
Ayi min hakuri Fans wannan Novel din bana bada page da wuri wasu Abubuwa ne suka rikeni in busy ne sosai,Dan Allah kuyi min hakuri da afwa da kyar nake samun time na typing.
AsmaBaffa
[7/22, 1:14 PM] Sis Asma: ????????????
JIN DADI SABO
71-75
Official
By
AsmaBaffa
Ahleef Yan London sun kwashe 2wks a garin suna zuba amarci kafin suka tafi Russia sun kwashe 1wk sannan suka wuce Saudi nan suka Iske Baba da Umma Sunyi Ibada sosai,sai kyau da haske da suka Kara tare da Yar kiba kowa ya gansu yasan suna Jin dadi,Shukura tana ta siyayya Ahleef Yana kashe Mata kudi sai abinda take so, Bayan sun Gama aikin hajji Su Umma suka dage zuwa Nigeria,Ahleef kuwa Shukura ya dauka suka wuce Dubai abinsu, Baba da Umma suna hutawa suka tafi Niger a jirgi wurin dangin Baba sada zumunci,can ma Sunyi Mamakin ganin Baba,domin tunaninsu baya Raye sai gashi ya kawo Musu ziyara tare da kyautuka na alheri, sunji dadi sannan Ya Basu labari dansa Ahleef, satinsu biyu sannan suka dawo Abuja cike da murnar ganin Yan Uwa.
Bayan 3weaks Su Shukura jirginsu ya sauka a Nigeria,Murna take faman yi zata ga su Umma, escort din Ahleef ne suka dauko su daga Airport zuwa gida, Umma da Baba ma murna suke sosai da dawowar yaran nasu,Shukura jikin Umma ta lafe sun Dade suna Hira har Ahleef tare da cin abincin Umma me Dan Karan dadi sannan suka wuce hadadden part dinsu cike da kaunar juna.
Niima ciki ya Kara girma sai fama take da laulayi, Momee kullum sai ta zubar da hawaye musamman yanzu da suke cikin talauci kudi ya Kare karaf,abincin da suka siya ma sun cinye Babu sai kadan,kudin cefane Babu shi kullum shinkafa fara da Mai suke ci abinda ya rage musu kenan, tuni suka daina girki da Gas sai itace ko coal,kamar kullum yau sun tashi sisi babu ko na Koko Basu samu ba sai taliya suka dafa suka ci da Mai,duk sun rame Sunyi Baki lalacewar tayi yawa ma,Babu Wanda yake taimaka musu,tunaninsu don sun tuba ga Allah shike Nan baza a jarab cesu ba sai gashi sunga ba Haka bane, wahalar tayi musu yawa yau Momee da kanta ta shirya tace Niima ku kula da gidan Bari naje wajen Farhan ko zan samu tallafi,Latifa tace Allah yasa a Dace Amma da na biki ko zanga Farhan naji sanyi, Momee tace to zo mu tafi,a gurguje ta gyara Fuskarta tare da yafa mayafi tabi Momee suka Shiga Napep suka nufi gidan Su Farhan.
Suna Shiga lokacin Farhan ya fito yaci wanka zai fita,Yayi mamakin ganin Momee da kanta,ya kallesu duk yaga sun lalace sun fita daga hayyacinsu da gani suna cikin wahala.
da sauri ya Isa wajen Momee tare da gaishe ta kamar yanda ya Saba, ta amsa fuska cike da annuri sannan ta fara karanto Masa matsalarsu ta Kara bashi hakuri sannan tace Dan Allah ka hadani da Ahleef ko ba komai zamu roki gafararsa tare da Matarsa.
Farhan ya tabbatar su Momee Sunyi Nadama,Latifa tana gefe ta wani rakube a bango kamar munafuka sai kallon Farhan take ba ko kyafta ido, Farhan Yana kallonta ya lura da abinda take suna hada Ido ya zabga Mata Harara tare da Jan tsuka kadan ya turo Dan lips dinsa gaba kamar yanda Mata sukeyi,Latifa tana gani sai ko ta bangale da dariya tana yaye Baki, fuska ya Kara tamkewa.
Farhan Yana kokarin bawa Momee Number din Ahleef sai ga Ahleef tare da escort dinsa sun shigo da motoci gidan,Momee Baki ta bude ganin motocin da Bata taba gani ba masu shegen kyau da tsada,Latifa kuwa ta ma manta a Ina take kamar Yar kauye Haka tabi motocin da kallo.
Da sauri suka budewa Ahleef mota ya fito cikin Shiga ta alfarma,tuni kamshi ya cika gidan,Yana fitowa ya Mika hannu tare da fito da Shukuransa cikin rantsatsiyar Shiga kamar zasu je gidan shugaban kasa,sun wani Kara ja da kyau,Momee da kyar ta ganesu,Haka Latifa ma Baki bude take kallonsu,Ahleef kuwa Bai kula dasu ba tunaninsa Yan maula ne.
Momee da sauri tace Dana Ahleef, Latifa tace ya Ahleef da karfi, Jin Muryar da ya sani da sauri ya juyo kallo daya ya ganesu, kafin yayi wani taku Momee tazo ta durkusa tana bashi hakuri harda kuka, Latifa ma Haka, Nan Momee ta fara bashi labarin duk halin da suke ciki da abinda Mubaraq ya musu etc.
