HAUSA NOVELINTEESAR 2

INTEESAR 2

kashe ac dake dakin ta lulube tadalilin rawar

sanyin da takeyi, ranar dae daga ita har

momy basuyi bacci ba, momy ta rasa abinda

ke damun ‘yar tata, duk ita ma hnklinta ya

tashi.

Gari na wayewa momy taje ta sami abba

ganin yanda jikin nata yyi tsanani, gashi sae

aikin kuka take, duk ita ma tabi ta daga

hnklinta don akwae soyayya da shakuwa

mai karfi tsakaninta da ‘yar tata don ita

kadae take gani taji ddi idan ta tuna mijinta

na farko umar, har daki abba ya shigo duba

intisaar din, “me ya sameki fatima, ina ke

maki ciwo?” ya tambayeta dadamuwa yana

yaye bargon da momy ta lullubeta dashi, ita

dae ba baki sae kuka, abba yashiga

lallashinta yana cewa”damabaki da lfya ne

fatima, kuma bakiyi maganaba tun jiyan?” ta

girgixa masa kai kawae, xainab tashigo

dakin hankalinta a tashe bayan ta tambayi

ihsaan ina intisaar don ita har tayi shirin

islamiyya da yake tare suke wuce, ihsaan

tace mata “my aunty is sick,” hkn yasatayo

bangaren nasu da saurinta, abba ya dubi

xainab da tashigo yace”je ki ki kiramin Ali

xainab,” tace to sannan ta fice da sauri, a

hanya suka haduda kursum take tambayrta

ko intisaar ta shirya don ita ma shirin

islamiyyar tayi, tunda Aliyu yyi masu mugun

duka ranannan suka fara xuwa makaranta

gaba dayansu dama, xainab tace “bata da

lfya baxa taje ba,” kursum tace “hva de me

ya sameta,” xainab ta yarfehannu tace nima

bn sani ba ynxu ma ya Aliyu xan kira abba

ma yana can, kursum tayi sashin nasu da

sauri xainab kuma ta tafi kiran Aliyu, tana

isa tayi sllma ta shiga palon, baya nan, tayita

kwada sllma ko yana cikin daki amma shiru,

sanin halin yayan nata ne ya sanyata

karasawa cikin bedroom din nasa yana ko

xaune laptop a gabansa yasa earpiece

kunne daya yana danna laptop, ya daka

mata tsawa a fusace yana cewa”baki da

hnkli ne don ubanki ko ke jahila ce,baki san

idan kika yi sllma a waje kika ji shiru gaba

xakiyi ba, xaki afko min cikin daki, ban

hanaki wannan habit din ba,” au ashe ma

yana jinta, ta tabe baki cikin rashin damuwa

tace “dama abba ne ke kiranka” ta juyafuu

xata wuce ya mike da sauri yana cewa

“xainab, xainab,” amma bata tanka masa ba,

ya fito palon da sauri har ta fice ya bita da

sauri yana kiranta, ta dawo tana kallonsa

fuskarta a hade tace”gani,” me yasa abba ke

kirana, ya tambayeta yana kallonta don dae

yasan sae da dalili ake kiransa, don kan

abba ya kirasa sau daya ya kira haisam sau

goma,”nima ban sani ba, intisaar dae ce

bata da lfya shine yace naje na kiraka” ta

fadi tana kallonsa, gabansa ya fadi yace “to

menayi ake kirana” tace “ni kuma ina xan

sani” hnklinsa ya tashi yace “me tace wa

abban?” tace “oho, ni ina shigowa abba

yace nayi maxa naje na kiraka” don ta gaji

da tambayoyin nasa, bai damu da ohon

datace masa ba ya kara tambayrta “ya mood

din abba yake” tace a kage “kai yaya ni ma

ban sani ba abba nacan yana jiranka,” ta

juya ta yi gaba ta barshi nan a tsaye. Ya bita

da sauri kuma yana kiranta, ta juya rai bace

tana kallonsa yace “ina abban?” tace”yana

can dakin momy” ya xaro ido yace”yana

me?” tace “oho! tayi gaba abinta” ta fara

suspect dinsa ita kam. Tana komawa

sashinsu intisaar abba ya tambayeta meya

tsayar da ita kuma ina Aliyun, tace”nemansa

nke a gidan abba amma gashi nan xuwa” ya

dubi momy da ta xauna tayi jigum yace “ki

hado mata tea xainab,” ta mike tace to

sannan ta fita, tana fita sae ga inna, tun

