KHADIJATUL IMAAN COMPLETE HAUSA NOVEL

KHADIJATUL IMAAN COMPLETE HAUSA NOVEL

Sa’adiya uzaifa tayi nacin son YARIMA kamar ta mutu amma bata samu nasara ba,sun had’u ne a nan malaysia,amma ita har yanxu bata gama karatun ta ba,wannan Kenan…

Ta kalli IMAAN tace”amarya sannu ya gida,ya amarci?,da k’yar IMAAN ta amsa mata saboda wani irin Abu taji ya tokare mata k’irji,hhh zakiyi bayani,

Ko da suka dawo gida sam IMAAN bata da walwala ko kad’an,YARIMA har ya gane ta yace”baby na yadai me ya faru ne?”,ba komai kawai tace dashi,murmushi yayi dan ya gane kishi ne takeyi…

A wajen kwanciya bacci ma juya mishi baya tayi sai da YARIMA yace”baby na juyo babu kyau juya ma miji baya fa kinji ki daina”,banza tayi dashi sai da ya sake cewa”to shikenan bari inyi abinda baki son”,ai ba shiri ta juyo..

Had’a fuskar su yayi yace”me yake damunki uhm fad’a min”,nace ba komai ai,yace”no ai da ba haka muka fita ba,ko dan kinga sa’adiya ne”,ai fa sai ta fashe da kuka tana cewa”ba ita bace take min wani irin kallo,ni me na mata”,murmushi yayi yace”kai baby na a yaushe kuma,kedai kice kishi kikeyi kawai”,b’ata fuska tayi tace”a a ni ba kishi nakeyi ba”,to menene uhm fad’a min “,love u so much baby na,ke fa kina son à?”, 6oye fuskar ta tayi a kan k’irjinshi saboda wutar d’akin a kunne take,hannu yasa ya kashe wutar,yace”to na kashe wutar fad’a min u love me?”, shiru tayi can kuma tace”ni bacci nakeji”,yace”sai fa kin fad’a min ko kuma inyi tafiyata in barki a nan”,tace”ka bari to sai gobe yanxu bacci nakeji”,hmm baby na akwai wayo to naji Allah ya kaimu….ni kuma nace Ameen!!!

Da asuba bayan sunyi sallah, IMAAN ta d’auki biro da takadda ta rubuta YARIMA I LOVE U,ta aje kusan shi ta juya baya gami da rufe fuska????

D’auka yayi ya karanta,cikin murna ya juyo da ita yace”baby na da gaske kike?” ko dai mafarki nake”,d’aga mishi kai tayi har yanxu fuskar a rufe,ya sake cewa are u sûre?nan ma kai ta sake d’agawa,jayota yayi ya fara kai mata kiss yana cewa zamuyi célébration na wannan ranar da Allah ya nuna min,wutar d’akin ya kashe…

YARIMA har ya fara kauce hanya ya tuna da dokar doctor,haushi yaji,amma ko ba komai ya dan samu nutsuwa…

Cikin IMAAN yanxu yakai wata d’aya har da kwana hud’u,YARIMA ya kira doctor yace”friend ya baka ce min komai ba ni fa a matse nake yanxu ai is OK ina iya kusantar ta KO?”,cikin zolaya doctor yace mishi”no da saura bari tayi wata biyu mana”,what YARIMA ya fad’a yace”so kake ka kasheni ko?”

Dariya yayi yace”wasa nake maka har kana min ihu a kunne”,hhhhh YARIMA ma dariyar yayi yace”to in mun gama cin amarcin mu zan kawo madam gidan ka”,ok to sai kunzo,aci amarci lafiya kuma a bi a hankali inji doctor,yana gama fad’ar haka ya kashe wayar….

    *'YAR MUTAN KAZAY CE????*

ANTY MAIMOUNATH????

+22969164943

????????????????????????
KHADIJATUL
IMAAN
????????????????????????

     *STORY*

               *&*

     *WRITTEN BY*:✍????



     *ANTY MAIMOUNATH*????

WANNAN SHAFI SADAUKARWA NE GA DUK MAI SUNA KHADIJAH
FAN’S NA KHADIJATUL IMAAN NAGA SAQONNINKU NA GODE DA ADDU’A,ALLAH YA BAR K’AUNA.TNX

BONNE GUÉRISON MON BÉBÉ ABDUL, UMMU BASHEER PREND SOIN DE NOTRE CHÉRI ABDUL

DEDICATED TO:
AYMAN
TIJJANI(TJ)
G.BOY

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Page2⃣3⃣~2⃣4⃣

YARIMA kuwa yana ajiye wayar ya fice sayen kaza,a cewar shi zai angonce yau,kuma zaiyi célébration na cewar yanxu IMAAN ta fara son shi,duk Wanda ya ga YARIMA yasan yana cikin farin ciki,da ya dawo har IMAAN tayi wanka tayi sallar ta,shima wankan ya shiga yazo ya gabatar da sallah…sun ci sun sha,tamkar dai yau ne first night nasu haka YARIMA yake ji,sai wani b’arin jiki yake,hmm pitié IMAAN…. ita dai binshi take da kallo,ko da sukaje gadon baccin su,kallon shi tayi tace”me ya sameka a idanun ka ko ciwo ne suke?”,murmushi yayi ya jayota jikinshi yace”a,a wani abu sukeso da fatan zasu samu a wajenki”,kallon rashin fahimta ta mishi,ido d’aya ya kashe mata yace”baki gane ba ko?”,zo in fad’a miki a kunnenki,rad’a ya fara mata yace”baby na kinsan dai na jima rabon da in kusance ki ko,so please ban da raki kinji ko,kiyi hak’uri har un samu nutsuwa”,IMAAN dai baki ya mutu sai kuma fad’uwar gaba kamar yau ne farkon had’uwar ta dashi….

