KAUYEN 'YAR KADDE COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

KAUYEN ‘YAR KADDE COMPLETE HAUSA NOVEL

“Muje na nuna miki tun kafin ki cinye ni da wad’an nan idanuwan naki” murmushi nayi ba tare da na bar kallon nasa ba.

“Muje nace, time na tafiya, gashi ko wanka banyi ba, kuma inason na le’ka asibiti da safen nan”.

“To muje” nace ina dawo wa kusa dashi, girgiza kai yayi tare da d’aga ‘kafan sa yafara tafiya, nima na fara.

Yana d’aga ‘kafa d’aya nima haka, waiga gefen daman sa da nake yayi yace “wai ni kakan kine baby?”.

” Kamar ya?” gaba yayi ba tare da ya bani ansa ba, ni kuma na bisa, kitchen d’in ya nuna min zai juya nace “mai za’a dafa maka?”.

” Abinda zaki iya ci, don da ganin wannan shafaffen cikin babu komai a cikin sa”.

“Hmmm, my heart kenan” kallo na yayi yana mai jin matsanancin farin cikin sunan da nakira sa dashi.

“Ina son ki” yace yana mai lumshe idanu wan sa, “nima haka” ba tare da na bud’e baki ba, lab’bana ne kawai suka motsa, kallon su yayi tare da jin wani irin yanayi.

Barin wurin yayi ni kuma nayi cikin kitchen d’in, tunani na fara “shin mai zan masa?” nai shiru ina nazari.

Ban iya kunna gas ba sai na kuna stove, d’aura ruwan zafi nayi, kafin yayi zafi na fere doya, yana tausa na juye, soya doya nayi da ‘kwai.

Ina gama wa na fito, lokacin shima ya fito a lokacin ya fito ‘kamshin shi ya cika ko ina na palon, ganin kallon da nake masa kamar wa wuya yasa ya saki wani had’ad’d’an murmushi.

Mayar masa nima nayi tare da nufo sa, cikin shagwa’ba nace lokacin da na iso gaban sa “gaskiya doctor kamin wayau” zaro ido da ya zama kamar al’adanshi yayi tare da min magana da ido, “name?”.

Turo baki nayi tare da cewa “kasani ma break fast bayan nayi wanka, kana ‘kamshi niko sai wari nake” nace ina shinshina jiki na.

Matsowa gab dani yayi yana murmushi tare da cewa “muji” yana kamo hannu na, tare da rankwafawa ya kai hancin sa a wuya na, yace “hunnnn, ‘kamshi, kinji ‘kamshin dakike kuwa baby?”.

Fincike wa nayi don nasan tsokana ta kawai yake, murmushin gefen baki yayi tare da cewa ” da gaske ‘kamshi kike, zo na’kara ji”.

Bibbiga ‘kafa na farayi a ‘kasa ina cewa “Allah ban wani ‘kamshi ni na sani, kuma ni wanaka zan sakeyi yanzu na fesa turaren ka”.

“Zo HAYATI, zo kinji” banza dashi nayi, shi kuma yana tsoron Allah yana tsoron abinda Joy za tayi.

Ko kallon sa banyi ba nayi hanyan d’akin sa “oh my god” yace tare da d’aura hannu aka, niko ina shiga nayi toilet d’in sa, wani irin ‘kamshi bayin yake, tu’bewa nayi na d’aura towel d’in sa, na fito da uniform d’ina a hannu palon na fito.

Jin motsina yayi tunani ko na fasa ne ya d’ago da kai don kallo na.

Da sauri ya kauda kai, murmushi nayi tare da mamakin sa, sai kace yaga wani abun tsoro.

“Ga uniform d’ina ka ninke min kafin na fito, yadda ba zai ya mutse ba” nace tare da ajewa kusa dashi.

Bai ce komai ba har nabar wurin, kuma ko sake kallo na baiyi ba.

Wanka na nake cikin nishad’i, da ruwa mai ‘kamshi, “nima yau zan zama ‘yar gayu” nace ina sakin murmushi.

Bayan na fito na ‘kwala masa kira don ba mirror bansan inda kayan ‘kamshin sa suke ba.

Yanaji ya kasa magana, don yana nan inda ta bar sa, a daskare yake don ko uniform d’in da tace ya nunke mata baiyi ba.

Sake ‘kwala masa kira nayi amma shiru babu ansa, don haka sai na fito tunani na ko ya fita ne, ina zuwa na gansa zaune inda na bar sa.

Cikin shagwa’ba na nufo sa, banyi wata wata ba na d’ane cinyan sa, d’ago da runannun idanuwan sa yayi tare da cewa cikin ma wuyacin hali.

Da sanyin murya “please kibar abinda kike, Allah addinin mu yahana haka, haramun ne abinda muke aika tawa, hakan zai kamu ga aika ta mummunan abu, ki bari kinji”.

