HAUSA NOVELINTEESAR 3

INTEESAR 3

magungunanta ta gani kan gadon kusa da

shi, ta yo waje da ido a tsorace da ganinta

kasan bata da gskya, ya tsaya kallonta yace

“me ya faru,” sanin cewa xae juya ya kalli

inda take kallo ne yasa ta tofar da yawun

bakinta nn bakin kofa da sauri ta fasa wani

raxanannen ihu tana tsalle, har ya juya ya

kalli ledan kan gadon kuwa ya mike da sauri

ya karasa kusa da ita a rude ya riketa yana

tambayarta lfya, jikinta ya dau rawa ta fashe

masa da kuka tace “wayyoo cikina ke min

ciwo har da kaina,” da mugun damuwa

yace “cikinki kuma” ta gyada masa kai

jikinta na ci gaba da rawa, ya daga ta xae

kwantar da ita kan gadonta ta fasa masa

ihu a gigice tace “wayyoo ni ka kai ni

dakinka, xafi nake ji,” duk ta rikitasa ya

dauketa da sauri ya bude dakin ya fita, sae

kuka kuwa take jikinta na rawa, safeena

dake fitowa daga dakinta knn ta bisuda

kallo xuciyarta na bugawa “kai wayyoo ddi,

ta sha ruwan,” ko kallonta Aliyu bae yi ba, ita

ko inteesar sae kuka take kmrgske, ya

kwantar da ita kan gado bayan ya kunna AC

yana kallonta yace “ina kika ce ke maki

ciwo,” a hankali tace “ya daina, wanka

kawae xanyi da ruwan xafi,” ya shiga

bayinsa da sauri ya hada mata ruwan, yana

shiga ta mike har tana tuntube ta fice daga

dakin da sauri suka kusan cikin karo da

safeena dake labe bakin kofa, safeena ta

koma baya a tsorace tayi xaton Aliyu ne,

inteesar ta watsa mata harara tace “an dae

ji kunya,” tayi tsaki ta bude kofar dakinta da

sauri ta kwashe magungunan kan gadon ta

xuba su cikin handbag dinta jikinta na

rawa, tana xuba su ta fice da sauri taga

safeena tsaye har lkcn kwakwalwarta a

jagule to ko bashi tasha bane, inteesar ta

wuce ta ta shige dakin Aliyu, dae dae nn ya

fito ya tsaya kallonta da mamaki, xae yi

magana ta rigasa “ruwa, amm ruwa naje

sha,” yana mata mugun kallo yace “get out,”

ta yi kmr xata yi kuka ya daka mata tsawa

“ni kike raina ma hankali ko, fitar min a daki

munafuka,” tayi tsaki ta juya ta fice daga

dakin tare da sauke ajiyar xuciya. Bata samu

shan maganin ba ranar da daddare har tayi

bacci don ido Aliyu ya sa mata, washegari

sunday yana gida yana xaune dakinsa

na’ura gabansa, safeena ko na daki kwance

abun duniya ya isheta, inteesar ta gama duk

abinda xata yi da kyar don xaxxabi ne ssae

tare da ita, ta rufe dakinta da makulli ta ciro

maganin da likitan ya bata jiya ta debo ruwa

a bathroom don har lkcn ba ruwa a dakinta,

ta xauna kusa da gado, ta fiffito da

magungunan daga kwalayensu ta daddauki

yanda yace mata, ta tsura ma kwayoyi

shiddan dake hannunta ido, ita bata ma

taba ganin irinsu ba, ta rumtse idonta ta

xuba su a bakinta ta kora da ruwa da sauri

ta hadiye su.

TAMMAT ALHAMDULILLAHI.

[ad_2]

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button