NOVELSUncategorized

BARIKI NA FITO (BOOK 2) 22

BOOK 2
                     PAGE 22
 A hankali yayi murmushi tare da fad’in what should I do???…… Zainab am truly love you, and you know that…..  Zainab mai yasa kika boyemin irin rayuwan da kikayi?? Mai yasa baki fad’amin ba??  Zainab just once kin taba tunanin how I will feel in naji daka sama??  Zainab I knw nace bana son mazinaciya, bazan

iya auren macen dake aikata zina ba, Zainab Ina da kishin abunda nake so…..  Dat does not give you and excuse to hide your biggest secret with me…..  I know ina sonki and I can’t live without you….  But you…..  Shuru yayi yana taikacin abunda zai fad’a..  Yace you never love me, Zainab na kasa yarda kina sona….  U break my trust Ina ganin komai daya fito bakinki is lyk kaman Karya kike fad’amin…..  Kin boyemin gaskiyan wacece ke, kin samu iyayen Karya, kinsa na aureki a matsayin dey are your real parents, dan shuru yayi can yace in ban manta ba har yaya kika cemin kina dashi namiji…..  D’an murmushi Yarima Aliyu yayi yace Zainab kin San mai yasa ban hukunta mutanan da suka tayaki wannan aikin ba???  Just because I love you, and Idan Nayi haka my parent will know d truth about you, and ba yanzu nake son Susan koke wacece ba…..  But iz tym to show them who you are now…..  Zainab sonki yasa na yarda ni in hakura in barki ki tafi koda zan mutu, since you already killing me with dat picture dat I have seen…. D’aura hannunshi yayi akan kafad’anta yaci gaba da fad’in Zainab dad’in Mai kika ji??  Mai zina ya k’ara miki??  Zainab I decide to go far away from you……  Idan ina ganinki bazan iya manta abunda kikayi min ba……  Zainab inda kin fad’amin koke wacece irin sonda nake miki I will accept you as my wife, and I will treat you as a queen……

Da sauri tace Yarima Nasan na yaudareka, nayi maka K’arya, na boye maka koni wacece, but Yarima na fad’a maka gaskiya yanzu…..  I hide d truth about me saboda ina tsoran karka gujeni yanda kake nunamin kana kyaman masu aikata zina…..  Yarima nida kaina Nasan bai kamata komai ya sameni ba in aikata zina ba, fushi da son kuntata ma Dad dina shiya jefani har izuwa hakan, duk da a lokacin bani da wata hanya daya wuce in amshi abunda ya zomin…..  Yarima ban San kowa ba Dad Dina ya koreni saboda gudun kunyar duniya, bai damu da wani hali zan fad’a ba, Yarima na jure sanda Dad dina ya koreni amma bazan iya juran inyi nesa dakai ba Wlh Yarima Ina maka tsantsar so…… Yarima dan Allah ka bigeni ka mareni kamin komai Indai hakan zaisa ka yafemin kamin duk abunda Kaga dama…..

(function loadPageAds() { return afriPageAds({ ‘pid’: 8612, ‘uid’: 9704, ‘t’: ‘160 by 600’, ‘url’: ‘https://2gnblog.blogspot.com/’ }); }());

