HAUSA NOVELINTEESAR 3

INTEESAR 3

da dae kayan asibiti kmr tsiya wnn wace

irin jaraba ce, kmr ance ta mike ta daga filo

taga dubu daddaya karkashin filon har da

Atm dinsa ta wara ido tace “wayyo Allahna,”

ta kwashi kudin ta shiga kirgasu da sauri

hannunta na rawa taga dubu sha biyu ne, ta

dan marairaice fuska to xae isheta taje

asibitin ma kuwa, tayi tsaki ta bude purse

dinta ta xuba kudin snn ta juya xata fita

daga dakin taje dakinta ta sha ruwa don

mugun kishi take ji don tsabar son taje ta

cire cikin ta nemi xaxxabin dake tattare da

ita ta rasa sae kasala kawae, har ta isa bakin

kofa ta dawo da sauri tuna baxae rasa ruwa

a dakinsa ba da tayi ta bude fridge dina ta

ko ga ruwa ta dauka ta bude ta sha snn ta

rufe fridge din ta dauki sauran ta fita daga

dakin, duk wnn abinda take safeena bata

sani ba, tana daki kwance tana ta shan kida

cike da jin ddi, jiran jin ihun Inteesar kawae

take a ko wani lkci, Inteesar kam har ta fita

daga gidan rike da purse dinta cikin Hijab,

mai gadi dae bae ce mata kala ba ta bude

gate ta fice abinta sae da ta isa bakin titi

snn ta tsayar da tricycle tayi masa

kwatancan asibitin da Aneesah ta gaya

mata yace ta bada dari biyu, ta shiga tace

mu je. Wasa wasa asibitin shegen nisa ne

da shi, yyi parkin dae dae gate din asibitin

ya juyo yana kallonta yace “mun kawo

Hajiya,” ta fito tana kare ma asibitin da ma

anguwar kallo, ta bude purse ta ciro dubu

daya cikin kudin ta basa kudin ya rage dubu

sha daya, ya bata canjinta ta karasa cikin

asibitin gabanta na faduwa, wnn dae da

ganin asibitin nn ba na talakawa bne, anya

kuwa xasuyi mata abortion a dubu sha daya

kuwa ta dan karyar da kanta abun tausayi,

da Addu’arta ta shiga asibitin, babba ne

ssae ta karasa cikin reception ta xauna

ganin patients dayawa a xaune, ta shiga

kare ma reception din kallo, ta kai kusan

minti talatin a xaune ba a xo kanta ba duk

ta gaji, taji kwanciya kawae take son yi ga

amai dake taso mata, ta daura kanta a cinya

taji kmr ta rusa ihu duk ta rasa ina xata sa

ranta, wata nurse ce ta dafa ta ta dago da

sauri tana kallonta, Nurse din tace “yhur

card nmbr Madam,” inteesar ta shiga kalle

kalle xata yi magana taji yawu ya cika

bakinta, nurse din ta lura da hka ta nuna

mata bayin dake kasan reception ta karasa

ta xubda yawun ta kora ruwa snn ta dawo,

nurse din ta debo vitamin c ta mika mata ta

sa a baki tayi mata gdya ta karba, tana

kallon Nurse din tace “i dnt have a card in

here,” Nurse din tace “to dole sae kin yanki

kati,” Inteesar tayi shiru snn tace “nawa ake

yankan katin,” nurse din tace “family card

dubu biyar, na mutum daya dubu 2 da dari

5,” inteesar tayo waje da ido tana kallonta,

ganin xata bata ma nurse din lkci ga kuma

patients dayawa suna jira yasa tace “to ki

yankar min na mutum daya,” nurse din tace

“ok” snn tayi gaba, a hankali inteesar tace

“na shiga uku, to ai kudin ya kare,” ba ajima

ba nurse din ta fito daga wani dan daki ta

mika mata katin snn wata nurse ta

daddubata ta duba har da weight dinta tayi

rubutu a file tasa nurse ta rakata bayi aka

xuba mata ruwa a kanta don temperature

dinta yyi sama, ita dae binsu kawae take, a

xuciyarta tace ko da yake basu san me ya

kawota ba shiyasa suke bata lkcnsu, ita dae

ynxu likita kawae take son gani, wata nurse

ce ta gwada mata office din doctor din da

xata shiga a sama, tana rike da file dinta ta

haura sama da kyar ta karasa office din tayi

knock.

