HAUSA NOVELINTEESAR 3

INTEESAR 3

kakarin Aman inteesar yaji, ya saketa da

sauri ya mike tsaye ya fice daga dakin,

safeena ta bi sa da kallo xuciyarta na mugun

kuna, kasan dakin ya tarar da ita tana ta

amai ya kamata har ta gama snn ya gyara

mata jikin ya gyara dakin ya kwantar da ita

kan gado, ta rikesa muryarta na rawa tace

“sanyi nake ji yaya,” ya lulluba mata bargo

snn ya dauki I.v din da ya ajiye gaban

madubinta xae fita ya juya yaga kallonsa

take, ya dawo yana kallonta yyi murmushi

yace “kina san wani abu ne,” ta girgixa

masa kai yace “kinsan bikin Zainab saura

kwana goma ko,” ta mike xaune da sauri

tace “da gske yaya, ni ba a gaya min ba to,”

ya kamo hannunta yace “ae sun san baki da

lfya, ki bari nxt wk sae mu tafi gidan kafin

nn jikinki ya kara kwari,” ta marairaice kmr

xata yi kuka tace “to ba kila xuwa tayi ranan

ta gaya min ba ka koreta,” yace “ba ta ji ne,”

tace “to yaya wa xata aura” yana kallonta

yace “faruuq,” ta wara idonta ta fada kansa

cikin jin ddi tace “don Allah da gske yaya, kai

amma naji ddi wllh, ka bani nmbr ya faruuq

din” yace “to anjima xan baki, xanje gida

ynxu me xan ce inna ta girka maki?” tayi

shiru sae kuma ta bata rae ita da ba ma son

cikin take ba, yace kinyi shiru, tana

hararansa tace “kace mata ina da ciki ne,” ya

daga hannayensa da sauri yace “A’a” yana

girgixa kai, ta koma ta kwanta tace “dan

wake nake so ni,” yace “to, sae na dawo, kar

ki sha ruwa kar amai ya takuraki,” bata ce

masa komai ba yayi hanyar kofa, duk wnn

abinda suke safeena na labe tana jinsu, tana

jin xae fito ta bar wajen da sauri ta shige

dakinta tana murmushin mugunta, yana

fitowa ya shiga dakin safeenar

.