Ahleef yace ba komai Momee Ni baku min komai ba Allah yafe Mana Baki daya,Shukura tana gefen Ahleef ta kankameshi Haka ta gaida Momee a ladabce, Momee ta kalleta da Faraa sannan tace ki yafe Mana Shukura mun zalunce ku,Shukura ta kalli Ahleef sannan tace Ni dama na yafe muku tuni ban rikeku a Raina ba,Ahleef yace kije Gida Momee zanzo anjima,Latifa tayi sauri ta bashi address din gidan da suke sannan suka tafi gida gwanin tausayi,har Sunyi Nisa Shukura tace kasa a kaisu gida a motarka,Nan ya bada Umarni driver dinsa daya yaja mota ya dauki su Momee ya maidasu gida,sai murna suke tare da bawa Niima labari itama sai dadi take ji zai aureta kwana Nan.
Shukura wurin Maman Farhan ta wuce,Ahleef Kuma ya tsaya tare da abokinsa suna tattauna magana kan su Momee, Farhan ya bashi labarin halin da suke ciki, Kuma gidan Dana maka waya ka siya shine nasu Momee, Ahleef ya tausaya musu kuma yasha mamakin karewar dukiya me tarin yawa Haka.haka Hukuncin Allah yake ko nawa ka Tara a duniya sai Allah yaso zasu zauna,komai kudin mutum idan Allah yaso ka talauce Dole su Kare Babu abinda ya gagari Allah har kaji mutane suna ai wane shi da talauci har abada,sai idan Allah baiga dama ba.
Wurin magrib Shukura tana wajen Maman Farhan tare sukayi girki suna hira,Mama tana Kara koya Mata dabarun rike me gida da yanda zata gyara kanta sosai,wasu Tsumin ta bawa Shukura iri iri da yanda zata dinga amfani dasu,har sukayi Sallar Isha Ahleef Bai dawo ba sun fita tare da Farhan.
Faskekiyar wayarta Shukura ta dauka tare da Kiran Ahleef, bugu daya ya dauka can kitchen ta shige sabo da tana kunyar Maman Farhan, kashe murya tayi tare da narkewa a hankali tana Shagwaba tace My Hero na gaji kazo mu tafi gida pls, wani yarrr yaji jikinsa ya amsa sabo da yanda tayi maganar,cike da so yace sorry Honey I wll be on my way soon, minti nawa zan baka? 10mnt Zaki ganni ok? Kai ta daga kamar Yana ganinta sannan tace to Allah kawo min Kai lfy sannan ta kashe wayar,har tazo bakin kofa zata bar kitchen din,Ahleef ya kirata back,ta daga taji me zai ce, tana dagawa yace na manta ban fada Miki ba? Tace mene fa? Albishirinki? Tace goro Fari Kar,tana jira taji sai yace I LOVE U SO MUCH, wani sanyi da sonsa ya Kara ratsata tayi Murmushi cike da farin ciki tace Love u much more, u are my World and u make me complete, sannan ya kashe wayar,sai ta sake kiransa again yayi picking tace missed u missed ur everything,Ur hand fit in mine just wanna sleep on ur chest sweety, Honey Zaki sa na kasa driving kina kashe min jiki, dariya sukayi gaba daya,Farhan Yana gefe Yana jinsa lokacin Kuma Niima da Dan cikinta tirtsitsi tana motar zasu kaita gidansu, su Momee tuni Ahleef ya musu kyautar gidansu back dama shi ya siye gidan.
Niima kamar tayi kuka taga yanda Ahleef suke ta diga love da Shukura baya kallon ko wacce mace sai Shukura, a ranta taji tsanar Shukura marar adadi ta kamata,Latifa da Umma su tuni Driver ya maidasu gidansu tare da kayansu.
Bayan sun ajiye Niima a kofar gidan suka juya sai gidan su Farhan,Maman Farhan tana mamakin Shukura yanda ta kasa zaune ta kasa tsaye ita mijinta ta Matsu ta gani kusa da ita, Dan yanzu Shukura tafi sabawa da Ahleef ko yini cikakke Bata iyawa ba tare da ta ganshi ba.
Tana Jin karar motar ta yafa gyalenta, sai gasu sun shigo,Maman Farhan tace Kun dawo kenan, wannan duk ta kasa sakewa baka Nan,Murmushi Ahleef yayi Yana kallon Shukura ta kasan Ido, a fili yace Haka takeyi ai da a Office nake ma da tuni taje, Farhan yace ki daina yarda Mama munafuki ne shima shine Dan anace Baya iya yini sai yasa an daukota, dariya Mama tayi tace to Dan sa Ido,Shukura tayi luf Wai kunya takeji,kallonta Ahleef yayi tare da cewa tashi mu wuce Madam,ta kwashi kayanta da Mama ta Bata sukayi musu sallama sannan suka fita,Shukura tace Ina escorts? Na sallamesu Ni zanyi Driving idan Kuma kina bukatarsu ranki ya Dade sai a kirasu sai abinda kike so, hararar Wasa ta watsa Masa suna nishadi suka wuce gida.
Suna Isa gida Umma tace Kun Dade yau,Ahleef da Shukura suka nemi wuri suka zauna a Palon Umma, Baba ma Yana nan, Ahleef ya kwashe komai da ya sani game dasu Momee ya sanar dasu sannan yace Umma yanzu Niima tana Nan da cikinta, gidan ma Allah yasa Ni na siya yanzu na bar musu shi kyauta,sannan kudin da Abba ya bani Wanda suke Usa an hanasu to nayi waya dasu nace a Basu na bar musu kyauta tunda Allah yasa sun iya business tun farko suja jari su juya kudin suna Samun na cin abinci,Sannan Niima Na Sa za a Bata aikin Gomnati su dinga yi tunda Ina da hanya Kinga ya Isa su rike kansu, Sai Latifa a nema Mata University taci gaba.