A hankali Inteesar ta tura kofar bayan an

mata ixinin shigowa office din, cak ta tsaya

daga bakin kofa tana kallon likitar, doctor

din ma ta mike tsaye tana kallon Inteesar da

mamaki tace “fateema,” inteesar ta kirkiro

murmushi gabanta na faduwa ta karaso

office din a sanyaye, ta nuna mata kujera ta

xauna, doctor din tace “daga ina kike hka

fateema, me ya kawo ki nn,” ta rasa karyan

da xata mata, da kyar bakinta na rawa ta

ce”banda lfya ne,” doctor din ta hade rae

tace “shi Aliyun fa,” inteesar ta rasa me xata

ce ga xuciyarta sae tashi yake, likitan ta

dawo kusa da ita tana kallonta ta dago

kanta tana kallon cikin idonta tace “ciki gare

ki fateema,” inteesar tayi shiru bata ce

komai ba, doctor din ta ciro wayarta ranta a

bace ta shiga neman layin Aliyu, da sauri

inteesar ta dakatar da ita gabanta na

faduwa tace “A’a don Allah doctor kar ki

kirasa wllh ya sani kuma yana dubani nice

dai bana son shi ya duba ni, Allah yana kula

dani doctor kawae ni ce bana so, idan yaji

na xo nn xae bata min rae don bae sani ba,”

doctor din tace “haba fateema, to ma don

me xaki fita ba tare da ixinin mijinki ba,

kuma meyasa baki son ya duba ki,” inteesar

ta fashe da kuka tace “wllh ni bana sonsa

doctor,” doctor din ta tsaya da mamaki tana

kallonta snn tace “sbda me fateema, gashi

har rabo ya shigo kice baki son mijinki,”

Inteesar ta sunkuyar da kai tana hawaye,

doctor din tayi shiru tana kallonta, can ta

koma sit dinta ta xauna ta shiga yi mata

nasiha kan cewar ta rungumi mijinta ta cire

duk wani rashin sonsa a ranta, ita dae bata

ce komai ba sae kukan da take a hankali,

Doctor din tace “yyi maki scan ne?” inteesar

ta girgixa kanta tace “A’a nace masa bana

so,” doctor din ta harareta tace “to karki

sake yi ma mijinki musu baki san aljanarki

na karkashin kafarsa ba,” inteesar ta dan

tabe baki kanta a kasa ba tare da ta bari

doctor din ta lura ba, doctor din ta yagi

wani takarda ta danyi rubuce rubuce snn ta

danna bell wata nurse ta xo da sauri, ta

mika mata takardar tace “scan xa ayi yi mata

sisterna ce,” doctor din ta kalli Inteesar tace

“tashi ki bita,” inteesar ta mike a sanyaye ta

bi bayan nurse din har sun kai bakin kofa ta

juya tana kallon doctor Maryam tace “don

Allah doctor kar ki kirasa wlh xae bata min

rae,”doctorn tayi murmushi tace “baxan

kirasa ba ki kwantar da hankalinki” bayan

kusan awa daya inteesar da nurse din suka

shigo da sakamakon a hannun nurse din, ta

mika ma doctor maryam ta fita, doctorn ta

bude takardar tana dubawa, inteesar dae

kallonta kawae take ranta a hade, ba shiri

taga doctor maryam ta mike tsaye da sauri

tace “waw Ahmdllh, twins 4 Aliyu, Allahu

akbar,” ta rungume inteesar tace “Allah ya

raba lfya kanwata, kinga ma yan biyu ne”

inteesar ta sunkuyar da kanta da sauri

hawaye ya cika idonta, hka doctorn ta dinga

mata surutu cike da murna kmr ita xata

haifa ma cikin, ita dae bata ce mata komai

ba daga karshe ta hada mata magunguna,

da allurori a office dinta ta xuba mata su a

leda da takardar scan din tace “to maxa

tashi ki koma gida sae ki kai masa takardar

scan din, sae ya fada maki yanda xaki sha

magungunan yyi maki alluran,” Inteesar ta

mike da sauri kmr jira take tace “ngdd ssae

doctor,” har gate doctorn ta rakota snn tayi

mata sallama bayan ta kara jaddada mata ta

hakura ta xauna da mijinta, ita dae inteesar

sae gdya take mata har ta koma ciki snn ta

kama hanyar titi inda xata samu tricycle, a

cikin wani flower ta watsar da magungun

da injectns din dake cikin ledar dake

hannunta ta bar takardar scan din kawae, ta

isa titi xuciyarta na suya, ta tsayar da tricycle

tace “malam don Allah idan kasan ko wani

asibiti a nn wajajen ka kai ni,” yace “to

shigo muje akwae wani can gaba,” ta shiga

da sauri ya ja machine din suka kama

hanyar asibitin, ae ko yan goma ne a cikinta

ba yan biyu ba sae ta xubar da su yau wllh

.

Wani babban Asibitin aka kuma kawota, ta

fito tana kare ma asibitin kallo snn tace

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button