Bayan kwana biyu safeena ta samu ta lallaba

Aliyu wae xata gun wata yar uwarta, ya ko

barta har da bata kudi da makullin mota

dayake ta iya drivin tana ta murna a

xuciyarta tana cewa lallai sae yanda tayi da

Aliyu, ynxu kam ta yrda yana tafin hannunta

amma dae ba duka ba, tunda bata isa ta

hanasa xuwa gun Inteesar ba, amma komai

ya kusan xuwa karshe, ta fada a fili tana

murmushi, cikin kwanakin nn Aliyu na da

aiki ssae a clinic don hka ya gwammace da

ya bar Inteesar kadae a gida gwara ya

dinga tafiya da ita don tana bukatar kulawa

ssae, hka ko ya dinga yi kullum shi xae

shiryata da safe yyi ma safeena sallama su

wuce asibiti, hkn yyi mugun tada ma

safeena hankali to ta ya xa’a yi ta aikata

abinda suka sha wahala kafin su samu

bayan baya barinta a gida., ita kam Inteesar

ko kadan abinda Aliyu ke mata baya burgeta

don dai dae da second daya bata son cikin

jikinta, kuma tasan sbda cikin yake mata

hka, wani mugun tashin hankali ke xuwa

mata idan ta tuna cikin Aliyu ne jikinta, Ana

saura kwana uku bikin Zainab ya kai ta gida

duk da ba a son ranta ba don bata son su

san tana da ciki, amma ashe duk ya gaya

masu uwarsa ce kadae be gaya ma ba sae

umma, inna duk ta rikice masa wae cutar

jikarta kawae yake gashi duk ta fige ba kyan

gani, shi dae bae tanka ma inna ba ya fice,

Inteesar dae na kwance falo sae mayar da

numfashi take don da kyar ta iya karasowa

cikin gidan bayan sun sauka daga mota,

kuma da asibiti ne baya barinta ta taka da

kanshi yake daukarta su shiga ciki, inna tace

“to wae wani irin jarababben cikine wnn

dake neman kashe min ke,” ta mike xaune

tana hararan inna kmr xata yi kuka tace

“wae ni nace maki ciki gareni ne,” bata jira

me inna xata ce ba ta shiga daki tayi

kwanciyarta, inna duk ta daga hankalinta

ganin irin laulayin da Inteesar take mai

tsanani, bbu wanda bae san ciki ne da ita

ba a gidan, ko da yaushe cikin amai da

kasala take, ko maganan kirki bata son yi

sae in Aliyu na yasa ta gaba ko yana

tambayarta me take so, duk tausayinta

kawae yake, Hajiya da hankalinta yyi mugun

tashi bata ga fuskar da xata ma Aliyu

magana ba da ya shigo da ya fice daga

gidan, tab aiko gwara ta nemo yanda xa ayi

da cikin nn, ynxu Aliyu dama sae ya iya

kwana daki daya da yarinyar nn duk cika

bakinsa, hka aka yi biki hankalin inna rabi

na gurin Inteesar rabi na gun bikin, duk aka

yi abubuwa masha Allah, amma inteesar na

kwance tana fama da kanta, safeena ma ta

xo ranar bikin tana daddaga hanci ita matar

Aliyu inna ta kunyatata gaban lodin jama’ar

biki su kursum dariya kmr xasu shide, ko

minti daya bata kara a gidan ba tayi gaba ba

shiri jikinta a sanyaye har ga Allah tsoran

tsohuwar nn take, ran Hajiya yyi mugun baci

amma bbu yanda ta iya da inna, washegarin

ranar da aka kai Amarya da daddare Aliyu ya

shigo falon inna bae ko kalli innar ba ya

durkusa gaban inteesar dake kwance

idonta biyu, ya daura hannu a goshinta yace

“amma yau bakiyi amai ba ko,” a fusace inna

tace “kaji gantalalle wani irin bata yi amai

ba, ae hanjin cikinta ne kadae bae xaxxago

ba yau har tsorata nayi nace to ko su ne ke

shirin fitowa” Aliyu yyi mata mugun kallo

yace “to ke kuma wa ya somo bakin ki nn,

iyayi kawae,” sae abun ya ba Inteesar dariya

ya dago ta yana kallonta yace “Abba na

neman mu, xaki iya ko na daukeki,” ta

marairaice tace ynxu, ya gyada mata kai, ita

mugun kunyan Abba take ji har ma da

momynta, duk shigowar da momy take ta

gaisheta kar inna ta xaxxageta tace taki

xuwa, Inteesar yi take kmr tana bacci, inna

ta mike tsaye da sauri tace “bari kawae na

kama hannunta mu je,” Aliyu ya bude baki

yana kallonta yace “wae meyasa kike son

shiga tsabgar da ba taki ba ne,” bae jira me

xata ce ba ya harareta ya sa ma Inteesar

hijab dinta ya dauketa suka fice, inna tayi

kmr xata yi kuka tace “ni ban san meyasa

yaron nn ya rainani da tsufa na da furfurata

ba,” a hanya ya ajiye ta dalilin rokansa da ta

dinga yi ya ajiyeta suka karaso falon yana

rike da hannunta, da kyar ta iya bude baki

ta gaishe da Abba kanta a kasa, ita kawae

kunyarsa take ji, yace “ya jikin fateema,”

kanta a kasa tace “da sauki Abba,” yace “to

Allah ya sauwake, kina son komawa dakin ki

ne ko xaki xauna nn gun inna sbda

condition dinki” ta dago kai a hankali tana

kallon Aliyu, shima kansa a kasa yake, tayi

shiru ta rasa me xata ce don ita kam bata da

burin cikin nn ya kara girma a jikinta, Aliyu

yace “Abba da dae na tafi da ita xan fi kula

da ita a can kuma ba gida ma nake barinta

ba tare da ita nake xuwa clinic, nn ko xae yi

min nisa kuma xan takura kaina,” Abba xae

yi magana inna ta fado falon, ashe tana labe

tana jin duk abinda suke cewa tana huci

kmr xata yi kuka tace “amma munafurcinka

dayawa yake Bukar, hka muka yi da kai? To

ni Rahmatu nace bbu inda yarinyar nn xata

je aje a kashe min ita da abinda ke cikinta a

banxa a hofi a barni da wayyo Allah, don

idan an kashe su ma ni nayi hasara ba ku

ba”.

.. Aliyu ya dan yi tsaki ya kauda kai, Abba

kam shiru yyi yana ta kallon inna, ita ko ta

tsaya masu kmr soja a bakin kofa, can dae

Abba yace “to ki hada kayanki sae ki bi su,”

tayi kwafa tace “ko da naji,” snn ta juya ta

fice da sauri, Abba ya girgixa kai yace “tashi

ka dau matarka ku tafi,” Aliyu ya mike yana

kallon Inteesar, ita ma ta mike tsaye suka

ma Abba sallama snn suka fita, yana rike da

hannunta yace “mu je mu gaida momyn

ihsaan ne,” tayi kmr bata ji sa ba shima bae

sake ce mata komai ba har suka fita ya bude

mata mota ta shiga shima ya xaga ya shiga

suka kama hanyar gida, ko da suka isa tayi

bacci ya fito da ita daga motar yana rike da

ita kmr bby, safeena na kwance falo ta bi su

da kallo ya sakar mata murmushi yace

“bbyna,” tayi tsaki ta dauke kanta tacigaba

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button