Albarka su Baba da Umma suka dinga sawa Ahleef yayi kokari da wani ne manta alkhairi zaiyi yaki tallafa musu, Ba komai Umma ai ko ba komai Momee uwata ce,ta rikeni Amana da Abba ko sabo da wannan ai bazan watsar dasu ba,har abada Ina ganin mutuncinta,dama Niima da Latifa sune suka Bata komai to Suma ga inda ta Kare musu. Allah ya kyauta yanzu idan Niima ta haihu sai Kuma tayi aure idan taga zatayi cewar Umma, Ahleef yace ai Momee tace aurarsu zatayi Baki daya Bayan ta haihu tayi istibrai, Farhan ma ya samu matar da zai aura Fatima kawar Shukura ce schl dinsu daya,Amma Wai wajen babansu yaje Kai Masa sako anan ya ganta,manya har sun Shiga zancen,Shukura ta kwalla ihun murna tace Fatima tawa dai Dana sani? Ahleef yace ae itace,yau Munje wajenta kawai naga Ashe itace ma, Umma tace Alhmdllh, Baba ma Haka yace Kinga kawa da kawa ga aboki da aboki,dariya sukayi Baki daya,Shukura sai murna take.
Umma tace Amma zaka dinga zuwa wajen Momee din taka kana gaisheta kamar da,Ae Mana, tace zata zo Wai har gida ta baku hakuri ma, sannan Niima zata zo Wai tayi sati daya anan gidan sabo da karfafa Zumunci,Umma tace Wlh mu ba komai mun yafe tuni ai.
Nan take Shukura ta hade fuska tunowa da tayi ai Tsohuwar budurwar Ahleef ce zai iya komawa yaso Abarsa,Kuma ance indai son farko ne ba a mantawa ko mutum ya tsufa soyayya zata iya tashi.
Kishi ya kama Shukura ta kasa Control a fusace ta mike ta nufi part dinsu,mamaki ya kama Umma da Ahleef,Baba Murmushin manya yayi yaje gano tuni,yace jeka Ahleef matar taka fa tayi fushi,Ahleef yace to me akayi Mata,Umma tace jeka wlh ka lallasar min yarinya ta.
Hankalin Ahleef ya tashi Shukura tayi fushi Bai San me akayi Mata ba,da sauri yabi bayanta,tun kafin ta Isa part dinsu ta fara rusa kuka, bedroom dinta ta shige tare da Sa key ta zauna dabar a kasa irin zaman Yan bori tana ta kukanta,Ahleef ya karaso da sauri ya Murda Handle Amma kofa Gam Gam,yace ki bude me ya faru,ko Baki da lfy Dan Allah ki bude Honey duk ya tashi hankalinsa.
Taki yin magana Kuma Bata bude ba kukanta take rerawa, magiya da rokonta ya Shiga yi idan baza ki bude ba to ki fada min me yake faruwa? tana shesheka tace Bayan kishiya kace zaka yi min, Ahleef Baki bude yace Ni din? Yaushe nace Haka? Yana mamaki tace ae ai Naga take takenka kuma wlh Allah indai kace Haka Ni Kuma sai ka sake Ni,Haka kawai za a kawo min jaraba gida a Jaja min cuta,Dariya ma abin ya bawa Ahleef Bai gane kan Zancen ba, yace Wai meke damun kanki ne? Ae kace Haka Mana ka zageni kaji dadi ai Dole kace min Haka tunda kaga wacce ta fini Kuma wlh baza ka dauko cuta a jikinta ka shafa min ba.
Salati Ahleef yaja shi bai San kan zancenta ba,tace idan shegiyar Nan tazo part dina wlh Allah da Kai da ita sai na yanka ku, Ahleef sai yanzu ya gane Niima take nufi ya Shiga sheka dariya yace to bude dai ki fito muyi zancen, da kyar ya roketa ta bude tare da fitowa, yasha mamaki ganin Fuskarta kamar an watsa mata yaji tayi jajir ga Hawaye ta ko Ina duk ac din dake gidan ta hada zufa.
Hannunta ya ruko ke yanzu Akan wata Niima kika Bata fuskarki Haka? Hawaye ya Kara shararo Mata tace gashi Nan yanda kake fadar sunan ma da dadi kake tsarawa kace NIIMA Mana Amma sai kayi iyayi kasa kalkala,Ahleef ya danne dariyarsa ya kumbura murya da Bakinsa yace to NI'IMA tace ai dai baka birgeni ba Tunda sai Dana fada kayi,yace muje nayi Miki wanka jiba yanda kike zufa Akan kishin banza,ai kinfi karfin kiyi kishi da Niima kucaka,Dariya Shukura tayi tana share Hawaye Wai taji dadi yace Mata kucaka.
Ya zura Mata Ido ya hango yanda take murna,Murmushi yayi tare da daura ta a cinyarsa yace to me zanci da wata Niima me katon goshi Bayan ga Shukura Balarabiya,Shukura ta Kara wani shigewa jikinsa tana Jin dadi Yana ta kushe Niima itace a sama, yace Shugabar Matana na aljanna Hurul ein,a aljanna ma sai abinda kika ce, Shukura tayi dariya tace Idan na Shiga Aljanna shuuma zan zama,Ahleef ya fara dariya,tace kasurgumar Yar giya zan Zama a aljanna kullum Nasha nayi tatul, Dariya Shidai Ahleef kawai yake na labarin Shukura sai da ya gaji sannan ya dauketa sukayi wanka suka kwanta suna hirarsu ta masoya bacci ya kwashesu me dadi.
