INTEESAR 2

tallabota, ta fada jikinsa ya turata da sauri
sannan yyi maxa ya riko hannunta dn
faduwa xatayi, ya fara fixgarta kmr wata
dabba tana binsa jikinta ba kwari sae jiri
dake kwasarta amma bae bari ta fadi ba, yyi
sashinsu daita, har bakin kofarsu ya kaita ya
bude kofar yana kallonta, duk a tsorace
take, ya tura ta ciki har tana faduwa yyi
gaba, momy ta taso da sauri ganin yanda
‘yar tata ta fado falon tana cewa “lfya
intisaar,”
Karfe tara abba ya shigo duba intisaar, har
lkcn inna na falonsu bata tafi ba, abba ya
shigo mata da fruits da tsire a leda ya ajiye
mata yana tambayarta ya jikin, tace “da
sauki abbana” sannan ta mike ta shige
bedroom ta bar masu falon, abba ya dubi
inna yace “nan xaki kwana knan yau?” tace
“aa dama kai nake jira, kasan iskancin da
wannan dan naka yyi mana yau” abba yyi
shiru yana kallonta, ta tabe baki tace “wllh
bkayi sa’an da ba bukar, shanya mu yyi a
nan ya gudu da dubu taran da kuka bashi,
sae wannan yaron faruuq yaxo ya dubata
kmr xata mutu” abba ya tsura mata ido yana
kallonta ya kasa cewa komai, “wllh ko minti
goma ba ayi da fitan yaron ba ka shigo, tun
safe yaki barin gidan nan yana kanta, gashi
ynxu jiki alhmdllh, yaron mutunci ne wllh”
abba ya jinjina kai cike da takaici yace “to
shknan yyi masa kyau, hkn yaga yafimasa
alkhairi,” inna ta mike ta tabe baki tana
cewa “ka rakani bangarena” yace “to
sannan yyi sallama da momy, ta rakosu har
bakin kofa tana ma inna sae da safe. Karfe
goma haisam ya shigo duba intisaar, momy
tace “kar dae ynxu ka dawo haisam” yace
“wllh kuwa momy,” bae bar sashin nasu ba
sae kusan karfe sha daya, suna ta hira da
momy da intisaar da ynxu bata jin ciwo a ko
ina na jikinta. Da safe ita da ihsaan suka je
gaida abba, kmr ba ita tayi ciwo jiya ba,
Aliyu na xaune a falon kansa sunkuye bayan
abban nasa yyi masa tatas, intisaar ta nemi
gefe ta xauna ganin Aliyu duk sae jikinta ya
mutu, ta gaida abba ya amsa da fara’arsa
yana tambayarta jiki, tayi murmushi tace
abba da sauki, ta kalli Aliyun da har ynxu
kansa a kasayake tace “ina kwana yaya,” ya
dago yana kallonta idonsa yyi jajir ya kauda
kai murya can ciki yace “lfya lau,” ta mike
tana kallon abba tace”abba sae anjima,”
yace “yauwa intisaar, kin dae sha
magungunanki dae ko,” tace “eh abba
nasha” yace “to yyi kyau” sannan suka fice,
Aliyu ma ya mike yana kallon abban nasa
yace “Allah ya huci xuciyarka abba,” abba ya
dauki kudin da Aliyun ya ajiye masa ya
watsar masa dasu yace “nace kaje da su
bama bukata,” Aliyu yyi jim sannan yace
“kayi hkuri abba, ita ma kanwata ce bbu
yanda xa ayi na karbi kudi wae don xan yi
treatn dinta, na gya mka dalilae na nayin
hkn, kuma bayan hka ma ni bn samu na yi
treatn dinta ba ” abba ya galla masa harara
yace “dalilanka na bnxa, ina ruwanka da
uwartaka da har xakayi hkn wae sbda taji
ddi, wae kae me uwa, ka burge uwarka
amma kuma ka xubda kimarka a idanun
mu, kai ko kunya ma bka ji ba, wawa
kawae, da’alla get out malam” Aliyu ya juya
jiki ba kwari ya bar falon. Da yammar ranar
ummi kanwar faruuq taxo duba intisaar,
yayan nata ya ajiye ta sannan ya wuce, sun
jima suna hira da intisaar da xainab kmr da
can sun saba sannan suka kaita gun inna,
inna ta rasa inda xata sata don farin ciki,
tsaraba ta hada mata lkcn da faruuq din ya
kirata wae yana waje don baxae shigo ba
wae, momyma ta hada mata nata abun
arxikin sannan intisaar ta rakota don xainab
tuni hajiya ta aika khadija ta kira mata ita, a
bakin gate suka gaAliyun a xaune fuskar
nan tasa bbu alamar rahama, ummi ta
gaisheshi, ya dago kai yana kallonta fuska
daure yace “lfya,” intisaar ma ta gaidashi
gabanta na faduwa yyi bnxa da ita har suka
fice, ummita juya tana kallonta tace “waye
wannan kuma,” intisaar ta kirkiro murmushi
tace “babban yayanmu ne” don ita ynxu
tunanin yanda xatashiga gidan yana bakin
gate din take, har bakin motar faruuq din
intisaar ta rakata suka yi sllma faruuq ya
kashe mata ido yace “sae nakiraki bbyna,” ta
kauda kanta da sauri tana murmushi ta bar
wajen, ya ja motar suka wuce, ta kasa shiga
gate din ta tsaya a waje, har wani bari
jikinta yake yi don tsoro.