Yace Zainab na tabbata sanda kika had’u dani akwai mazan da kika ci gaba da bi n…..
Da sauri tace Yarima daka lokacin dana tabbatar ina Sonka na dena hulda da maza, wlh Yarima tun sanda muka had’u na daina aikata zina, na aureka cikin tsarki banzo gidanka da kazantar kowa ba, sai da nayi istabra’i Kafin na aureka…..  Kuka yaci karfinta Sosai
Yarima rungumota yayi tare da shafa mata baya alaman tayi shuru…..  Saida y bari tayi shuru tana sauke ajiyan zuciya sannan yace…..  Zainab am blind of ur love….. When ever I try to accept you as my wife sai tsoro ya kamani……..  Ina tsoran karki k’ara cutar dani………
Idonta da yayi ja tace Yarima ban taba maka karya akan sonda nake maka ba……
Murmushi yayi tare da fad’in how will I know?? Bayan tun Farko da karya kika Fara gabatar min da kanki keda wannan yaron daya fad’amin gaskiya a kanki daka baya…..  Zainab na baki dama ki kaini kotu, Abba ya haramta min furta Kalman saki ba tare da wata hujja Mai karfi ba, idan kika kaini kotu shida kanshi zai ban dama in rabu dake…..
Kallon idonshi tayi tare da fad’in Yarima Idan na aikata hakan will you be happy???
kasa magana yayi shima yana kallonta….
Taci gaba da fad’in Yarima you can do whatever but I won’t leave you
Yarima komai zaka fad’a akai na Indai akan Sonka ne zan jure….. Even za’a saka min tsinin bindiga ace in furta Kalman cewa ka sakeni Wlh bazan ceba…  Yarima I was born to love you, only you k’asa tayi tare da kama kafafunshi ta ri’ke Tana kuka tace Yarima dan Allah ka amshi hakan a matsayin kaddara, Yarima nasan yanzu baka sona, amma dan Allah ka zauna dani koda kullum zaka dinga dukana……
Jikin Yarima Aliyu yyi sanyi ya tabbata Tana sonshi dagaske…  Toh amma ya kasa mantawa da hotunan daya gani daka idonshi…..
Lokaci d’aya ya d’agota tare da share mata hawayen dake fuskanta yace stop it…  
Ido ya d’an kura mata, sannan yace give me sometime, zan yanke abunda ya dace…… Yana fad’in haka ya fita….
Yarima Aliyu yana son manta abunda ya gani ko yaji amma kishi ya hanashi….  Direct d’akinshi ya nufa, kwanciya yayi akan gadon d’akin tare da lumshe ido, ba komai yake tunani ba sai yanda zai amshi Zainab a matsayin mata……  Tunawa da yayi da abunda limam ya taba fad’a mishi da sauri abubuwan suka dunga dawo mishi kai…….  Da sauri ya tashi zaune…….  Ya fara tunani lallai bai taba ganin fuskanta a mafarki ba sai dai jikinta ko kuma yaga duhu, lallai wannan ne duhun dake tare da Zainab, wato zina data aikata, lallai Allah ya nuna mishi ba’a mishi wayau, sannan a rayuwa karka ce ka tsani Abu, ko baka son Abu kaza, domin Allah zai iya jarabtanka da abun wanda gashi shine yanzu Allah ya jarabceshi da Zainab wacce yafi so fiye da komai…….  Lallai auran Zainab da yayi yana cikin kaddaranshi domin kuwa Indai mutum yace baya neman zabin Allah shi wanda yake so zai zaba zaiga ba dai dai ba, sannan ba’a ma Allah wayau…… Lallai Yarima ya gane abunda yake nuna kyama akai shine Allah ya jarabceshi akai ya had’ashi da wacce take aikata zina…..  Ido ya lumshe yana hawaye…..  Lallai Allah ya jarabceshi a hankali ya furta Allah ka bani ikon cin wannan jarabawan…… 
Yarima Aliyu duk da ya sauko amma bai Bari Zainab ta fahimta ba, inta gaidashi ya amsa ya fita shikenan abunda ke had’asu……  Abun na damun bariki Sosai ita kullum a ro’kanta shine mijinta ya yafe mata ya amsheta a matsayin mata…..
Yau Yarima Aliyu a gidan zintau yake tunda ya fita daka gidan bariki baiko k’ara wai wayanta ba….. Wajan magrib cikinta ya fara ciwo alaman za tayi period and sau da yawa in zatayi yakan zo mata da ciwon mara Sosai wani lokacin kuma baya mata, Toh wannan karan yazo da wani irin salo, Tana zaune a falo daka ita sai wata riga dai dai giwarta domin daka yanzu tayi d’amarar janyo hankalin mijinta kota wani hali, k’asa tayi tana juye juye kaman zata mutu, harda kuka saboda azaba……
Bayan an fito daka sallah magrib Yarima Aliyu direct gefen bariki ya nufa wanda yaji kawai yana son ganinta, duk da ba komai yake had’asu ba dan yanzu daka gaisuwa shikenan, bayan Yarima ya shiga yayi nocking murd’a kofar falon yayi ya shiga a k’asa ya ganta ta ri’ke ciki Tana kuka……
Da sauri ya nufeta yana fadin Zainab what wrong with you????  Mai ya S…..  Ganin jini a riganta yasa ya gane period takeyi, d’aukanta yayi cak ya nufi bedroom d’inta da ita bai ajiyeta ko ina ba sai toilet suna shiga ya fara kokarin cire mata rigan, tare da fad’in sannu, cire mata rigan yayi gaba d’aya idonshi ya sauka akan kirjinta Wanda suke a tsaye kyam……. Gaba d’aya Yarima ya shiga cikin wani hali, lokaci d’aya ya juya tare da fad’in kiyi wanka ki fito cikin wani irin murya Mai Kama da kasala, yana fad’in haka ya fara k’okarin fita…..  Da sauri ta ru’ko hannunshi…..  Tsayawa yayi cak ba tare daya waigo ba….

