KUSKURE Complete Hausa Novel

Zee zee t d’auko wata Leda t mikama Aishatu tace gashi asama baby ,kafin kowa yayi mgn nawara tace laaa harda wani Abu Haka ,Dan ALLAH ? Zee zee tace b komai ai Haneef din mune ,sanan Aishatu tace angode aunty zainab m tace angode nawara kawo Mata Abinci , nawara t tafi kawo Mata ….
Bayan nawara t ajiye Mata abincin tace ,gashi harda su drinks ,sai g hassana d ussaina sun shigo ,suna cewa matar Yaya Ina boy Haneef ne nifa Adinga kularmin d yaro kinsan bana Sanya d jini na ,nawara tace ai kema kinada hakin kula d abinka tunda Kinga ita zataji d kanta ….
Sai ussaina tace ayya hakane fa wlh mussaman d akamata C’s dinan damma matar Akwai kwari mace ce Mai dauriya wazece Aiki akayi ,d irin wasu matan ne suna Nan suna langwabewa kamar taliya Yar hausa wlh,akasa dariya , ussaina tace ,Dan ko bana mantawa d haihuwar Noor mumynta ko jikaken tsumma Albarka , ni nadinga komai wlh …. Nawarace tace to mude y zama past test ,Kar ace munacin Naman wata ,kawai kawata kinsan jarumace ko acikin jarumai tunda kinsan d haka shikenan ,kema kiyi koyi d irin nata jarumtar b irin nasu langwai ,ba d NAWAL din take Amman t saya Kar ace sunayi ta ita ….
Duk Abun Nan d akeyi zee zee na sauraren su tana nadewa a brain d’inta ….
Sun Jima suna Hira cikin d’akin gabanta ,sai aunty zainab CE lura d yadda take kare musu kalo dama Kuma Bata gama yadda d ita ba ,Dan Haka tace zainaba kice Abincin Mana? Sai tayi murmushi tace toh ,sai Aishatu tace ko kunya takeji , ai ko aunty zainab sai tace to nawara d’auki Mata kayan Abincin ki kaimata parlour ki Mata masauki Mai kyau ,Aiko Jin za’a koreta zata denajin lbr gashi ko hoto 1 Bata d’auka b ,sai tace aa ku barni anan ma zanci ai , aunty zainab tace aa kunyarmu kikeji nawara maza Kai Mata ,Aiko nawara tayi saurin bin umarnin aunty zainab t d’auki Tran Abinci takai Mata ,aunty zainab tace gashican t iaimiki Dan ALLAH kici Abincin ,ganin anmata karfakarfa haka t dauko Jakarta t koma parlour badan taso ba ….
Tana fita ,aunty zainab t rakata d harara , Aishatu tagani tace aunty lpy? Aunty zainab tace banni d wanan matar, Kuma ku dinga iya bakin ku ,kusan Wanda zaku dinga yadda dashi ,duk sai sukayi wani iri ,aunty zainab ce tace karsu sa komai aransu ,sucigaba d abinda yake gaban su …..
Zeee zeee Tana parlour ,tanata zare Ido Tana ganin zance yanata barinta, sai d’aukan gulma d takeyi n bishasha d Abinci d akeyi d su Naman kaza ,Abun kamar kudin banza ….
Suko sunata shagali n su hankaki kwance , Aishatu inta leko parlour takan yima ‘yan parlour magana harda zee zee ,sai t Mata yake tace b komai ,zee zee taje hanun mama ta dinga yima Haneef hoto har t dinga hadawa coverage n bishasha d Abinci d akeyi d jama’ar sunan d irin cikar d akayi. …..
Ganin t takura g kowa sabgarsa yake gashi Bata d abokin Hira t takura Tana tsoron Kar asirinta y tonu ,sai t yi Shirin fita kawai Dan t huta d takurar d tasa kanta ….
Har daki t biyo Aishatu akan zata Mata sallama , ganin Irin kayan sunan d aka Tara Mata ,ga Aishatu n canja Kaya ,sai t dinga d’aukan kayan a hoto komai d komai d’auka take ,can tace ita zata wuce yara sun dawo dg school ,sai Aishatu tace laaaa nagode kinyi kokari ai ,tare suka fito tacema nawara taba zainaba Naman ciki ,shine nawara t zubo Mata a Leda d su snacks ,tanata godiya Tana leka manyan raguna d sa har ta faki idon su t kafta musu hoto , Aishatu tace y sunan me gidan naki ko shi dadyn Noor din ze ganeshi ? Zee zeee aka Kama inda inda can akace , Yusuf zakice Mai ,ko baban su huzaifa, Aishatu tace to nagode ,sanan ta tafi tanata murnar Sha dakyar d tayi ita zeee zeeee …..