daga waje suka dinga jin muryarta kmr

speaker tana cewa”me ya samu intisaar din,

ni rahmatu,” abba ya juya rai bace yana

kallonxainab yace “donuwarki ca nayi ki ji ki

gaya wa inna taxo ta daga mana hnkli a nan

ynxu?” xainab ta mike da sauri ido a waje

tace “wllh tllh abba ban je wajen inna yau

ba ni,” abba bae sake cewa komai ba har

inna ta shigo dakin, “bukar me ya sameta

wae” abba ya dubeta yace “shine ae xa a

dubata don bbu wanda yasani,” inna tasaki

salati tana girgixa kai tace “Allah ubangiji

dae ya bata lfya wllh duk hankalina ya tashi

da aka je aka gya min,” abba bae sake tanka

mata ba tana ta surutanta, illa Aliyun da yake

jira, murya can ciki Aliyu yyi sllma, duk

jikinsa yyi sanyi, ynxu yarinyar nan sae ta iya

bude baki tace yyi mata wani abu dama,

inna ce ta amsa masa da karfinta tana cewa

“maxa shigo,” hankalinsa ya kara tashi ya

shigo palon ya tsaya yana waige-waige kmr

munafuki, abba yace”karaso mana” da kyar

yyinamijin kkri ya shiga dakin, ya rusuna ya

gaida abba don duk yau bai je gaisheshi ba

gashi har karfetara, ya juya ya gaida inna

ma sannan yace”abba gani,”

.

Dama fatima ce bata da lfya, shine nace a

kiraka ka dubata, abba ya fadi yana kallonsa,

Aliyu ya saki ajiyar xuciya, sannan ya maida

dubansa ga kangadon yana kallonta, idonta

a lumshe yake, duk da dae ba bacci take ba,

ya karaso kusa daita yace “meke damunki?”

tayi shiru kmr mae bacci, hkn ya bata masa

rai don yasan idonta biyu, a dan fusace

yace”kinajina xakiyi min banxa?” inna cikin

tsawa tace “kai mahaukacin wani gari ne,

baka ga bacci take ba yarinya tana fama da

kanta xaka dinga mata ihu,” xainab ta

karasa kusa da ita tana bubbuga kafarta a

hankli tana kiran sunanta, ta bude ido tana

kalln xainab din, Aliyu ya juya yana kallon

abban nasa yace “ko dae a wuce da ita clinic

kawae abba” inna tayi karaf tace”wllh bbu

inda xa a kaita, gamu da likita a gida kace

xa a wuce da ita wani wajen, meye amfanin

ka” Aliyun ya dubeta rai bace yace “to ni din

Allahn musuru ne da xan san abinda yke

damunta,” cikin tsawa inna tace “shiyasa

naga an kai fadila asibitida bata da lfya, don

ubanka ba kai ka dubata ba ka bata

magunguna da allurori ba kuma gashi nan

ta warke,” Aliyu ya dubeta a walakance ya

kauda kai kawae, abba yace “shknan bari a

kaita asibitin ka iya tafiya” da sauri yace “aa

abba bance baxan dubata ba ae, guri nake

jira su ban na dubata,” ya fadi yana

kallnsuinna, haisam ya shigo dakin da

sllmrsa ya karasa kusa da intisaar din ya

xauna cike da damuwa yana kallonta yace

“intisaar me ya sameki, dama jiya baki dalfya

baki yi magana ba,” ta sunkuyar da kanta

kawae sae hawaye, nanya shiga lallashinta,

ya dube abba yace “asibiti xamu wuce

abba?” inna tace “asibitin lfya ga likita a

gida, ynxu xae dubata ae” sllmrsu hajiya da

umma ne yasa kowa yyi tsit a dakin, momy

ce kadae ta amsa masusuka shigo suna

cewa ashe abinda ya faruknan, momy ta

basu waje suka xauna sannan suka gaisa,

suka tambayeta mae jiki tace masu da sauki,

hajiya tace Allah sarki duk ta rame sae kace

warce tayi sati tana jinya, umma tace wllh

kuwa baiwar Allah, inna ta tabe baki tace

“ikon Allah” xainab ta girgixa kai cike da

takaici, ynxu har anje an barbada masu

shine suka kwaso jiki suka xo gulma,

kumatasan baxae wuce kursum ba ko

rahma, abba ya dubi gaba dayansu yace “to

ae kwa bashi waje yyi aikinsa de ko” hajiya

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button