Bayan sati biyu su Momee komai ya Dan fara gyaruwa suna Dan Jin dadi komai ya fara zamar musu Normal Ahleef ya gama musu komai Kuma Yana zuwa akan lokaci, yaune Kuma Niima ta hada kayanta ta nufi unguwar su Ahleef, da kyar masu gadi suka barta ta Shiga sai da ta Kira Ahleef a waya sannan ta samu aka bude Mata kofa, wani maaikaci ne ya rakata part din Shukura,Ahleef Yana Office Amma ya kusa dawowa Shukura tana Bed room ta Gama tsantsara masa girke girke masu dadi, tayi wanka tana tsane ruwan jikinta taji Sallamar Niima, Jin mace ce sai ta sakko daga sama daure da guntun Towel Fari ga karami a hannunta tana tsane ruwan gashinta, lekowa ta fara yi kadan ta hango Niima zaune, karasa sakkowa tayi tana tamke fuska Amma ta danne kishinta da Faraa ta tarbeta suka gaisa, Niima sai kishi take na Shukura tana wani Shan kamshi,Shukura ta Dan zauna kadan sannan ta kawo Mata kayan ci Dana sha.
Tana zuba Mata juice Ahleef ya Danna Door bell ya dawo, cike da Shauki tace Hero ne? Yace yeah Honey I'm Back, kofar ta bude a hankali cikin takunta na Jan hankali, Bai San anyi bakuwa ba ya daga Shukura sama tana Masa Oyoyo ajiyeta yayi tare da rungumeta a jikinsa suka fara kissing din juna sunkai 5mnt sannan Shukura tace muje ciki Mine.
Zai zame Mata towel tace akwai fa bakuwa a Palon Nan baka ganta ba,sai lokacin yayi tozali da Niima tana kallonsu kamar Mayya ko kyafta ido Bata yi,kishi ji take kamar ta kashe Shukura ta huta.
Da kyar ta iya gaida Ahleef,ba tare da ya kalleta ba ya amsa sannan ba kunya ya tsuguna yace Honey hau muje ki min wanka, bayansa Shukura ta haye kamar yarinyar yaye tana Wasa da gashinsa tana cewa Unique I love u, ta juyo ta kalli Niima dake Shirin kuka sabo da kishi, Shukura tace Bari mu sakko pls baza mu Dade ba wanka kawai zan masa.
Niima kanta ta dauke gefe tare da goge kwalla a boye su kuwa tuni ma sun bace Basu San tanayi ba,Niima tana Palon tun tana sa ran ganin zasu sakko Shuru kamar an shuka dusa, saida suka Gama Raya sunna sannan suka sake wanka tare da shiri ka rantse party zasu je suka sakko kasa, Allah sarki Niima sai gyangyadi take yi bakinta cike da yawu na laulayi HHH.
Ahleef ya kalleta kadan baya Jin tausayinta ko kadan gashi ta Sa Yar Jakarta a gaba, Shukura tace sannu mun barki kina jira, Baki cike da yawu Sautin maganarta baya fita sosai tace Bha..Bha...komai,Bhani...yedha( Leda) idan kina dha yita(ita) Shukura tace ai yawu Zaki Tara a ciki? Niima ta daga kai, No Ni Mijina abinci zai ci tsakani da Allah kyankyami gareshi bazai iya cin abinci Yana hangoki kina Tara yawu a Leda ba,Ina laifin ki na Shiga toilet, tsaya a raka ki wajen Umma ita zata Miki dabarunsu na Mata sai kiga yawun ma ya daina taruwa.
Ahleef waya yake dannawa baice komai ba, Shukura ta Kira Me aiki tace Barira kaita wajen Umma,Niima tace ai Ni a Nan zan zauna ba wajen Umma nazo ba,Harara Ahleef ya zabga Mata ba shiri yace to ita Umman ba gida daya muke ba,ko Shukura kawarki ce?, a Dalilin me Zaki zo wajena Ni, salon ki takura mu motsi bazanyi ba kina kallonmu, tsawa Ahleef ya daka Mata ba shiri ta mike tabi Barira wajen Umma zuciyarta na tafasa tana Kara Jin tsanar Shukura.
Ahleef yace bazan iya cin abinci yanzu ba Bari sai anjima yawun Nan nata ya daga min hankali,dama yawunki ne ko Sha zan iya Amma wannan Abu ba kyan gani, Shukura taji dadi Ahleef ya Kori Niima tasan badan Allah tazo musu ba, kallon American film suka fara Shukura tana jikinsa Yana Wasa da Dukiyar Fulaninta etc.
