HAUSA NOVELINTEESAR 3

INTEESAR 3

na kuka Inteesar” Anty Nafeesah tace maxa

tashi kije ki gyara fuskarki kiyi kwalliya kar

na bata maki rae ke dae baki gajiya da wnn

shegen kukan naki komai kuka komai kuka,

ita dai bata ce komai ba suka bar dakin

Aliyu Zainab ta kulle suka koma nata dakin,

sae da ta sake wanka snn Anty Nafeesa ta

sa ta gaba ta tsantsara kwalliyanta snn ta

fito mata da wata shaddarta dogon riga

maroon colour ta saka Nafeesa tayi mata

dauri mai kyau, Zainab tace”waw yan matan

yayanmu kin ga yanda kika xama kmr wata

balarabiya,” inteesar ta galla mata hara, ba

karamin kyau tayi ba duk da ta rame ssae,

Anty Nafeesa tace “to akwae abinci ne a

gidan? Don ni yunwa nake ji,” Inteesar tace

“sae da na girka maku,” Anty Nafeesah tace

“to da dae yafi,” ta ce “toAnty suna falo

kuma,” Anty nafeesa tace “to ina ruwanki da

su ae don su ganki da kyau nake son kije

kiyi mana girkin,” ta mike ta dauko mata

takalmikalan shaddar ta ajiye mata snn ta

feshe ta da turare tace “maxa sa ki tafi

indomie kawae xaki girka mana,” Zainab

tayi dariya tana kallon Anty Nafeesa,

Inteesar kam murmushi tayi ta sa takalmin

gabanta na faduwa ta fita xuwa kitchen,

duk suna xaune falon har da safeena kusan

su goma banda wa inda ke ta jere a daki,

Inteesar bata ko kalle inda suke ba a nutse

cikin takunta mai jan hankali ta nufi kitchen

ta bude kofar kitchen din tana yatsine fuska

don duk sun dauki cups sun sha lemo da

shi, ta dan tabe baki ta shiga kitchen din,

duk kawayen safeena suka juya suna kallon

safeena da yanayinta ya sauya lkci daya

xuwa bacin rai tana kallon kofar kitchen din,

inteesar ta kunna gas ta daura ruwa snn ta

fito falon ta shiga kwala ma Zainab kira

cikin wani irin tsiga, da sauri Zainab ta

sauko tana cewa “na’am yan matan

yayanmu wnn kira hka,” inteesar ta galla

mata harara da wasa tace “ban fa son

iskanci indomie nawa kike ga xae isheku,”

Zainab tace ” wani irin tonan asiri ne wnn,

ko ma dae duka nace ae gidan yayana ne nn

bbu uban da ya isa ya hana,” Inteesar tayi

dariya ssae tace “ikon Allah to shigo ki girka

maku kinsan dae ni ba daga nn ba ban gaji

rowa ba kuma duk yanda nace hka xa ayi a

gidan nn bare kice kina tsoran wataran ki

xo…,” a fusace safeena ta mike tana nuna

Inteesar da yatsa tace “ke ki kama kanki kar

ki kaini bango don dukan tsiya xan maki

wllh wllh kuma sae dae mijikinki ya gode

min idan ya dawo,” Zainab ta yo waje da ido

tace “wa xa a duka ni Zainb” Inteesar tayi

dariya tace”tambayan min ita don ni kaina

ban gane inda ta dosa ba,” Safeena ta ciro

wayarta da sauri ta shiga kiran Aliyu, “Aliyu

Aliyu ka ja ma ballagaxar da ka ajiye a gida

kunni wllh ta fita harkata idan ba hka

bakafin na bar gidan nn yau sae na yi mata

kaca kaca, kuma wnn shegiyar kanwartaka

ita ma kaja mata kunne,” Zainab tace “wllh

ni ba shegiya bace sae dae kece shegiya,”

Inteesar ta ja ta suka shiga kitchen suna

dariya, safeena tayi shiru tana sauraran

abinda Aliyu ke ce mata tana bubbuga kafa,

sun gama dafa indomien knn xasu wuce

samaAliyu ya shigo gidan, ba karamin

tsorata inteesar tayi ba tayi hanyar stairs ba

tare da ta kallesa ba, Zainab tace “ke kar ki

bada kanki mana ki tsaya ae Anty nafeesa

na nn,” Aliyu na kallonta yace “ke xo nn,” ta

galla masa harara tace “nayi maka me,”

karasowa kusa da ita yyi ta dake xuciyarta

na bugawa, duk yan falon suka xuba masu

na mujiya, ita kanta Zainab karfin hali tayi ta

tsaya, Safeena kosae taunar cingam take

tana jujjuya ido xuciyarta fal murna ita nn

kawayenta suka yanda ta isa da Aliyu, yana

isa kusa da inteesar ya kama hannunta ta

fixge tace “da’alla malam kyaleni,” ya tsaya

kallonta da mamaki bae ce komai ba,ya juya

yana kallon Zainab yace “je dauko mata

mayafinta ko ki bata naki,” Zanab ta cire

mayafinta ta mika ma Inteesar taki karba,

shi ya karba snn ya sureta kmr wata bby

suka fita daga gida

.