Kwantar da ita yayi a hankali zatayi magana ya hanata sakamakon had’e bakinsu da yayi waje d’aya,hannu ya tura cikin yaloluwar rigar ta Wanda ita dan babu duk d’aya,wasa ya fara da dukiyar fulanin ta Wanda suke a tsaye bare yanxu da take da yaron ciki sun d’an ciko suna tsone idon mai kallo,hhh ba ni ba fa,YARIMA dai,ko ya kikace UMMU BASHEER????

Wasa fa yayi nisa inda YARIMA ya fara sakin layi yana neman hanyar shiga,a hankali yake bi da ita dan kar tayi mishi raki saboda IMAAN akwai son jiki, amma duk da haka sai da ta d’an yi k’ara baki ya d’ora kan kunnen ta yace”sorry baby na,hmm su YARIMA an kamu maganar ma da k’yar take fita,hhhh….yau dai ya huce haushin shi na tsawon lokacin da ya d’auka bai kusance ta ba,dan sai da yayi second round da asuba ba ma haka har sai da ta fara mishi kukan shagwa6a tana cewa ita fa ta gaji ya bar ta haka in ba so yake ya kashe ta ba,hmm….

Bayan sunyi sallah asuba komawa sukayi suka kwanta dan ramuwar baccin da basu samu ba jiya….

Sai wajen 11 na safe suka tashi shima knocking ne ya tashe su YARIMA ya tashi ya saka doguwar riga irin ta sallah,kakana ma yanada irin ta????

Fita yayi yaje ya bud’e k’ofar,MUSTAPHA ya gani tsaye ya muk’a mishi hannu suka gaisa,MUSTAPHA yace”kai mutumena ba dai sai yanxu kuka tashi ba”,dariya YARIMA yayi yace”wallahi kai ne ma ka tashe mu”,shima d’in dariya yayi yace”oh sorry friend,daman zamu fita shop ne nace bari in fad’a muku karku ji mu shiru”,YARIMA yace”shop shirin tafiya ne kukeyi Kenan?”,yace”eh wlhy ina so zuwa jibi insha Allah mu koma gida kasan aiki muka baro kuma Hutun mu ya k’are daga ni har madam”,yace”ok sai kun dawo Kenan bye”,MUSTAPHA ma yace”bye”,YARIMA ya koma ciki,ko da ya shiga d’aki har IMAAN ta shi wanka,murmushi yayi,yazo bakin toilet d’in yace”baby na shine baki jirani mun shiga wankan tare ba?”,shiru tayi,ya saké cewa”ko in shigo muyi?da Sauri tace”a,a kar ka shigo na gama yanxu zan fito,dariya yayi yace”sai fa na shigo kar ma ki rok’eni ah to,ai ba shiri ta fito daga ita sai tawul,karo sukayi inda yasa hannu ya taro ta,ta fad’a jikinshi,kallon kallo sukeyi ita ta fara kauda kanta tana mutsuniyar ya saketa,amma ina Wace ita ai bazata iya amsar kanta a hannunshi ba,hannu yasa ya juyo ta wani iri yake jinshi saboda k’irjinta yana gogar nashi,sai da ya tsotse bakin ta son ranshi sannan ya kyaleta ya shige toilet din,ta jima a tsaye saboda kasalar da ta sauko mata….bayan sun shirya sunyi break suna falo a zaune suna kallo yake ce mata”su UMMU AYMANA sun fita MUSTAPHA ne ya zo ya fad’a min shine ma yake knocking d’azu,kallon shi tayi tace”ina sukaje?”,shop suka je ya bata amsa,sannan ya jayota ya rungume yace”baby na Allah yayi miki albarka,ya saqa miki da gidan aljannah firdaussi,hhh su YARIMA fa an shiga sambatu kuma,hmm…d’agowa tayi ta kalleshi yace”eh mana hak’ik’a kin kashe min k’ishirwar da ta jima tana damuna,babyna inaso ki rink’a hak’uri dani,ki zamo mai juriya a kullum saboda zuwa yanxu nasan kin gane cewa yariman ki yana daga cikin maza masu yawan sha’awak”,IMAAN dai shiru tayi ta kyale ita duk kunya ta isheta ga cikinta yana ciwo”,YARIMA ya d’ago ta yace”yadai baby na wani abu kikeji ne?”,tace”daman cikina yake d’an yi min ciwo da kuma mara ta”,a zabure yace”what?tun yaushe?,ya jero mata tambayoyi ta ce”bayan munyi sallah asuba ne na fara ji”,ido ya zaro yace”shine baki fad’a min ba da ban tambayeki ba shikenan bazaki fad’a ba ko,sai dai in abu yayi tsanani ki sani gaba kina kuka ko”,tashi maza muje asibiti wajen doctor”,tace”a,a ba sai munje ba zan warke ya kusa dainawa,hmm IMAAN na gane ki wato tsoron allura ko,amma fa nima ina d’an tsoro kad’an…

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26Next page

Leave a Reply

Back to top button