Da dare wurin 8pm Niima tayi wanka harda kwalliya ga ciki a gaba kurtsitsi dashi Wai a Haka take so ta birge Ahleef, harda Sa damammun Kaya ciki ya fito, ga mazaunai sun wani shamule kamar babu ba karamin Muni tayi ba,Amma Haka tace Umma zanje wajen Shukura muyi Hira,Umma ta tabbatar wajen Ahleef tazo badan Allah tazo musu ba, amma Bata ce komai ba tace a dawo lfy, Shukura suna Palon sama Babu kayan kirki a jikinsu suna ta zuba love sun zauce, dai dai wannan lokacin Niima taga basa Palon kasa kawai ta tafi sama tana ta kwada sallama Basu San tana yi ba, kawai sai ji sukayi an wangale labule an shugo tana sallama, Ahleef ya ganta ransa yayi mugun baci, Shukura tace kut..mene Haka Zaki afkowa mutane daki ba sallama ko Nan huruminkine, jahilar Ina ce ke?, Hijab Shukura ta lalubo zata sa Ahleef ya rike yace ta Saba gani ai kyale ta zauna ayi a gabanki ki gani idan zan fasa shegiya Mayyar Karuwa, dabba, Shukura ya jawo tunda akwai night wear a jikinsu Allah yasa, kawai yaci gaba da abinda yake,ba shiri Niima ta sauka da gudu kasa,sai da ta Gama kukanta sannan ta lallaba ta koma part din Umma tare da shigewa Room din da aka sauketa , kusan kwana tayi tana kuka tana tsinewa Mubaraq.
Da safe da wuri ta Kira Momee ta sanar Mata abinda Ahleef ke Mata,sannan tace Shukura ce a gabansa ta Gama shanyeshi,Momee tace ai Ni danaji Shuru na zata kun daidaita dashi ma Bayan kin haihu zai aureki, Amma ki gwada fada Masa idan yaki Ni zan Masa dabarar da Dole zai Amince kin San Yana ganin girmana.
Tun farko ke kika jawo,Nan Momee ta Kara Mata salon da zatayi Ahleef ya dawo sonta har ya amince zai aureta.
Da safe ya fito cikin kana Nan Kaya yayi azabar kyau,Shukura ta rakoshi cikin Shiga ta alfarma suna kamshi, Niima ta saman bene ta hango su suna ta soyewa a cikin mota,da sauri ta Sa hijab har kasa ta nufo su itama, har kasa ta tsuguna tare da gaida Ahleef, lfy kawai yace yaci gaba da magana da Shukura dake gefensa, ta maza Niima tayi tace Dan Allah Yaya Ahleef kayi hakuri ka yafe min abubuwan da nayi maka a rayuwa sharrin shedan ne, bazan sake ba,Dan Allah ka bani lokaci anjima idan ka dawo zan Gaya maka wata magana sako ne kawai zan fada.
Bai ce komai ba Shukura tace ance an yafe Miki har sau nawa Zaki nemi yafiya ya yafe Miki, a wayance Niima ta harari Shukura ba tare da kowa ya gani ba,Ahleef yace time da zan Baki kuyi magana da Honey idan ta Amince sai ta bani time na saurareki.
Niima zatayi magana kenan yawu ya ciko Mata Baki har Yana tahowa kamar zai zubo gwanin kazanta,ba shiri tace uhm...ohmm....sai ta mike tayi baya da gudu kafin kace me yuuut sai gata jikin bishiya wurin flowers tana kyara Amai, Shukura ta zaro Ido waje tana kallon Ahleef dake dariya,tace Dan Allah ka daina Mata dariya Kar ka jawo Allah ya jarabceni da laulayi irin nata,Allah ma baya Sa ba ya Kara kyalkyalewa da dariya tare da cewa duniya kenan.
Latifa yau ta dau wankan Sugar zata tafi Office din Farhan an rambada Powder da jambaki, Momee tace ai gidan Make up Zaki je Nan ta zaro kudin kwalliya ta bawa Latifa daga can zata wuce Office din.
Zamu ji ya Latifa za a Kare oho.???????????????????????????? Nafi yiwa Niima dariya wallah, magana ga yawu cike da baki hhhhh….
Up…up…Ni
AsmaBaffa.
[7/22, 1:14 PM] Sis Asma: ????????????
JIN DADI SABO
76-80
Official
By
AsmaBaffa
Farhan Yana Office hankali kwance Yana waya da Fatimansa wacce zai Aura sai zuba love suke yarinya Yar mutunci ga tarbiya ga wayewa gata itama kyakyawa da ita.
Latifa taci kwalliya ta Sha kyau itama, Office din Farhan tayi knocking,kafin ya Bata damar Shiga sai da ta gyara tare da kallon Fuskarta a mudubi, come in yace sannan yaci gaba da wayarsa ta soyayya, Yana ganin Latifa ce ya canja fuska Amma sai ya danne yace I will call u back later ya datse Kiran, sannan yace zauna, Latifa sai da ta wani karairaye sannan ta zauna tana fari da Ido tana juya kafada.
Farhan ya girgiza Kai wani haushi ma ta bashi yace fadi meke tafe dake Ina sauri akwai aiki a gaba na,Latifa tayi fari sannan tayi wani murmushin Jan hankali sannan tace zuwa nayi na maka Godiya Akan abubuwan da kayi mana, yace no Need ai ba damuwa,Murmushi tayi tace ok tare da Mikewa tsaye tana juyawa Dan ya gani,sai taci gaba da magana tana juya idanu baka da wani aiki da zanyi maka sabo da abinda kayi mana Ina so nima na saka maka da alkhairi kaima,Farhan ya zaro Ido yace Dan Allah nayi bana bukatar a saka min.
Latifa ta kalli Office din tana kashe Masa Ido tare da cewa Naga kamar yayi dirty ai da ko shara da mopping nayi maka,yace no na gode jeki kawai, Dan Allah Ina so na fada maka magana Amma tamin nauyin fada, biro ta dauka da paper a saman table dinsa kana ta Rubuta Masa I love u a jikin paper sannan ta Mika masa,ya karanta takaici ya kamashi ba aji ba komai direct, a fili yace Ina da matar da zan aura kiyi hakuri, Latifa takaici ya kamata dama Bata fiye kunya ba sai ta hayayyako Masa da masifa Kar ka Soni din sai me Dan nace Ina sonka ko Kai kadai ne Namiji mtswwww taja tsaki tare da bude Kofa ta fice a fusace.
