HAUSA NOVELINTEESAR 3

INTEESAR 3

maka ba wlh mugu kawae,” juyawa yyi ya

fice daga dakin da sauri ta mike jikinta na

rawa ta shige bathroom ta rufe da key.

Karfe sha biyu saura taji ana ring din Bell, ta

sauko gabanta na faduwa don tasan Aliyu

baya danna bell, ta karaso kusa da kofar

tana lekan ko waye, wani mutumi ta gani

tsaye, ta ki bude kofar tace “waye,” yace “ina

yini madam, Yusuf ne, oga Hydar ne ya

aikoni waexamu je registration da ke yau,

shi yana buzy,” tace “kaje kace masa ban

xuwa,” bata jira me xae ce ba ta koma sama

abunta, da daddare Aliyu ya dawo gidan

direct dakinta ya nufa ta hada tea knn xata

sha, duk da ba karamin tsorata tayi ba

amma ta dake bata nuna ba, kuma taki

dago kanta, ya karaso inda take ya fixgota

cikin tsawa yace “wani sako kika bada a

kawo min daxu,” ta shiga kikkifta ido a

tsorace tace “ni ka kyaleni wllh,” ya jefar da

ita ya fice daga dakin ta bi sa da harara, ko

minti biyar ba ayi ba ya dawo rike da belt, ta

fasa ihu a tsorace ta mike tsaye tace “na

shiga uku, wayyo Abbana,” ya fixgota ya

shaketa yana huci yace “na rantse da Allah

idan baki kama kanki a gidan nn kinsan da

wanda kike xaune ba sae na sumar dake

watarana” yana kai wa nn ya buga ta da

bango ya fice daga dakin, hka ta kwana

kuka da ciwon kai ranan, Da safe yana fita

ita ma ta shirya xata bar gidan amma mai

gadi yaki bude mata gate ta dinga rusa

masa kuka tana rokansa ya bude mata gate

amma yace “to ko yau sae da yallabae ya

kara jaddada min cewar kar na bari ki fita,”

ta fashe da kuka abun tausayi ta kasa cewa

komai, kmr daga sama taji Muryar inna da

karfi tana cewa “salama alekum, kin tabbata

nn ne gidan kursum”

.

Inteesar na jin muryar inna ta fasa kuka

tana kallon gate din, inna ta shiga bubbuga

gate din tana cewa “lah nn ne kursum ga

muryarta nn naji, a bude mana” Mai gadin

yace “waye wnn,” inna ta bude baki tace

“nashiga uku amar ya waye? Waye ke min

wnn tambayar,” Inteesar tace “malam ka

bude mata kakata ce fa,” mai gadi yace “ko

ma wacece yallabae yace kar na bude ma

kowa gate,” cikin daga murya inna tace “yau

naga jaraba waye wnn kuma” kursum tace

“mai gadi ne,” inna tace “mai gadi? To ya ci

ubansa ba a gaya masa ko ni wacece bane

ni da gidan jikokina xae hana ni shiga,”

kursum ta fashe da dariya inna tace “ke ban

san shashanci fa,” sae kuma ta shiga kiran

Inteesar,” cikin kuka inteesar tace “Na’am

inna yaki bude gate din,” a fusace inna tace

“yau ni naga jarababben dan iska gate din

ta ubanka ce ko ko, kaji min mutum,” dariya

ma abun yaba mai gadin inna tace “shi

Aliyun yana ina,” Inteesar tace “oho nima

ban sani ba,” inna ta shiga buga gatedin da

karfi tana duddura ma mai gadi xagi,shi dae

yana xaune sae shan rakensa yake inteesar

tace “wae kai wani irin mutum ne baka jin

ka bude mata gate ne ka maida mutane

mahaukata,” inna tace “ki rabu da shege,

kursum maxa kira min Bukar,” kursum ta

karbi wayar ta kira Abba ta mika mata tace

“Bukar Bukar gani gidan Aliyu wani kato

yahanani shiga, na kai awa biyu tsaye cikin

rana Bukar,” Abba yyi murmushi yace “to ae

umarnin da aka basa knn baaba ku koma

gida kawae,” cikin kuka inna tace “kambu,

Al’quran bbu inda xani sae ya bude min

gate don uwarsa,” nn ta shiga jijjiga gate

din kmr xata cire tana tsine ma mai gadi,

maigadi yyi tsaki ya ciro dan wayansa ya

kira Aliyu “oga ga wata tsohuwa nn ta xo ta

cika anguwa wae sae an bude mata gate,”

