KANWATA HAUSA NOVEL

KANWATA HAUSA NOVEL

Farhan dan Allah wata alfarma xakamin haba abokina ai tsakaninmu ba irin haka fadi kanka tsaye yai dariya wani abu ke damuna haba muhd inbaka fadanba wane kakeso kafadawa baka da kamata nima banda kamarka Fadya ce matsalata matsalarka kamar ya santa nake narasa yadda xanyi ta fuskanceni waima wacce fadyar kanwarka yai tsaki tunfarko shine baka fadanba to nai mata miji sekaje ka nemi wata xumbur ya mike what yasa daria xauna kaji Allah ya temakeka ban bada itaba karkaji komai xan sameta nagode aboki sukacigaba da firarsu.

Hartakai bakin kofa yace inkin kai kayan kixo muyi wata magana to yaya ta fice .
Kace xamuyi maga eh daman so nake naroki wata alfarma tai saurin dago kai haba yaya alfarma kuma bani umarni kawai xakai nabi yaji dadin batunta yawwa kanwata aikinsan muhd ko eh yaya to shine yaxo guna kan inbashi dama yaxo kugana kan yanasan ku fahinci juna watakil hakan takaiga aure kinga yanxu university kike yakamata ace kin tsaida wanda xaki aura tai shuru dakyar ta iya cewa to yaya tunda kayadda da dabi’unsa nima nayadda matsayinsa na babban abokinka yawwa kanwata nagode tashi kije.

Koda tabar dakin bayan dakinsu taje tasha kukanta watakan ita daya take haukanta shi bema san tanaiba tunda gashi da kansa yake mata batun wani yanaima ma wanin kanfen.
Ita kadai tasan mai takeji aranta duda kokarin datake wajen yakiceshi aranta wajen ganin bata nuna wata alamaba duda kuwa da’ace yayan nata mai ganewa ne da tuni ya gama fuskanta.

Mum wai yaushe dad xai dawo ne eh to may be a cikin week dinnan to Allah yadawo dashi lpy amin fara kina da bukatar kudine babu daya kawai naga ya jima acan tai dariya nima haka nagama naw korafin yako karatun naku karatu basauki mum niduk nagaji wallahi hakuri xakiyi haka karatu yake da cinrai.

Waiko ya kike ganin tafiyar karatun fara komai normal aikasani duda yar shagwabace bata wasa da karatu duda ta fara mita ta gaji aikindanta batasan wahala kafin ta sabane ince dai ana kiyaye dokata tai dariya itama kanta batasa soyayya atsarinta ba balle ta bada fuska yai dariya haka nakeso nafiso tai karatu dakyau.

Fadya na iya kokarinta wajen tsayawa da muhd duk dan farantawa yayanta rai duda kuwa bata taba jin sansa arantaba bakumatajin xata soshi.

Kanwata
Wane karatu haryaushe karatun xai kare nagaji wallahi inba sokake sai na mutu sannan xaka aurar da ita ba tafara sharar kwallah ya durkushe gabanta kiyi hakuri inna nai miki alkawarin awatannan xa’a gama komai na auran tasa dariya kokaifa ya mike nixan wuce to Allah yabada sa’a yayi albarka ya amsa da amin.

Lafiya kuwa dady naga kamar kana cikin damuwa yai dariya baccine kawai a idona Fara to dady kaje ka kwanta ka wuta kasan rashin bacci natsalane ya mike kumafa gaskiyarki bara naje.

Mum naga kamar dad nacikin damuwa mekika gani naje inai masa mgn yanacan cikin tunani towo bara naje na sameshi.

Zarya kawai yake adakin dadin fara lpy kuwa yajuyo yaxauna gefen gadon itama ta xauna nan ya fada mata dik yadda sukai da innars tai shuru kafin tace ai wannan ba matsala bace kamarya ba matsala bace ka eh ba matsala bace tunda ai babu wanda takeso balle ace bai shiryaba cikin yayan abokanka kabaima daya wanda xai barta tai karatunta sai alokacin yai dariya kumafa kin kawo shawara mai kyau bama dan abokina xan baimaba ba.

