HAUSA NOVELINTEESAR 2

INTEESAR 2

ta mike tana cewa”me xae hana, Allah dae

ya bata lfya yasa xakkan jikine,” suka mike

gaba dayansu har da yaran xasu bar dakin,

Aliyuyace “to..to abba ya xa ayi treatin din

nata?” abba da har ya kai bakin kofa xae fita

ya juya yana kallonsa cikin rashin fahimta

yace “kmr ya fa?” yace”aa…dama…emm, to to

ae naga sae da magunguna da allurori xa

ayi treatn din nata, kuma ni….” sae kuma yyi

shiru yana kallon tagan dakin, abba

yyimurmushin takaici ya girgixa kai yace “to

nawa xa a baka?” inna ta mike ta saki salati

tana girgixa kai tace “ita intisaar din sae…..”

da sauri abba ya katse ta yace “aa baaba ae

hakkinsa ne bari a basa” nawa ne kudin

treatment din gaba daya? Abba ya tambaya

yana kallonsa, cikin bacin rai haisam yace

“abba ka bari na wuce da ita asibiti kawai,”

abba yyi saurin cewa “aa haisam ka bari xae

dubata,” abba ya sake tambayrsa nawa xae

basa, yyi shiru kmr me lissafi sannan yace

ba tare da ya kalli abban nasa ba “dubu

takwas da dari biyar gaba daya,” abba yyi

murmushi, haisam cike da takaici yace “to

yyi kyau, ka dubatani xan baka,” da sauri ya

juya yana kallon haisam din rai bace yace

“to da baki na xan siyo kayan ne koya? Ko

kuma ina da kudin xan tsaya cewa abba ya

bani,” inna cikin ihu tace “Allah ya babbake

mae krya sannan ya tsinemasa,” Aliyun ya

juya ya galla mata harara sannan ya dauke

kansa, haisam ya ciro dubu biyar daga

aljihunsa ya mike xae fita abba yace ina

xaka, yace xan dauko kudi ne,abba yace

nawa ne a wajen ka ynxu, yace dubu biyar,

abba ya ciki dubu hudun haisam ya mikawa

Aliyun ya karbe yana kirgawa, duk wannan

abinda akeyi a kan idonsu hajiya ne, hajiya

taji kmr ta maida dan nata ciki don murna,

sae murmushi take yi, umma kuma ji tayi

kmr ta tsine ma haisam da bai yo hali irin ta

Aliyu ba, shekaranjiya tace ya bata dubu

goma yace bai da, amma sae gashi ynxu ya

kirgo har dubu biyar ya bada don a duba

wata bnxa ita kam bata san irin dan da Allah

ya bata ba, momy kam sunkuyar da kanta

tayi tana jin duk abinda sukeyi cike da

takaici, intisaar kuwa idonta ta rufesbda

axabar da take ji ko ina na jikinta ciwo yke

mata barin ma kanta sannan kuma ga

ciwon mara shima ya kunno kai, abba kam

tuni ya fice su hajiya suka bi shi a baya a

xuciyarsu suna fatan Allah yasa cikita yo,

don rahma ca tayi masu amai take ta

kwararawa, Aliyu ya dube inna yace”a bata

tea kafin na dawo, xan je siyo abinda ya

kamata,” ya fice haisam ya bisa a baya da

sauri, sai da suka kai tsakar gidan sannan

yace “canjin nawa xaka dawo da knan?”

Aliyu yace kmr ya, haisam yace eh ae dubu

tara aka baka, kuma dubu takwas da dari

biyar kace, Aliyu yyi masa wani irin kallo

sannan yace “to da kafa xanje siyo

magungunan?” sannan yyi tsakiya wuce

yana cewa “dn ma kun samu xan bata lkcn”

.

. Su Aliyu na fita inna ta mike tana tambayr

intisaar din me xata ci, ta girgixa kai alamar

ba komai, xainab tace”to ki daure kisha tea

din” inna ta dauki kofin ruwan shayin ta isa

kusa da ita tana cewa “tashi ki sha kafin ya

dawo to” intisaar ta girgixa kai murya can

kasa-kasa tace “wanka xan fara yi,” momy ta

shiga bathroom ta hada mata ruwan

wankan sannan ta mike da kyar jiri na

kwasarta ta shige bayin, ko da ta fito rawan

sanyi ta dinga yi, inna ta lullubetatana cewa

“ikon Allah, ciwan lkci daya ya kwantar da

ita,” ya haisam ya shigo dakin yana tambayr

ko Aliyun ya dawo,inna tace “ina fa! yana

can yana sokwanci” haisam ya girgixa kai

yace “ni dae wllh inna nafi son a kaita

asibiti,” inna tace “wae ni kuna bani mamaki

wllh, ga likita a gida kuyi ta kiran asibiti,”