Aliyu yyi dariya yace “karka kuskura,” snn ya

katse kiran mai gadi ya mike yana fito ya

shige dakinsa. Inteesar taji kmr ta shakesa

ta karasa kusa da gate din tace “inna Aliyun

ne fa yace kar ya bude maku wlh, ku tafi

gida kawae ba budewa ae yi ba,” inna ta yo

waje da ido tace “me? To wllh bbu inda xani

ina nn har sae an bude min gate din,” cikin

kuka take maganar, kursum kuwa sae

dariya take har da faduwa,inna ta nemi

dakali ta xauna tana sharbe majina, tace “ae

yau bbu abinda xae hanani shiga gidan nn

wllh sae na shiga” Inteesar ta gaji da

tsayuwa ta shiga, ciki lkci lkci ta kan fito ta

tarar suna nn, sae tausayin innan ya cika ta

taji kmr ta dinga ihu don takaici lallai Aliyu

ya cika mara mutunci, duk irin yanda ta

lallaba inna ta tafi kin wucewa inna tayi, har

aka kira azahar inna na nn xaune kursum ta

gaji ta kama hanyar gida inna ta rakata da

xagi, shegiya kawae ni ba mutum bace

kuma ban san ciwon jikina ba sae ke ko,

ganin har kusan karfe hudu inna na nn a

xaune yasa inteesar ta fito da ruwa tana

kallon mai gadi tace “don Allah don annabi

malam ka dan bude gate din sae ka mika

mata ruwan nn wllh tsohuwace,” da kamr

baxae tashi ba sae kuma ya mike ya karbi

ruwan da take mika masa ya dan bude gate

din yana lekota yace “ga ruwa kaka,” ta

mike tsaye tana kallonsa da shirin masifa ko

me ta tuna sae kuma tafasa, ta karaso kusa

da gate din kmr xata karbi ruwan ta

bangajesa da karfi ta shige gidan da gudu.

Me inteesar xata yi idan ba dariya ba, ta

durkushe kasa ta dinga dariya kmr cikinta

xae kulle, mai gadin ya bude baki yana

kallon inna dake huci tace “don buhun

ubanka ni xaka hana shiga gidan jikokina,

mugu katon bnxa kawae, wllh baka sameni

lkcn ina Rahmatu ba da yau bbu ubanda xae

hanani faffala maka mari dan iska,”

Inna na kai wa Aya ta yi hanyar garden kmr

xata tashi sama tana huci Inteesar ta bi ta

da sauri tana ci gaba da dariya tace “ba nn

bane hanyar shiga inna,” Mai gadin ya sauke

ajiyar xuciya yana bin inna da kallo, bae taba

ganin tsohuwa da karfi hka ba, har suka

shiga falo Inteesar bata daina dariyar da

take ba inna ta hade rae tace “ke ni fa ban

san tsiya meye abun dariya a nn, wlkncin da

katon can yyi min ko me” kan Inteesar tace

komai inna ta rike haba baki bude

tace”A’aah bene kuma cikin gida ni

Rahmatu naga abinda ya ishe ni,” Inteesar

tace “kuma shi xaki hau muje daki ba,” inna

tace “ni ina xan iya,” inteesar na dariya ta ja

ta suka haura sama tana mitan kafafunta na

ciwo, sae da inna ta fara sllh snn Inteesar ta

kawo mata abincin da ta dafa kmr dae

tasan inna xata shigo gidan daga karshe,

inna aka xauna aka bubbude kafa tana ci

tana xagin mai gadi da Aliyu, sae da inna ta

gama cika cikinta snn Inteesar ta xaga da

ita ko ina na gidan har dakin Aliyu sae da

suka shiga, inna sae washe hakora take

tace “ashe dae xan ga wnn rana da xan

taho gidan jikokina ni rahmatu, ae Bukar

bae yi ba, ni ban san meyasa yake min hka

ba gidan jikokina ma ya hanani xuwa sae

da ixininsa sae kace ubana, daba dan hka

ba ae sae na dawo nn ma gaba daya gani

ga ku, ni dae ynxu ‘ya yana nake son gani

duk da bamu san gawan fari ba, xan so

naga yayanku da Aliyu,” Inteesar dae bata ce

komai ba a xuciyarta tace Allah shi kyauta

na Haihu da Aliyu, inna ta juya tana kare

mata kallo tace “wae ni ya naji shiru ne har

ynxu Inteesar ga fadila can da ciki, anya

kuwa bakwa shan abu yaran nn, barin ke,

nafi tausaya maki don shegen yaron nn kai

ki xae yi ya baro ki” Inteesar ta hade rae tayi

gaba ta barta nn tsaye, inna ta bita a baya

tana cewa “to ni dae banga abun bata rae

ba a nn daga fadan gskya” suna komawa

daki inna ta xauna ta hade rae tana kallon

Inteesar tace “ki maxa ki hada kayanki tafiya

na xo yi dake dama, wae ashe gantalallen

yaron nn aure xae yi ban sani ba,” sae kuma

ta fashe da kuka tace “sakayyar da xae

mana kenn, wllh sae ya baki takardar ki ba

rasa masoya kika yi ba,” Inteesar tayi shiru

da mamaki tana kallon inna kmr ba ita ba

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button