Tsaki yaja ya Danna Kiran Fatimansa suka dora daga inda suka tsaya, Momee ta bawa labarin abinda ya faru tsakaninta da Farhan harda Hawaye,Momee tace Kinga kin nuna Masa Baki da tarbiya bazai taba sonki ba,Haka na koya Miki kiyi? Nan Momee tayi ta masifa.
Niima dai dai Lokacin data San Ahleef Yana dawowa daga Office lokacin taci kwalliya yau dai tayi kyau ba laifi,Compound ta fito tana jikin wata bishiya dake facing din inda ake parking cars yanda Dole Ahleef ya ganta, Bata Dade da Zama ba sai ga Motocin Ahleef sun shararo cikin gidan,ya fito da sauri sabo da Burinsa yayi sauri yaga Shukuransa,Bai kula ma akwai wata Niima a gefe ba tuni hankalinsa yayi wajen Matarsa,jikin kofar Kuma Shukura tana Nan ta kyafe cikin kwalliya da Shiga ta gaske Wanda kowa ya kalleta sai ya Kara,Niima sai gani tayi Shukura ta sakalkale mijinta cike da Shauki tayi ciki dashi tare da banko kofa.
Nan suka barta tayi tagumi tana sake saken duniya a ranta tana neman Mafita yanzu ta fara tunanin Ahleef ya Mata Nisa yafi karfinta, sai dai Shukura abin ba a cewa komai sai du'a'i kawai.
Hankalinta tashe tayi cikin gida bangaren Umma kwalla cike a idonta,Zazzabin son Ahleef ya lullubeta sai yanzu Allah ya jarabceta da matukar kaunar Ahleef,ji take kamar ranta zai fita sabo da sonsa, idan ta kalli cikin Mubaraq dake jikinta sai kuka ya Kara kwace Mata tare da Nadama, Umma ita kanta tausayin Niima ya fara kamata Kuma ta gane Ahleef take so.
Niima ta iske tayi tagumi Hawaye na zararo Mata masu dauke da sinadarin dafin son Ahleef a cikinsu????
Lallashi tare da Nasiha Umma ta Shiga yiwa Niima,Kuma Niima taji sanyi a ranta, na gode Umma Dan Allah Umma kisa Baki Ahleef ya aureni Nan gaba,Umma tayi Shuru sannan tace zan gwada rokarsa Amma idan yaki bazan Masa Dole ba,matar mutum kabarinsa Dole idan mijinki ne sai ya aureki,idan ba shi bane idan duniya zata taru a kansa wlh bazai aureki ba,kiyi Addua Allah Baki na gari me kaunarki.
Niima tace na gode Umma tana share hawayenta.
Da dare Ahleef yazo wurin Baba suna Hira Umma ta shigo itama ta zauna,sai da suka nutsu sannan ta kawo bukatarta na Ahleef ya taimaka ya auri Niima Nan gaba,Baba zaraf yace Saudatu ki fita daga idona,ke ko kunya bakya ji Zaki sa ayiwa Shukuran taki kishiya da kanki,Allah ne ya halatta,Amma Ana so mutum ya nemi yarinya ta gari ba irin Niima ba,mene Bata yiwa Ahleef ba,sai yanzu da bukatar ta ce sannan zata damu Mutane,lokacin da shi ya Shiga wani Hali a kanta ta tausaya Masa?to wlh ko ba Raina ban yarda ya aureta ba.
Umma a sanyaye tace Mene abin fada anan tunda kace Haka ai shike Nan Nima ba cewa nayi Dole ba,idan yaga zai iya nace,to bazai Aureta ba cewar Baba Kuma kika takura wlh da kaina zan koreta daga Nan gidan.
Ahleef ba karamin dadin Maganar Baba yaji ba,dama shi ko me za ayi bashi da Burin karawa Shukurnsa kishiya bare ya auri wata Niima.
Shukura ce ta shugo part din Umma kenan ta Dan tsinci Zancen kadan Amma Bata Gama Jin me ainihin Zancen ke nufi ba,share zancen tayi kawai tare da gaida su Umma ta nemi wuri ta zauna itama sannan ta ajiyewa Umma wani flask me kyau, me Kuma kika dafa na kwadayi yau? Umma ta furta, Murmushi Shukura tayi tare da cewa Baba Naga Yana son danwake shine nayi Masa,da Tsantsan Jin dadi Baba yace oh Yata na gode Allah ya muku albarka, Umma tace Ameen, kwalliyar da Shukura ta sheka itace ta tafi da hankalin Ahleef sai binta yake da kallo ya kasa dauke idonsa a kanta, Shukura tana kallonsa ta gefen Ido Kuma taji dadi tasan kwalliyarta tayi,Mikewa tayi ta wuce part dinsu Kar Ahleef ya kunyatata sabo da taga sai wani magana yake mata da idonsa daya tana tafiya yayiwa Su Umma sallama yabi bayan Shukuransa.
A kitchen ya isketa tana dube dube sai ji tayi ya rungumeta ta baya tare da Rada Mata sallama a kunne,Jikin Shukura har ya harba wani bukatar Mijin nata ya taso mata tana a jikinsa ta juyo suna Facing juna,hannayenta biyu tasa ta tallafi fuskarsa tana kallonsa a hankali in a sexy way tace kana da kyau Hero I love u,kissing din lips dinsa ta farayi a hankali,shima Yana yi har suka koma da zafi zafi kamar zasu cinye kansu Yana cewa I love u to the bone Bae.