haisam yace “to shknan, ni xan wuce kd ne

ynxu ina da wani aiki a can amma yau xan

dawo in’sha Allah,” inna tace “to Allah ya

kiyaye” yace “ameen” sannan ya karasa kusa

da intisaar yana kallnta yace “Allah ya

sauwake kanwata kinji” tayi murmushi, a

hnkli tace “ngdyayana” yyi ma momy ma

sllma sannan ya fita. Da kyar inna ta lallabata

tasha kunun da ta dama mata, xainab sae

fama kallon agogo take yi dn har sha daya

ya wuce, tun kusan karfe goma da Aliyu yaje

siyo magunguna har ynxu bai dawo ba, tuni

bacci ya dauke intisaar din bayan inna ta

bata paracetamol kafin Aliyun ya dawo,

amma har karfe sha biyu bbu Aliyu bbu

lbrinsa, “kai jama’a ko dae wannan yaron

bata yyi ne” inna ta fadi tana kallon momy

da xainab dake dakin bakinta a bude, momy

dae bata ce komai ba, xainab ta tabe baki

ita ma bata ce komai ba, wasa-wasa har

karfe biyu bbu Aliyu, inna na idar da sllh

tana xaune kandarduma cikin ihu tace

“amma wannan anyi tsinannan yaro,” daga

momy har xainab sae da suka raxana sbda

irin bude muryar da inna tayi, momy tace

“kai inna, kika san uxurin da ya tsayar

dashi,” a fusace inna tace “yaci ubansa shi

da uxurin,” ku bni waya na kira bukar,

momy tayi ma xainab ido alamar kar ta kira

mata abban, inna ta mikawa xainab din

wayar tana cewa “maxa kira min uban

nasa” xainab ba don ranta yaso ba tace ma

inna baya xuwa bayan ta kara wayr a kunne

kmr me kira, don ita da momy ta barta kiran

abban xatayi, ita kam bata san irin yayan

nata ba, basu san tuni abba ya kira momyn

yana tambayrtajikin intisaar din ba tace

masa da sauki sosae, yace Aliyun ya bata

duka magungunan tace masa eh sannan

sukayi sllma, xagi kam Aliyu ya sha shi a

wajen inna ba adadi, har da dan hawayenta,

“ni da nasan abinda tambadadden yaron

nan xae yi knan da asibiti kawae na bari

muka wuce, gashi ynxu yrnya na ta shan

axaban ciwo ba magani, shi kuma bukar na

rasa uban me xae sa ya dinga kashe

wayarsa ni kam, ynxu wa xae kai mu

asibitin gashi haisam ba ya nan,” daga

momy har xainab bbu wanda ya tanka

mainna, intisaar kam jikinta yyi xafi sosae

kmr wuta, hka inna ta ishesu da mita tana

hawaye, wajen karfe uku da rabi wayan

intisaar yyi kara xainab ta dauka tana kallon

me kiran, faruuq ne, da har xata ajiye don

bacci intisaar din take yi sae kuma ta fasa ta

daga, suka gaisa ya tambayeta intisaar din

fa, tace “bacci takeyi wllh, bata da lfya,” cike

da damuwa yace “subhanallahi, me ya

sameta” xainab ta yarfe hannu tace “wllh

bamu sani ba, tace dae ciki da kantake mata

ciwo,” yace “tun yaushe?” tun jiya da

daddare wae,yace “ya salam! kunje clinic

ne?” tayi shiru ta rasa me xata ce, yyi saurin

cewa “ohk… Gani nan xuwa,” ya kashe wayr,

inna tace “faruqu ne?” xainab ta gyada mata

kai kawai, cikin minti goma sha biyar faruuq

ya iso gidan, hanklinsa ya tashi sosae, momy

da ta bar masu dakin ya rage inna daxainab

kawae, ta tashi xaune tana kallon faruuq din

da ya sata gaba yana tambayrta inda ke

mata ciwo, cikinta t.a nuna masa da kai,

yasa hannu ya danna cikin nata ta xaro ido

tace “waii! ciwo yake min” me ya buge ki a

nan ya tambayeta yana taba goshinta da yaji

xafi sosae, ta girgixa masa kai kawae sae

hawaye, duk ya rude ya shiga lallashinta

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button