Aunty zainab hankalinta be kwanta b seda taga tabar gidan , sanan Tama Aishatu magana tace su dinga kula d kowa dai ,suka cigaba d shagalin su …..
Har yamma tayi wasu sun warwatse ma ,wasu suna Nan ,ansha shagali sosai ,Inna d mama d aunty Mai d’inki Bayan magriba suka tafi gida , Aishatu cike d kewan su kamar karsu tafi ,t cikasu d kayan ci d kayan cikin d aka soya ….
Aunty baraba ma d Yan uwan Ammy sai dare suka tafi , Aishatu t cikasu d kayan ci d na kayan cikin d aka soya …..
Gidan y rage daga aunty zainab sai heedaya sai su twins sai nawara sai ,su twins nata sauri Kar yayan su y dawo y gansu Basu tafi ba ,Dan Haka mazajen su na cewa suzo su tafi ? Sukace eh Dan Haka d wuri suka tafi ,sukama kowa sallama ,suna tafiya safwan din y dawo kuwa ,sai d y tmby su kuwa akace sun tafi tun d’azu yace ALLAH y temakesu d ransu y baci …..
SAFWAN y dinga tsokanar nawara tabar angon karni a gida ,tace shi ai y zama Mai kamshi yanzu shine angon karni …..
Aishatu dai yau ba Wanda yace taje ga mijinta hankalinta ne y Bata Haka ,har daki taje tamai sannu d zuwa t tayashi cire Kaya ,t kawo Mai Abinci d soyayen kayan ciki ,yanaci Yana Santi ,Yana cewa Bata wahalar da kanta bade ko? Tace eh amman duk tagaji ,yace Bari y gama y Mata tausa tace to ,cikin nishad’i d Jin Dadi suka gama nunama junan su k’auna Abin su …..
Bayan nawara ta tafi ,suffaya ma ta tafi ,sai su kadai ….
Aunty zainab d heedaya kwanan gajiya sukayi ,Aiki Kuma saima gobe Dan sai anyi hayar masu Aiki ,dama tuni antanadesu …..
Washe gari ,tun wuri masu aikin Naman suka sasara yadda Mata zasuji dadin aikata shi ,dagabaya aunty zainab d heedaya d iya kakar heedaya suna kalon komai suna nuna musu yadda zasuyi ,har yamma suna Abu daya safwan ma wuni yayi agida Yana renon Haneef din shi ,Noor ma tanata jin son kanin ta ….
Sai dare komai y Kamala n suyan nama ,aka biyasu kudin Aiki d ladan kamshi ,suka tafi iya agidan t kwana …
Washe gari heedaya suka koma gidan Ammy Amman heedaya zata dinga lekosu lokaci zuwa lokaci ….
Gida daga aunty zainab sai Noor sai Amaryar karni d angon karni ……
Safwan so d shakuwa nakara shigarshi t ahalin nashi ,an raba Naman kowa ankaimai duk Wanda y Dace akaima d yajin dadawa ,Dan Haka sai su kadai a gida ,ganin sun Sami Nutsuwa d kwanciyar hankali safwan y tsaida ranar d za’ayi magana Akan Rayuwar mlm mamman hafeez agidan Inna Dan Haka ze Kai su Aishatu can Noor Kuma zai kaita gidan Ammy ….
Bayan kwana biyu y sanarma Inna d Aishatu d mlm mamman hafeez ,zasu hadu gidan Inna Akwai maganar d zasuyi , Aishatu nata murna duk d Bata tsananta binciken irin mgn d za’ayi ba ….
D dadare safwan y Kira Aishatu y dinga Mata magana t fahimta yasanar Mata ,Akwai mafarkin d take tunanin tayi to b mafarki bane gaske ne ,yanzu so yake t samu nustsuwa zasuje za’a warware komai d izinin ALLAH ,Dan Haka tamai Alk’awarin nutsuwarta d rashin tada hankalinta Akan Abun ,dake y San kanta y gama shawo Kan abunsa ,t Mai Alk’awarin t samu Nutsuwa ,Amman fa d Abin t kwana cikin ranta burinta mafarkin ta y zama gaskia ,sanan t Kara tozali d wanan Wanda take ganin shine mahaifinta kamar yadda shima yake kirari ….
Washe gari d wuri aunty zainab t samusu ruwan wanka Tama Haneef t kaima Aishatu nata taje tayi t fito ta tsala kwaliya Cikin wani tsadaden boyel d yaji Aiki d safwan y musu anko d ita ,ganin shi tasa shima y sauya shigarsa ,aunty zainab nata musu dariya ,itama tasaka sabon kayanta suka nunguma sai gidan inna…..
Bayan safwan y sauke su ,sai ya tafi y dauko mlm mamman hafeez Dan kawo shi gidan Inna ,gidan Inna yasha gyara yayi fes g kanshi d yaketa tashi , aunty zainab Nanda Nan t hau girki a risho …..