Dago ta momy tayi tana kallon ta tace “jikin
ne intisaar?” ta girgixa kai ta mike da
kyartace “aa faduwa nayi,” bedroom ta
shige momy ta bita da kallo ta kasacewa
komai tausayin yar tata ya cika ta, ita ta rasa
abinda ke damunta. Washegari da ciwan
kan ta tashi amma bata bari momy ta gane
ba don bata son tana daga wa uwarta ta
hnkli, faruuq ya kirata da safen yana
tambayr jikinta tace yyi sauki sosae, tare
abba ya shigoda Aliyu falon nasu wajen
karfe tara, lkcn innana nan a xaune don tun
karfe bakwae ta iso sashin nasu da kunun
ta da kosae ta kawo ma intisaar, ihsaan ta
rungume abban nata ya daga ta sama yana
cewa”how re yhu momyna” tace fyn sir, ya
dubi intisaar yana murmushi yace “ya jikin
fatima? Tayi murmushi tace “da sauki
abbana,” to Allah ya kara sauki, kina shan
magani dae ko? Tace “eh abba ina sha,”
Aliyu ya nemi guri ya xauna yana satan
kallon momy dake xaune tana linke kayan
ihsaan, ba tare da ya kalleta ba murya can
ciki-ciki yace “ina kwana,” tayi kmr bata ji sa
ba, ya tabe baki ya gaida inna ita ma tayi
masa bnxan, ya dake yana duban intisaar
din yace “ya jiki,” ta sunkuyar da kanta tace
“da sauki,” sannan tace masa”ina kwana” ba
tare da ya kalleta ba yace”lfya lau,” ya sata
kallonabbansa da ke kallon Tv, yace ba tare
da ya kalleta ba”kwaso min medicines din
da kike sha nagani,” ta mike jiki ba kwari ta
shiga bedroom ta kwaso masa
magungunan da faruuq ya bata ta durkushe
gabansa ta xubesu tana kallonsa, inna ta
tabe baki tace “ko uban me xae yi dasu idan
ba gulma ba,” bae tanka mata ba ya shiga
dudduba magungunan ya cire guda biyu a
ciki yace “ki ajiye wa innan kar ki sha,” to
kadae tace, inna tayi karaf tace “akan wani
dalilin, kafi sa sanin aikin nasa ne malam,”
da’alla kwashe magungunanki ki maida
kirabu da wannan gantalallen, dariya ma
abun yaba Aliyun, abba ya dubesa
yace”sbda me xata ajiye su,” ya shafa kanshi
yace “sbda aikinsu kusan iri daya ne gaba
daya, dama xan karo mata wasu ne shiyasa
nace ta ajiyesu,” abba yace “no ka bari ta
gama da su tukunna sae ka bata wanda
xaka batan, shima yasan abinda ykeyi ae
yaron,” Aliyun yyi shiru bai ce komai ba, inna
ta galla masa harara tace”munafukin bnx
kawae, idan yaga ubansa ya dinga yi kmr na
Allah,” Aliyun ya mike yana kallon abban
nasa yace “abba xan wuce clinic sai na
dawo,” inna tace “kaji makaryacin bnxa, ca
xakayi xaka je gantali,kai din aiki kke xuwa,”
ya tabe baki bae tanka mata ba, ya dan kalli
intisaar din ya watsa mata hararar tsana
yace “Allah ya sauwake,” ya juya ya fice.
Suna tsakar gidagaba dayansu intisaar na