Daukanta yayi cak suna kissing juna ta ko Ina haka suka fito zuwa Bedroom, tun kafin su Karasa sun cire kayan jikinsu, Nan suka Shiga baje harkoki Baji ba gani abin nasu sai Wanda ya gani, Ahleef ya susuce sai kalamai yake ratartakowa Shukura Mata itama Haka daga Nan ya Shiga zuba Mata adduoi Wanda bai ma San me yake cewa ba, sai Bayan sun nutsu tare da tsarkake jikinsu Yana zaune ya mike kafafu saman bed bayansa ya jingina da fuskar bed din.
Sanye take cikin wani mini skert da Yar Riga ko cibi Bata Kai ba me siririn hannu tayi kwalliya sosai tayi kyau,tsakiyar kafafunsa ta zauna itama Yana Danna system ta lafe a jikinsa,hannunta dauke da glass cup na fresh milk tana Sha tana bashi shima Yana Sha Yana aikinsa.
Ba tare da ya kalleta ba yace Honey gist me,Murmushin da tasan Yana tafiya da imanin sa ta saki, cike da Shagwaba tace Hero makaranta fa University ga result dinmu ya fito yaushe zaka sani, Zancen ya share, kukan Shagwaba ta fara masa, mene Kuma? ya tambaya, ba Kaine ba Ina ma maganar schl sai kana shareni baka son zancen ma, a hankali ya lankwaso da kansa tare da daura Mata kiss a lips dinta itama ta Kara turo Masa Dan lips nata tare da sakalo hannunta daya ta wuyansa ya Shiga kissing nata sai da ya gaji sannan yace ina sane da schl Dinki Baby,bana son kina barin gida kullum bazan jure ba Amma Dole inshallah Zaki je schl ki jirani.
Murna ta kama Shukura bata San sanda ta rungumeshi ba tana kissing dinsa ta ko ina zata yi University itama a daina Mata iyayi, dariya Ahleef yake sabo da yanda shukura take murna kamar zai sata Aljanna.
Niima ganin ba fuska wajen Ahleef kawai sai ta tattara nata ta dawo gida wurin Momee, ta waya Momee ta Kira Farhan da Ahleef suzo tana son ganinsa cikin gaggawa tare da Farhan, Babu komai a ransu suka yi parking compound na Momee kana suka Shiga bakinsu dauke da Sallama,Latifa ta labe jikin kofa tana leken Farhan,Niima Kuma Ana can ana cancada kwalliya.
Momee da farin ciki ta tarbesu tana murna suka gaisheta cike da ladabi,Ahleef yace Momee gamu da fatan dai lfy, Baki washe tace wlh lfy Lau,wata alfarma nake nema a wajenku,nasan nafi karfin komai a wajenku musamman Kai Ahleef Umarni ma idan na baka nasa zaka yarda, Ahleef yace Haka ne Momee ai har yau uwarmu ce har abada ma, Baki Momee ta Kara washewa sannan tace Ina so Ahleef Dan Allah ka rufa Mana asiri ka auri Niima idan ta haihu,Farhan Kuma ka rufa min asiri ka auri Latifa,kafin Momee ta Gama zancenta Gumi ya jike Ahleef duk da ac dake Palon,Farhan kuwa ko a gefen rigarsa yace Momee kiyi hakuri wlh Ina da wacce nake so na rigada na fitar da matar aure saura 3mnths biki ma,Allah ya Bata miji na gari Wanda ya fini,Kuma na gode sosai da Babban tayi da kika min,Dukul Momee taji a ranta,a fili tace ba damuwa Farhan na gode Allah bada zaman lfy yace Ameen.
Latifa Dake labe hawayen kauna ya kwararo mata tasan ta rasa Farhan shike Nan.
Saura Kai Ahleef me ka gani? Ahleef yace kiyi hakuri Momee bazan iya auren Niima ba wlh sabo da Shukura baza ta iya Zama da kishiya ba,baya ga Haka ma yanzu Niima Bata Raina ko kadan,Momee ta jinjina Kai sannan tace kaje kayi tunani Ahleef tukun Nan da 1wk sai muyi maganar again.
Ahleef yace Momee bazan boye Miki ba ko nayi tunani amsa daya ce, da naso Niima kin sani itace ta yaudareni, ban yarda ba Ahleef na baka time kayi tunani cewar Momee,ganin Momee taki yarda yace to zanyi tunani Momee tunda kince,Murmushi Momee tayi tare da cewa yawwa na gode,Mikewa sukayi sai gida.
Shukura taga Ahleef ya shugo dauke da damuwa a fuskarsa tare da sassan jikinsa da gani ransa a bace yake, cikin nutsuwa Tasha kwalliya ta gaske tana walwali tare da kamshi ta rungumeshi tare da kwantar da kanta a saman lafiyayyen Kirjinsa, Kam Kam ya Kara kankameta a jikinsa Yana shakar Kamshinta,Jin Bai ce komai ba sannan ya Saba fada Mata zafafan kalamai da kisses Amma yanzu ko daya baiyi ba sai rungumeta da yayi a jikinsa Yana sauke ajiyar zuciya.
