HAUSA NOVELINTEESAR 3

INTEESAR 3

da kallonta, sae da ya kai Inteesar sama ya

kwantar da ita snn ya sauko ya sameta, ta

mike tayitsaki ta haura sama ta bar sa nn ya

bita da kallo snn yyi mmrshi yabi bayanta.

Washegari sae da safeena ta sa ya makara

xuwa office, wanka kawae yyi ya shirya ya

dauki makullin motarsa ta rakasa tanai

masa shagwaba ya manna mata kiss ya ja

motarsa ya bar gidan, ta sauke ajiyar

xuciyan jin ddiyau dae ya manta shegiyar

gaba daya, ta koma cikin gida murna fal

cikinta, tana shiga daki ta fito da kullin

maganin da aka basu su sa ma Inteesar a

ruwan sha ta tsura ma maganin ido tana

murmushi,dukiya fa knn a hannunta, ruwan

fridge ta kwashe gaba daya ta bar guda

biyu ta xuxxuba maganin cikisnn ta rufe

fridge din ta koma sama, ta lura kasa

Inteesar ke saukowa shan ruwa bbu ruwa a

dakinta kuma bata ga alamar an siyo ba,

tana ta kwance a daki tana jiran jin

saukowar Inteesar amma shiru, ita ko tana

kwance daki ta rasa inda xata sa ranta sae

juye juye take ga yunwar da take ji tun safe

ta gane Aliyu ya bar gidan hkn yasa ta daure

ta mike ta sa ma kofar ta key, kishin ruwa

duk yabi ya ishetagashi ba karfin sauka

kasa, da kyar ta rarrafa ta shiga bathroom

ta bude tap ta sha ruwa ta dawo tayi

kwanciyarta kan tiles. Washegari ma abinda

ya faru knn Aliyu bae shigo ya ga halin da

take ciki ba ya bar gidan da sassafe, duk da

jiya don ita ya dawoda wuri amma safeena

ta gusar masa da hankalinsa ya manta me

ya dawo da shi, ganin yunwa na neman yi

mata lahani yasa ta dinga daurewa tana

hada tea a nn dakinta da ruwan sanyita sha,

shima tana sha ta amayo, duk ta kara

xabgewa bata da aiki sae na kuka ita daya a

daki, wani lkcn sae taji kmr ta dauki waya ta

kira inna kawae sae ta fasa don bata ga

amfanin kiran ba don rabuwa kawae take

son yi da cikin, ita safeena bbu abinda yafi

daga mata hankali irin yanda taga ruwanta

na nn ajiye ba a taba ba, hkn yasa da

daddare da Aliyu ya dawo ranan tace “anya

kuwa kana shiga duba baiwar Allahn nn

dear, gashi ita bafitowa take ba, na kan

shiga na dubata wllh, amma ba ddewa nake

ba kar ace xan yi mata wani abun ne” Aliyu

ya mike da sauri kmr an tsikaresa yyi hanyar

stairs ta bude fridge ta dauka ruwan da

sauri ta bi sa tana cewa “gashi ka kai mata

ruwa naga kmr jiya ruwan dakinta ya kare

na fanfo take sha, ni kuma kar na kai mata

ta xata wani abun ne,” ya karba ya haura

sama ya bude dakin ya shiga rabon da ya

ganta yau kwana uku tun ranar da

sukadawo daga gida, ya karaso gabanta ya

durkusa yana kallonta a hankali yace “ya

jikin fateema, kin daina aman,” tayi tsaki ta

juya abinta, ya bude fridge dinta ya ajiye

mata ruwan yace “me xaki ci,” tayi bnxa da

shi, yyi shiru yana kallonta, ta juya cikin kuka

tana kallonsa tace “wllh tllh idan baka cire

min wnn shegen cikin ba….” bae jira ya

karasa jin maganarta ba ya xuba mata mari,

“don uwarki kika sake min maganar cire

ciki sae nayi mugun saba maki kina ma da

hankali kuwa, to ki je ki cire tunda ke

mahaukaciya ce,” ya mike a fusace ya fice

daga dakin ta bisa da kallo dafe da kuncinta.

Ranar bata yi bacci da daddare ba, kawae

Allah Allah take gari ya waye, gari na

wayewa ya shigo dakin kafin ya tafi aiki, tea

me kauri ya hada mata ya ajiye matagefenta,

snn ya dauko goran ruwan da safeena ta

basa jiya ya ajiye mata gefenta safeena ta

shigo dakin tana murmushi tayi ma Inteesar

ya jiki ko kallonta inteesar bata yi ba suka

fice tare da mijintata rakasa ya shiga mota

ya manna mata kiss snn yaja motar ya bar

gidan, safeena ta koma gidan xuciyarta fari

tasa ganin goran ruwan da ta ba Aliyukusa

da inteesar yau dae xa ayi ta ta kare, ta

shige dakinta tana dariya. Inteesar ta mike

tsaye ta dauki Hijab dinta ta saka, duk irin

wahalan da take sha ko sau daya wanka

bae taba wuce ta da safe ba dole sae ta

daure ta shiga tayi, ta fito tana ganin jiri mai

gadi ya tsaya xae mata maganar bnxa ta

fixgo gate din ta fice abinta ta barsa nn

tsaye, gidan Aneesah ta shiga, tana xaune

tana ba shakur Indomie, tana shigowa ta

kwanta kan kujera tana mayar da numfashi,

Aneesah tace “lah daga ina hka Inteesar

daxun nn nagama xancenki a xuciyata wllh”