Salim din yaya faiz yasha mun magana inacewa yakara time shima yaya faix din haka xance kawai yaxo su tattauna nasan innar xatai farin ciki itama tai dariya Allah ya nuna mn time din lpy.

Fara na'am dady kishirya yau xakiyi bako ni nabashi dama ta dafe kirji bako dad eh kinma sanshi yayanki ne salim amman dady bai bari yaji mai xatace ba yai ficewarsa.

Wai fara gambo batace miki kina da bako bane ta turo baki tafadan to maxa kije aman mum maxa tashi kije.

Ko sallama bataiba taxauna yana kallonta ya washe baki hajiya Fara ina yini dakyar ta iya amsawa da lpy.

Wai kai vakasan amaka shiru bane ka ishenifa yai dariya ayimun afuwa baxan sakeba pls alfarma xaka min katai maka kaje kasamu dad kace bakaso na pls yai dariya ina baxan iya ba tokuwa wallahi kadaukowa kanka wahala dan wallahi baxan sokadady.

Kanwata
Yanxu mum haka ake ace baxa’a tambayeni ba kawai ace anmun miji ama rasa wanda xa’amin sai salim niwallahi banasansa to inbakya sansa wane kikeso ni wallahi uncle Farhan nakeso toshidin dan uban waye haba mum shinefa nake baki lbr malaminmu a sch what baki da hankali wallahi kima rasa waye kikeso sai teacher kuma na private sch wanda akoyaushe xe iya barin aiki haba mum ni bakudinsa nakeso ba shi nakeso kinga kimayi shiru da wannan batun tunkan dad dinki yaji.

Ni wallahi dabadan badanba sai ince ya salim kai maye ne ance ba’asanka ana soyayya dolene nace banasanka banasanka.
Gaskiya baba nagaji da abinda Fara take mun nama yanke shawarar hakura da ita kayi hakuri bansan xumunci ya baci ina baxai yuwuba xan samu baban nata kotanaso ko bataso se anyi baxata batan tsarina ba.

Yanxu a hakane kake cewa ka isa da yarka har ada innaxo nace kabaima salim dama yabayyana mata kansa kace inyi hakuri lokacine dakanka xaka ban time innace kar wani ya rigashi kace ka isa daita vata kula kowa to jiya salim yasameni yafadan irin cin kaahin da take masa ita tanada wanda takeso what Faran eh ita kayi hakuri yaya xan sameta.

 Fara fara yake kwalla mata kira da gudu ta fito opp lpy dad kake kwalan kira haka keni kike tambaya lpy nake kiranki yi hakuri dady tafada xonan magana xamuyi ta fahinta to dady.

Kanwata
Mai kika cema salim takalleshi bakomai karya kike kifadan mai kika ce masa cewa nai ya rabu dani inada wanda nakeso what me kika ce eh dady cewa kai nai karatu karnai wasa da karatun kar inbiyema soyayya kuma naga ina karatu soyayyata da Farhan bata taba hanani kawo maka result mai kyauba ya mike naji wayeshi farhan din dad malamin mune a sch what kina da hankali kuwa awacce unguwa yake dad dan unguwar nan ne yadan xauna dan wane gidane dad dan gidan rinji ne ya mike wallahi baxai yiyuba yata baxata taba auran talakaba ta fashe da kuka nima wallahi bansan yaya salim farhan ne xabina.

Yauce ranar farko dayafara danasanin yima fara duk abinda take so.

Alhaji lamarin yarinyar nan yafa fara ban tsoro ta dena fitowa abinci in ankai yadda aka kai haka ake daukowa ya mike bara naje basameta tana kudundune akan gado ya dagota jikinnan rau xafi subhanallahi baki da lpy sai hawaye da sauri ya fice ya hado mata tea mai xafi yabata nan danan gumi ya rufeta haba fara yakikeson illata kanki tai shiru kiyi hakuri da xabin danai miki nan gaba xaki fuskanceni sai kuka dad dan Allah kabarni da xabina wallahi banasan salim xan iya mutuwa na aureshi aiko saidai ki mutu aure ba fashi ya mike gami dayin tsaki ya fice .