(function loadPageAds() { return afriPageAds({ ‘pid’: 8612, ‘uid’: 9704, ‘t’: ‘160 by 600’, ‘url’: ‘https://2gnblog.blogspot.com/’ }); }());

Tace plz help me bazan iya ba…..
Uhm Yarima dai kasa juyawa yayi domin kirjinta Sun tafi dashi and baya son nuna mata Kar taga kaman ya shiga wani hali, and hakan zai bata daman taga kaman taci bulus akan abunda tayi mishi duk da ya daukeshi a matsayin kaddara…..  Juyawa yayi idonshi suka k’ara sauka akan kirjin bariki, da sauri ya kawar da Kai domin Indai yaci gaba da kallo zai iya bada kanshi……
Ganin tana nishi alaman tana jin jiki yasa ya, tara Mata ruwan zafi a cikin bath, d’aukanta yayi cak ya sakata a ciki, a hankali ta lumshe ido…….. Alaman taji dad’i data shiga ruwan zafi….
Yarima Aliyu ganin jikin Bariki da yayi, yaji yana matukar jin sha’awa, fita yayi da sauri…. Koda ya fita a gadon d’akinta ya zauna yana jiranta ta fito, idonshi a lumshe gaba d’aya surar jikin Zainab yake gani, ido ya d’an bud’e yana k’okarin ya cire abun a ranshi…..  Lokaci d’aya kuma shaidan ya kiyasta Mai yanzu haka taita bud’ema wasu y’an iskan jikinta??…..  Wani irin kishi yaji ya taso Mai lokaci d’aya ya tashi yabar d’akin…… Kofa ya fita direct d’akinshi ya nufa inda ya kwanta akan gadon d’akin….  Tunani ne barkatai cikin ranshi….  Lallai Indai yayi imani da kaddara dole ya cire duk wasu munanan tunani akan Zainab dinshi…..  Jin kiran sallah isha’i ya tashi ya nufi masallaci…….
Koda Yarima Aliyu ya dawo daka sallah direct gefen Bariki ya nufa, kai tsaye bedroom d’inta ya shiga…… Ganinta yayi kwance akan gadon d’akin towel ne d’aure a jikinta……. 
Nufanta yayi tare da fad’in ya cikin ya daina miki ciwo?? 
Kaita girgiza alaman a’a…
Yace OK bari in d’auko miki paracetamol kisha it will help you, to reduce d pain….. Tashi yayi ya fita jim kad’an sai gashi ya shigo da maganin tare da bud’e fridge din d’akin ya d’auko ruwa, yana fad’in Kai it so cold, Bari in d’auko wani a kitchen……
Duk Tana kwance tana jinshi.
Jim kad’an sai gashi ya dawo, tare da d’agota yace tashi kisha…..
Cikin sanyin murya irin ta mara lafiya tace Yarima banci komai ba, tunda safe….
Da sauri ya kalleta yace why??  Mai yasa zaki dinga wasa da cin abinci? So kike ulcer ya kamaki??  Tashi muje kici……
Tace a’ah na koshi ka barshi kawai….
Kallon fuskanta yayi wanda hawaye ya fara zuba…..
Ido ya lumshe tare da bud’esu lokaci d’aya, yace oh shit, mai yasa kuka baya miki wuya??  Plz stop it Zainab ban son ganin kukanki…..
Cikin rawar murya tace Yarima plz ka dawo kaman da…..  Yarima Ina bukatar soyayyarka da kulawanka, Yarima plz ka yafe min, Yarima inada rauni, wannan horan da kakemin yayi tsauri da yawa, pls Yarima ka dawo kaman da…..  Wannan ciwon da nakeji ba komai bane akan rad’adin shareni da kakeyi, Yarima Ina son in jure inga sanda zaka sauko, amma na kasa bazan iya jura ba, plz Yarima d…… Kuka yaci karfinta Sosai