Inteesar ta tsorata ssae murya can kasa tace

“don Allah kayi hakuri ka saukeni wllh ita ce

ta fara,”Safeena kam binsu tayi da kallo da

mugun mamaki don tsabar mamaki kasa

rufe bakinta dake bude tayi, ita nn jira take

taga ya rufe ta da duka, Zainab kuwa dariya

tayi tace “kai irin wnn soyayya hka, ko me

Inteesar ke ma yayana hka oho,” ta haura

sama tana ci gaba da dariya, bayan mota ya

jefata snn ya xaga ya shiga motar ya ja ta,

ita ko kallonsa kawae take gabanta na

faduwa ko ina xae kai ta, sun yitafiya ssae

snn taga yyi horn aka bude gate ya shiga yyi

parkin, ya bude mata kofa yace “fito kar na

mareki,” ta fito tana kare ma wajen kalloduk

da tasan inda ya kawota don ta taba xuwa,

lallai ma Aliyu asibiti ya kawota, yyi gaba

tana biye da shi a baya kmr xata yi kuka,

nurses duksuka kama kansu ganinsa, suka

bi inteesar da kallo suna masu sannu da

xuwa, bae ko kallesuba sae ita ce ta

gaishesu ganin yanda suke kallonta, can last

flour office dinsa yake kusa dana aminin

dad dinsa don shine mai asibitin wato

 

dad din Sadeeq, ya bude office dinsa ya

shiga, ganin taki shigowa yasa ya fixgota, ta

shiga karema office din nasa kallo, ba

karamin haduwa yyi ba kmr ba office ba ita

fa bata taba gskata Aliyuna aiki ba duk da

tasan da sassafe yake barin gida ya dawo

late, ya shiga dakin da ke cikin office din ita

dae tana nn tsaye har ya fito bayan kmr

minti goma sanye da kayan surgery, green

colour yana kkrin sa hand gloves alamar

theatre xae shiga, ya galla mata harara yace

“kada Allah yasa ki xauna kuma idan lkcn

sllh yyi kar kiyi,” snn ya fice, tayi tsaki kmr

xata yi kuka ta xauna kan kujera tana kare

ma office din kallo, ko minti goma ba ayi ba

da fitarsa wata nurse ta shigo rike da abinci

a rufe da lemo ta ajiye mata tace “sannu

madam,” snn ta fita. Hka inteesar ta yi ta

xama kamar gantalalliya a office kmr tayi

kuka, abincin da aka kawo mata ma kin ci

tayi, ta gaji da xama ta kwanta kan gadon

da ake duba pregnant women tayi

kwanciyarta sae bacci, ko da ta farka taga

biyar ya kusa ita da ta kwanta tun kusan

daya da rabi, bata damu ba don dama bata

sllh, ta bude abinci daxu ta yatsine fuska ta

rufe, aka bude kofa wasu nurse biyu suka

shigo da jarirae har biyu suka yi ma inteesar

sannu, snn suka daura su kan gadon yara

dake office din daya ta kunna wani wuta

mai haske dae dae fuskarsu snn suka fita,

inteesar ta wara ido tana kallon yaran

kyawawa dasu, ta karasa kusa dasu da

mamaki tana kallonsu tace “yan biyu,” a

hankali dayan ya shiga kuka yana tsotsan

hannunsa dayan ma ya karbe taji kmr ta

daukesu don tana bala’in son yara, ta rasa

yanda xata yi dukta rude ganinsu tayi can

tayi nn, aka bude kofar dakin Aliyu ya shigo

ta juya da sauri tace “ya Aliyu yan biyu ne?”

ya cire abun bakinsa yace “ehh” ba tare da

tasani ba tace “waw a ina kukasamo su” ya

karaso kusa da gadon yana kallonsu yace

“daxun aka cirosu daga cikin mamansu,

bata farfado ba har ynxu ma” inteesar ta

juya da sauri tana kallonsa kmr xata yi kuka

tace “theatre aka mata,” xae yi magana daya

yaron ya tsala ihu tace “wayyo ya Aliyu in

daukeshi,” ya harareta yace “basu da

lafiyasuma,” tayi shiru tana kallonsu kmr

xata yi kuka.Ya dauki dayan a hankali ya

mika mata yana kallonta.

.

A hankali Inteesar ta sa hannu ta karbi bbyn

da yake mika mata tana murmushi, tace “ya

Aliyu ni ina son twins ssae” yana kallonta

yace “kina sonki haifi twins knn,” da sauri

tana kallonsa tace “eh mana ina so,” ganin

irin kallon da yake mata yana murmushi

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button