Alhaji kasan mai xakai yaron xaka kirawo kabashi kudi kasa shida kansa yace bayayi yaxo yace mata yadena santa kin kin kawo shawara gobe xansa akiraminshi yawwa alhaji dan gaskiya banasan kasaida akuya taxo tana cimana danga ai hakan xanyi Allah dai yakaimu goben

Kanwata
Na F.A.Ya’u

Kanwis yakika ganni takalleshi gaskiya ka hadu yaya amman hularce dai bari kaga ta shiga dakin tadauko wata yawwa kaga wannan itace dai dai yakarba yana dariya kai nima sai yanxu naga nafito kanwar tawa ta iya xabi.

Yaya naji umma na cewa agaidasu wai ina xaka ne yai dariya aff afuwan nayi mantuwa ban fadamiki ba baban auntinki yake kirana bansan mai xai cemunba tai dariya wadda kana gani yake ce to yaya Allah yasa adace agaida mun da ita yace amin bari naje yana fita ta fada bandaki tasha kukanta ta fito.

 Zaune yake kasan kafet din kansa akasa yaji shigowar sa ya mike alamar girmamawa saida ya xauna sannan shima yakoma mazauninsa yagaidashi cike da girmamawa kafin yace.

Nakirakane dan muyi wata masala Fara ta fadan komai inasan kamin wata alfaema komai kakeso xan baka daga million daya xuwa hamsim yakalleshi baba wacce alfaema kenan yawwa so nake karabu da fara what yabfada baxan iyaba wallahi kudi baxai taba sawa in saida soyayyata ba  to kuwa inbakai tasaukiba inada hanyoyi da dama na rabaku inason daga yau bakai ba yata na fada maka baba dan Allah karka rabamu wallahi inasanta kai ni kake fadima haka maxa fitaemin daga gida da alama talauci baxai barka ba natsiyaci kawai.

Yaya lpy kuwa naga kafita cike da farin ciki kadawo duk rai abace yadan kalleta kafin ya share kwallar data kawo masa subhanallahi yaya kuka kuma nan yafada mata abinda ya faru ga mamakinta mai makon taxama mai marin ciki sai tasamu kanta cikin kunxi kayi hakuri yaya ai kasan halinsa da ake fade yasaba cima talakawa murunci kuma in matarka ce dole sai ka aureta kudi kuma insha Allahu sai ka bashi mamaki kudi bashine jin dadi ba kaji yayana yadago yakalleta nasani kanwata nagode da kokarinki na karfafan gwiwa.

Kanwata
Na.F.A.Ya’u

Yaya dan Allah ka cire damuwa aranka komai dan hakuri ne yai dariya Fadya kenan abinda ke damuna gidan nasu an hanani xuwa innaje mai gadi ya hanani shiga a sch dinna naje yafi akirga van ganinta kawarta tace an gahanata xuwa se bayan bikinta yanxu sauran sati uku.

Tai shiru kafin tace inada dabara lokacin dabaka da lpy ba tareda kakarta taxo ba yace to kasamu kasa taje can gidan kakar naga alamar tanasanta da yawa tasauyama baban ra'ayi ehto kin kawo shawara but yanxufa nace miki banida damar samunta wayoyintama an kwace kabari xanje gidan nasu nagode sosai kanwata Allah yabarmu tare tai dariya baka bukatar godiya yaya ta mike ta fice.

 Sun gaisa da mum din fara kafin fadya tace momy fara tananan kuwa eh tana dakinta ta nuno mata dakin ta mike tai dakin tana kwance afadonta ta rufe idanta da alamu ba bacci takeba tadan tavata ta bude idon ganinta yasa ta mike xaune kanwarmu kece tai dariya en nice da fara'arta tace lalelale taje ta kawo mata ruwa da lemo tace gambo ta kawo mata abinci bayan tadan xaunane take fada mata abin da yakawota tai shiru kumafa kin kawo shawara suka dan taba hira kafin fadya ta mike bara na wuce har farfajiya ta rakota.

