xakiyi sllhn, ina yayana,

nasan kin sa shi makara yau da gani,”

intisaar dae bata kara kallon inda zainab

take ba ta gama shafa mai ta shiga sa

kayanta wani material mai kyau orange n

milk colour,

.

Zainab ta sauka kicin ta dauko plates da

cups ta dawo dakin tana kallon intisaar

dake gyara fuskarta gaban madubi tace ”

wae yaya fa?” intisaar ta baxa mata hannu

alamar ita ma bata sani ba, xainab tace

“joke apart intisaar da gske baya nn,”

intisaar tace ” Allah ni ban gansa ba ma tun

jiya, daxu dae naji fitar motarsa” zainab ta

tabe baki tace “to Allah ya kyauta, kice jiya

ma baki ci ‘yar kazar nn da madara ba”

intisaar ta sauko kasa ta xauna kusa da

xainab kmr xata yi kuka tace “inna fa?”

xainab tayi dariya tace “ke dae bari, ai yau

karfe 5 duk muka tashi a gidan nn wae xa

tayi maku waina kuma a murhu xatayi, snn

xata dama kunun gyada ta dafa muku

ruwan lipton hadadde, ae mun aikatu yau,

har da su farfesun kaxa da kayan ciki, duk

ga su nn” intisaar tayi dariya sosai tace

“Allah sarki innata, amma de ba yanxu xaki

tafi ba ko xainab?” xainab ta galla mata

harara tace “to uban me xan maki, ni de

daukokuloli ki juye abincin nn don dasu xan

wuce gida , kuma islamiyya xan wuce,”

intisaar ta kamo hannunxainab din hawaye

ya cika idonta tace “Zainab ni kadae ce a nn

tsoro nke ji wllh,” zainab tayi dariya tace

“xaki saba ne ai, kuma naga ai yaya na

dawowa da yamma,” intisaar ta goge

hawayen idonta tace ” aa ni dae ki bari

anjima ki tafi don Allah,” xainab tace to naji

je ki dauko abu na juye maki abubuwan nn,

intisaar tace “ni ban san ina ne kitchen din

ba ai,” xainab tayi dariya tace “yaya bai xaga

dake gidan ba knn,” intisaar ta harareta

tace”wnn yayan naki mutum ne,” xainab ta

dinga dariya ta ja ta suka sauka falo suka

xaga ko ina na gidan, intisaar dae bbu

abinda ya burgeta game da gidan hasali ma

ita tsanar gidan tayi, dakinsa kadae taki

shiga duk da irin tilasta mata da xainab ta

dinga yi tace baxata shiga ba, xainab din

dae ta shiga ta fito.sae kusan karfe goma

suka karya da xainab, ta dinga ji kmr xainab

ta dawo gidan da xama kwata kwata. Karfe

sha daya xainab ta tattara ina ta ina taxata

tafi gida intisaar ta dinga kuka wae don

Allah kar ta tafi, xainab tayi ta kwantar mata

da hankali tare da assure dinta ae xata

kawo mata abinci da yamma.

.

Da yammar kuwa Zainab ta kawo mata

tuwan shinkafa da cous-cous sae dan

fankasau da miya kusan kala uku, sae

farfesun naman rago, intisaar tace ” xainab

na safen da kika kawo fa na nn har ynxu, ya

xanyi da wa innan kuma” xainab ta harareta

tace “to shi kuma yayan fa, ai ba ke daya

inna ke yi ma ba, ke dashi ne,” intisaar ta

tabe baki tace “to ai sae ki jira randa ya

dawo sae ki kai masa,” xainab ta girgixa kai

tace “intisaar knn, baki san ke mace bace

kece xaki jawo hankalin mijin ki gare ki, duk

wani tsoro da fargaba ki ajiye sa gefe ki

daure…..” intisaar ta dakatar da ita a fusace

“kinga idan baxa ki min maganar arxiki ba

kiyi shiru, ni fa ban dauke ya Aliyu matsayin

mijina ba fa, yanda aka tilasta masa aurena

nima tilasta min akayi, wllhwllh bana sonsa,”

xainab ta mike tace “to ai yyi kyausae kuyi ta

xaune a hkan, kinga tafiya ta sae da safe.”