Saman lumtsumemiyar 3seater ta jashi suka zauna tana saman cinyarsa a zaune hannayenta ta sarkafosu ta wuyansa suna Facing juna,Bai son kallonta ma Dan kar ta gane Yana damuwa,amma tuni ta rigada ta ganoshi,sansanyar muryarta tace lfy My Heart? me ya sameka?waye ya Bata ma Rai?waye ya taba min Mijina? Murmushin karfin Hali yayi sannan yace Honey bana boye Miki komai wannan ma bazan iya boye Miki ba, Nan ya Bata labarin abinda Momee tace na auren Niima,kafin ya gama labarin Shukura tuni Hawaye sun wanke Mata fuska,yace kinji abinda tace min,a hargitse ta mike daga jikinsa,Yana riketa tana kwacewa,sai kokawa suka fara tukuru tana kuka,Yana rirriketa tana zillewa,da kyar ta samu ta kwace kanta ta nufi Bedroom dinta da sauri ta zura Hijab dinta sannan ta fito zata bar gidan, ya riketa Nan ma suka ci gaba da kokawa tana kuka da Nishi, Ina zakije daga fada Miki magana ko nace Miki zan aureta, tana Haki tace gashi ka fada min kawai kace kana son abarka zaka Raina min hankali kace wata Momee waye ai na San halinku maza,Ni bazan zauna da Kai ba ka sakeni kawai ko ka barni nayi tafiyata bazan zauna da Kai ba ta Kara fashewa da Kuka.
Yayi lallashin duniya har ya gaji ya saketa ai kuwa ta Sa Hijab dinta tayi waje kamar zata tashi sama,tunaninsa Wasa take ko wajen Umma zata je,Ashe tuni ita ta bar gidan ma,da sauri yabi bayanta wajen Umma.
Yana Shiga Umma ta tsorata yanda yake a hargitse a gurguje ya labartawa Umma komai,Umma tace maza bi bayan yarinya ta ka dawo da ita Kaine da shirme ta ya zaka fada Mata wannan magana Kai tsaye,Baba da dawowarsa kenan daga unguwa yace sai Naga kamar Shukura tana tare taxi Zata Shiga,da sauri Ahleef ya fita tare da fisgar mota yabi bayanta, Allah ya taimakeshi Bata samu taxi ba,sai kuka take a gefen titi tana tafiya, Horn ya Danna Mata tana tabbatarwa Ahleef ne sai ta Kara sauri zata tsallaka titi saura kadan mota ta bigeta, ransa ya mugun baci,parking ya gyara ya fito da sauri tare da jawota daga titi tana kokawar kwacewa ya wanke ta da gigitaccen Mari,kafin tayi magana ya Kara Mata wani sabon Marin sannan ya finciketa ya jefa ta a mota yasa lock kana ya Shiga shima tare da Jan motar suka koma gida tana dafe da kumatunta Wanda yasha Mari yayi jajir dashi.
Yana parking niyyarsa ya kaita wajen Umma ta lallasar Masa ita,amma Yana parking tana kukanta ta balle murfin motar ta fice tayi part dinsu da sauri, kansa ya daura saman sitiyari duk abin duniya ya Masa zafi,ya rasa meke Masa dadi a duniya sai daya gaji da Zama sannan yaje wurin Umma tare da cewa Umma Dan Allah kizo ki lallasheta ta hakura,Murmushi Umma tayi tace ba ruwana wa yace ka fada Mata,kaje ka shawo kanta tun wuri.
Fita yayi ya kyale Umma Yana Jin haushi taki zuwa ta shawo Masa kan Shukura,Shukura kuwa bedroom dinta ta shige Bata leko ba,yayi yayi ta bude Amma taki Haka ya hakura shi kadai ya kwana har gari ya waye da kyar yayi bacci Shukura ma Haka sun rigada sun Saba kwana tare suna manne da juna.
Bata fasa ayyukanta ba ta fito tayi komai har breakfast ta shirya kamar yanda ta Saba sai dai tana yi tana hawayen kishiya,tana tsaka da shirya Dining Ahleef ya fito sanye cikin jallabiya,suna hada Ido yaga har yau kukanta takeyi,mamaki da dariya a bin ya bashi,wani dadi ma yake ji duk a kansa ake wannan kuka Lallai Ana sonsa sai ya godewa Allah.
Kallonta yake Yana sakar Mata Murmushinsa ita Kuma tana harararsa ga Hawaye nabin kumatunta, Ahleef yace sannu da aiki Honey har kinsa naji yunwa wannan kamshi Haka,Banza ta Masa.
Tsokanarta yayi yace da Zaki hakura ma ai da na Baki kyautar gida da mota sannan na kaiki Makka,ai kafin ya rufe Baki tace bana so ko duniya ce ka rike abarka,me zanci dasu tana Harara tare da ajiyar zuciya, dariya yayi sosai yaci gaba da tsokanarta ke da Zaki ma huta da aiki idan na kawo Miki Amarya tana tayaki, Jin ya Fadi Haka a ranta tace Lallai da gaske ne abin Sai ko ta Kara barkewa da kuka sosai take rerawa, Ahleef Baki bude yake kallonta ta shige Bedroom ta dakko takarda da biro tace sai ya Rubuta Mata saki, Bai kulata ba yace Ni ai Ina sonki tare dake nake so na rayu kima daina tunanin wani rabuwa, wucewa tayi zata koma dakinta Bai hanata ba ta Shiga ranar Haka ya yini ba dadi har aka kwashe 3days Shukura taki sakkowa ta hakura, shiryawa yayi ya fita Bai tsaya ko Ina ba sai Gidan Momee.