Dad dan Allah inasan xuwa gidan inna kaka ok kibari xan kaiki inyaso inxan dawo naxo na tafi dake to dady.

Amarya da yawo aishiyasa nace bara na kawota da kaina yagaida innar yabar gidan ya fita Fara ta fada kan innar tana kuka yanxu inna da ranki xa'amin auran doke kekinsan Farhan nakeso tasa salati yanxu daman yaronnan karya yamun yace ku kuka shirya kanku keda salim din kodaya inna wallahi banasansa kibarni dashi dagashi har faiz din ta ce daukon wayata kiramin faiz din ta kira tana shiga ta mika mata kaxo kaida salim inasan ganinku ta kashe kiramin shi baban naki ta kirashi shima tace yaxo yanxunnan.

Cikinku ba wanda akaima auran dole dan haka itama zabinta xa'a bata kuma duk wanda yakibin abinda nace van yafe masa ma salim ne yace haba inna karki mantafa ni jikanki ne wancan vare ne tai dariya ban mantaba shi aure ba ruwansa da alaka kubata abinda takeso faiz ya mike gami da yarfe hannu daman nasani kintsaneni gashi abin har yakai ga kan dana bai jira amsarsuba ya fice yabar gidan shida salim din dady ya daka mata tsawa sai kitashi mu tafiko kaga masur karka takura mata na fada maka.

Tunda kin nunan ni ban isa dakeba harkinasan hadani da uwata kisani zan aura miki wanda kikeso ta buga tsalle alhamdulillah dakata ai ban gama anman inasan kisa aranki daga randa kika fita gidannan matsayin matar wannan yaron kisa aranki kin fita kenan karkiyi tunanin ke daya na haifa yadda kika nuna ni ba ubanki bane to wallahi kema ba yata bace dad dan Allah kayi hakuri bana nufin batamaka rai vata rai na nawa ai kin ban mamaki ace duk gatan danai miki ki kasamun alfarma daya danataba naima agurinki.

   Kanwata
    Na.F.A.Ya'u

Tunda suka shiga motar take kuka tanai masa sannu yayinda hankalinsa baima jikinsa gaba daya ya gama fita daga hayyacinsa suna xuwa akai emergency da su likitocine wajan su hudu akansa sunfi minti goma sha biyar kafin daya daga cikinsu ya fito yana share gumi sukai kansa suna tambayar lpy yai office inda baba yabi bayansa.

Gaskiya yaronku na cikin matsala domin kodarsa duk biyun sun lalace yana bukatae adasa masa wata subhanallahi yanxu doctor yaxamuyi ehto xuwa xakuyi a gwaggwadaku in ansamu mai lpy acira anman sai kun hanxarta dan yanacikin hatsari bara naje nan ya fita su umma sukayo gurin suna tambayar lpy ya fada musu fara da tun fitowarsu fadya tai mata waya yanxu ta fito tai office din doctor ni aciri tawa yace muje sai an gwada.

Angwada saidai itama tatan vatada cikakken lpy duk ta wanda aka gwada bataiba ta fadya ce kawai normal dan haka tata xa’a cira abba yasanya hannu akan takaddun yayinda fadya taja Aisha gefe Aisha inaji araina baxan tashiba duda kuwa doctors sunce ba matsala ki min wata alfarma inajinki samo min biro da takarda tasamo suka xagaya baya taxauna tai rubutu gashi wannan nasanki kinada rukon amana karki sauya ayau kitai maka saikin ga gawata xaki baima yaya farhan bance ki karantaba inna fito lpy xaki bani abata ta rungumeta ki rike alkawari nasani xaki tashi kedai vari taja hannunta suka dawo ta shiga dakin aikin tana daga musu hannu.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8Next page

Leave a Reply

Back to top button