intisaar bata ce mata komai ba duk da bata

ji ddin tafiyartata ba har ta fita daga dakin,

karfe goma tana kwance kan gadonta rike

da littafin hisnul muslim tana dubawa taji

shigowar motar Aliyu, gabanta ya fadi ta

mike xaune ta kashe wutandakin gaba

daya, ta takure gefe daya xuciyarta na

mugun bugu, har taji ya hayo sama ya bude

dakinsaya shiga ya rufe. Ta sauke ajiyar

xuciya ta koma kangadon tayi kwanciyarta

ta lullube da blanket. Washegari tana kan

darduma tana tilawa bayan ta idar da slln

asuba taji fitan Aliyu da motarsa daga gidan,

a xuciyarta tace ae indae irin xaman da

xasuyi knn baxae dinga cin ubanta ba

Alhamdulillah.Yau kwanan intisaar hudu a

gidan Aliyu, amma ko sau daya basu taba

haduwa dashi ba, in ya fita tun bakwae na

safe baya sake waiwayo gidan sae

karfegoma wani lkcn ma har sha daya na

dare, ko kadan hkn bae taba damunta ba

don ita gaba ma ya kai ta, ita kam bata taba

tunanin Aliyu xae bar ta ta kai har wnn lkcn

a gidansa ba tare da ya cuceta ba, sae daefa

bai san cin ta da shan ta ba. Yanxu kam ta

fara kwantar da hankalinta a gidan ta fara

sabawa da xaman kadaici, dama yana fita

xata fito ta gyara ko ina na gidan ta share ta

goge snn tayi moppin, ta fito da kwanukan

da taci abinci a daki ta wanke a kitchen ta

gyara kitchin din ta tsaftace ko ina, ta kanyi

mamakin inda Aliyu ke cin abinci safe da

ranadon tasan shi ba gwanin cin abinci a

waje bane da daddare kuma yafi shan tea

ko coffee, indae ta shigo kitchen da safe ta

kan ga mug din da yasha coffee da daddare

sae ta wanke ta maida inda yake.

 

Duk safe da yamma inna na ba xainab

abinci ta kawo mata wani lkcin zainab ta

dan tsaya taya ta hira wani lkcin kuma tace

sauri take duk da tafi tsayawa ma da

yamma, don da safe tana xuwa islamiyya,

intisaar ta sa zainab ta kawo mata novels na

turanci dayawa don ita bata fiye karanta

littafin Hausa ba kuma kallo ishenta yake

don wani lkcin sae ta yini bata kunna tvn

dakinta ba, karatun da take yi yana matukar

taimakonta don yana debe mata kewa

sosai, wani lkcin idan ta gaji da karatun ta

kan tafi garden tayi xamanta tana kallon

tsuntsaye, yau ma kmr kullum intisaar na

falo tana goge gogenta da ta saba, wajen

karfe karfe sha daya na safe ne don Zainab

duk ta bata mata lkci ta cika ta da surutu da

ta kawo mata abinci da safe bata barta tayi

aikinta ba don bata fi minti goma da barin

gidan ba intisaar ta fara gyare gyaren gidan

har lkcin kuma kayan barci ne jikinta,

muryar Aliyu taji bakin kofa yana waya duk

da bae shigo falon ba amma ya bude kofar,

gabanta yyi mugun faduwa ta mike a

tsorace tayi bayan kujera da gudu ta

durkushe a wajen tana xare ido, taji ya

karaso cikin falon tare da rufe kofar, bata

kara jin takunsa ba ko ina yyi tsit, ta rasa

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button