Inteesar xata yi magana taji yawu bakin ta

mike da kyar taje bathroom ta xubar

Aneesah tace “A’aah kice oga yyi aiki”

.

Inteesar ta harare Aneesah snn tayi tsaki

tace “ni don Allah taimako naxo kiyi min

Aneesah,” Aneesah tayi dariya tace “to

kawas ina jinki amma cikin nn na baki

wahala gskya, kinga yanda kika rame

kuwa,” Inteesar ta dawo kasa kusa da ita

tace “don Allah don Annabi Aneesah kinsan

inda ake abortion?” Aneesah tayo waje da

ido da mamaki tana kallonta snn tace “kina

da hankali kuwa inteesar,” inteesar ta

jinginar da kanta jikin kujera hawaye ya

cika idonta, Aneesah tace “kinyi shiru,”

inteesar ta share hawayen idonta tace “wllh

xubar da cikin nn xanyi kin dae ji na rantse

in ma xaki gaya min ki gaya min,” Aneesah

ta gyada kai tace “to tashi ki fita a gidana, ni

bana hulda da maras tsoran Allah,” inteesar

ta juya tana kallonta tayi shiru snn ta mike

tayi hanyar fita daga gidan, Aneesah ta bita

da sauri ta kamo hannunta tace “haba

inteesar bafa kiyi kama da jahila ba,” kuka

inteesar ta fashe da tace “baxa ki gane ba

Aneesah wllh bana sonsa bana son cikinsa,

bae damu dani ba sae wahala nke ta sha,”

Aneesah ta xaunar da ita tana kallonta da

tausayi tace “ni na tabbatar maki kina haife

wnn cikin xaki ga tsantsan so gun mijinki,

ni banga rashin son da mijinki yake maki ba

inteesar nafa ga abinda yyi ma kishiyarki

ranar sbda ke, don me xaki walakanta

kyautar da Allah ya baki yar uwa,” inteesar

tayi shiru tana ta sauraran Aneesah tana ta

wa’axinta da nasiha, har ta kai Aya snn

inteesar ta kirkiro murmushi tace “to ngdd

Aneesah, ta dauki shakur tana ta wasa da

shi yana mata dariya, tace “amma a gida

kika haife yaron nn ko Aneesah,” Aneesah

tace “me kika gani,” inteesar tayi yake tace

“aa kawae tambaya ce nayi don ni dae ina

tsoran Haihuwa,” Aneesah tayi dariya tace

“A’a a asibiti na haifesa,” inteesar tace “wani

asibitn?” Aneesah tace “A’a tender care na

haifesa, ai kin san asibitin bbu wani nisa,”

Inteesar tace “A’a” Aneesah ta gaya mata

inda asibitin yake kuma dama abnda kawae

take son ji knn, ta mike xuciyarta fal murna

ta bar gidan.

.

Inteesar na fita daga gidan Aneesah ta

koma gida cike da jin ddi ta shiga dakinta

tana haki kmr warce tayi gudu, ta tabe baki

jin wakan da ke tashi dakin safeena, sae da

ta huta na kusan minti goma snn ta mike ta

dauki purse dinta ta fita daga dakin, dakin

Aliyu ta bude a hankali ta shiga ta bude

drawer din da taji yace Safeena ta bude ta

dauki kudi ranan, taji ta a kulle, tace “na

shiga uku,” ta mike ta fara kalle kallen cikin

dakin kmr xata yi kuka, to ina xata samu

kudin xuwa asibitin ynxu, drawers din

dakin ta dinga bubbudewa gaba daya ko

xata ga kudi amma bbu, duk ta gaji sae haki

take, tuni ta fara kuka tana cewa “Allah ka

taimakeni in ga kudi” ta bude lst bedside

drawer din taga wani babban book an

rubuta my diary a gaba, tayi tsaki ta ajiye ta

mayar da drawern, ta mike ta isa wardrobe

din da yake ajiye kayansa na sawa ta bude

ta lumshe idonta sakamakon wani kamshi

me ddi da ya bugi hancinta, ta gama

bincikenta nn ma ba ta ga kudi ba ta rufe ta

xube kasa ta daura hannu a ka tace

“wayyoo Abbana wllh ni na gaji,” ko ina ta

bude daga taga Allura sae taga magunguna

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button