” Ki adana su zuwa bayan auren mu” yace yana kauda kai, kallon sa nayi da mamaki, nace “meye abinda nake mara kyau?” shiru yayi bai ce komai ba.

Hannaye na nasa tare da juyo da fuskan sa, ina kallon cikin idon sa nace “meye laifin abinda nayi?, kaban ansa”.

Saka hannu sa yayi tare da zame hannu wana yace ” addinin mu ya haramta ke’bance war mu haka”.

‘Dage gira nayi tare da girgiza kai “to d’an d’agani please, kije kuma kisa kaya mu karya zaku makara fah, kalli” yace yana mai nuna min agogo.

Takwasa saura minti goma na gani, mi’kewa nayi tare da cewa “ina ka aje kayan ‘kamshin ka?” bai ce komai ba ya mi’ke, d’akin ya nufa nabi bayan sa.

Muna shiga ya mi’ka min wani jaka “gashi, please kiyi sauri muje” yace tare da fita bayan na ansa.

“My heart d’an kawo min uniform d’in” zuwa yayi bakin ‘kofa ba tare da ya d’aga labulen d’akin ba .

Yace “gashi” turo hannu sa kawai yayi, murmushi nayi ina mamakin wani irin addinine haka mai shegen ta kura?.

Saka kaya na nayi na fashe jikina da turarukan sa masu shegen ‘kamshi, amma abin takaici banji ‘kamshin kamar na jikin sa ba.

Fito wa nayi, kallon sa nayi tare da kallon break fast d’in bai ko ta’ba ba.

“Ya bakaci ba?” kallon na yayi tare da cewa “ke nake jira” ya tsina fuska nayi tare da cewa “kaci kawai na ‘koshi”.

Mi’kewa yayi ba tare da yace dani komai ba ya nufi ‘kofa, da mamaki na kira sunan sa.

Waigo wa yayi yana kallo na ba tare da ya ansa ba, ” bakaci ba “.

” Na ‘koshi ne nima” murmushi nayi tare da nufan inda yake tsaye, kamo hannu sa nayi .

Bai ce dani komai ba har na zaunar dashi, bud’e wa nayi tare da zuba wa a plat, na had’a masa tea duka nace “muci” tare da saka hannu.

Bai ce komai ba ya faraci, kad’an yaci yace ya ‘koshi tare da mi’kewa.

Nima na mi’ke, kallo na yayi tare da cewa “ci inajiran ki waje” .

“Na ‘koshi, kin tabbata? uhum”.

” Shikenan muje 8:10am har yayi ‘kila ‘kawan ki ta tafi” fita yayi na bisa a baya, ina fita ya saka key ya rufe ‘kofan.

Mukayo waje ya rufe gidan shima, rana ya fara fito wa mutane nata kai da dawo wa.

“Shiga kira ta” bace komai ba na nufi cikin gidan nasu.

Mama na tarar a tsakar gidan, gaishe ta nayi itako tana kallo na da mamaki a fuskan ta bata ansa min gaisuwan ba.

“Baku tafi ba?” tace, cewan ta haka ne ya ganar dani cewa Aisha ta tafi, don haka sai nai tsuru tsuru na kasa bata ansan tambayan ta.

“Joy dake nake fah” sosa ‘keya na farayi sai na dake tare da cewa “mantuwa nayi shine na dawo, to na duba d’akin mu ban gani ba shine na tuna jiya tazo ta ‘kar’ba, shine nazo duba wa”.

Shiru tana kallo na kamar bata yadda da abinda nace ba, sai daga baya tace ” me kenan?”.

“Litafin wata ‘yar class d’in mu, shiga ki duba, amma ai da kun dawo tare ta barki ke d’aya kin dawo”.

” Amma a mashin kika dawo ko?” tace ina gab da shiga d’akin.

“Uhum” nace kawai tare da sa kai.

Kallon d’akin na tsayayi kawai har kusan minti biyar sannan na fito, ganin bata tsakar gidan na saki ajiyan zuciya tare da falfalawa da gudu.

Ina fita na bud’e mota na fad’a cikin tare da sauke numfashi.

“Lafia?, ina ‘kawar taki?” yace yana kallo na.

Ban sa ansa ba nace “muje kawai” bai wani matsa ba ya tada mota muka bar wurin.

Mun fara nisa sannan nace “Aisha fa ta tafi, kuma nasan ta shiga gidan mu nema na”.

“Yayi, kinga mai himma kenan” turo baki nayi tare da cewa “naji ni ban da himma”.

” A’a ni bance ba” banza dashi nayi shima bai matsa ba ya cigaba da tafiyan sa.

Yana parking na bud’e ‘kofa zan fita, “ansa” yace .

Waigo wa nayi tare da kallon hannu sa, “ki ansa nace” hannu a dun’kule.

“Me zan ansa?” nace ina le’ka sa’kon hannu ‘kara dam’kewa yayi tare da sa d’aya hannu sa ya janyoni tare da kar’be jaka ta yasa min tare da saki na.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button