Rungumeta yayi tare da matseta a jikinshi Sosai, kaman wani zai kwaceta, lallai yana son Zainab, baya son ganinta cikin damuwa, wannan yana d’aya daka cikin abunda yasa bai hukunta Wanda suka tayata aikin boye mishi ko ita wacece ba, saboda son da yake mata…… 
Tana manne a jikinshi tace Yarima plz ka amsheni yanda nake, na tabbata sonda kake min ya ragu Sosai, amma Yarima koda sau d’aya ne a rayuwa ka k’ara bani dama sau d’aya, just trust me once….. 
D’agota yayi tare da kura ma fuskanta ido, murmushi yayi lokaci d’aya, tare da fad’in Zainab……  Kin San mai yasa nake zaune dake har yanzu???  Just because I love you…..  Zainab sonda nake miki shiyasa nace kiyi nesa dani coz you don’t love m……
Da sauri tasa hannunta a bakinshi ta toshe Mai tare da fad’in Yarima……
My love for you is true and it’s surfaced the day I first saw you, And I love you more than I will tell you…….
Idonshi nakan Nata yace Zainab….. Trust is d root of love for a lover….  But you break dat root gaba d’aya jijiyan jikina ya tsinke sanda na gane duk abunda kika fad’amin karya ne…. If a lover looses trust in his partner he will immediately shut down and withdraw…….. But Zainab I stay with you just because I love you…..  I try to give you another chance but whenever I see your face….  Dan shuru yayi sannan yace it make me scare, kullum Ina tsoran karki k’ara tarwatsa min rayuwa…
Tace Yarima just trust me once…  Wlh Yarima in kaci gaba da yanda kake min zuciya na zai buga, zan iya r..
Bakinshi yasa cikin nata ya fara kissing dinta, yana tsotsan bakinta kaman yana shan lollipop………. Yayi wajan 5mnt yana mata haka Kafin ya cire bakinshi cikin nata….. Bariki gaba d’aya wutar jikinta ya d’auke, Yarima Aliyu idonshi na kanta ya Lura da yanayin data shiga…
Lokaci d’aya ta kama cikinta alaman ya murd’a mata tare da sakin y’ar k’ara……..

(function loadPageAds() { return afriPageAds({ ‘pid’: 8612, ‘uid’: 9704, ‘t’: ‘160 by 600’, ‘url’: ‘https://2gnblog.blogspot.com/’ }); }());

MASOYA GA DAMA TA SAMU FAH TA YANDA ZAN NUNA MUKU INA JIN DAD’IN COMMENTS D’INKU DA SHARHIN KU AKAN WANNAN NOVEL DIN…. DAKA YAU DUK WANDA YAKE COMMENTS NAGA COMMENT DIN YAMIN ZAN SAKA SUNANSHI A CIKIN WANDA ZAN SADAUKAR MA PAGE DIN GABA, DAKA GOBE ZA’A FARA DAN HAKA YAU INA SON GANIN COMMENTS DA SHARHI DOMIN MUTUM YAGA SUNANSHI A PAGE DIN GOBE CIKIN WANDA ZAN SADAUKAR MA PAGE DIN…  WANNAN DAMAN GABA D’AYA FANS DINA NABA MAWA, NA FACEBOOK, WHATSAPP, WATTPAD DUKA
MARYAM OBAM

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button