KUSKURE Complete Hausa Novel

Hatta su Ammy d su twins d yaransu d su suffaya su nawara duk sun yadda d canjawan NAWAL Babu wani Abu tsakanin su yanzu ,anyi bikin hidaya kawar su Indo ,sunsha shagali anmata goma ta Arziki gidan Ammy har safwan ma d Aishatu dake iya Mai aikin gidan Ammy Bata d karfi hidaya anata murna lpy aka kaita d’akinta d angon ta aka baro su ….
Su Noor d haneef anata girma ,safwan nata tatalin iyalin sa bashi d case d kowa ga harkokin shi sai bunkasa yakeyi ,har yake tsakanar Aishatu d nawal ko y raba musu gida?
Har suna had’a Baki wajen cewa aa abarsu tare yafimusu ,safwan y dinga dariya Suma sukasa dariya d suka Gane tsokanar su yake ,suka cigaba d Hira cikin Raha da Wasa d dariya abinsu hankali kwance ..
Abban Aishatu ganin Aishatu Bata samu matsala d nawal ba hankalin shi y Kara kwanciya ,aunty zainab ta samu ciki tun Tana b’oyewar har ya bayyana kanshi cikin ,lokacin haihuwar ta tayi ta haifo d’anta Mai Kama d baban shi ustaz Aiko kusan Babu Wanda yakai Aishatu murna d farinciki yau ga k’anin ta a duniya Ashe tanada rabon samun k’ani ,Abban ta har mamaki ta dinga bashi kamar wata k’aramar yarinya ,aunty zainab d’in ma ta dinga tsokanar Tana cemata ta girma fa ,ita dai tace Bata girma ba Haka akayi suna yaro yaci sunan bbn shi Hafiz Ana Kiran shi da affan ,inna d su Ammy d su mmn nawara d su nawara su twins har heedaya Amarya d su aunty Mai dinki d su maman NAWAL kowa sai d yaje sunan affan.
kusan kulin sai Aishatu ta Kira waya Taji lpy bro Affan ko aturo Mata d hoton shi ,Haka takeji d kaninta tilo a duniya bbn ma yaji dad’in samuwar wani d’an a duniya Ashe yanada rabo k’ara godema Allah ,
Gidan safwan dai normal hankalin shi kwance na matan shi ma kwance Dan Haka Rayuwa take tafiya yadda yadace , Aishatu d nawal tare zaka gansu ko awajen biki ko suna sunki bada k’ofan d za’a shiga tsakanin su Sam….
*Tamatbihamdullahi*????????????????
“`Anan Na Kawo Karshen Novel D’ina Mai Suna KUSKURE Abin da Nayi Dai Dai ALLAH Ya Bani Ladan Abin Da Nayi KUSKURE Nima ALLAH Ya Yafe Min Ba Yin Kaina Bane Ajizancin D’an Adam Ne“`
_ALLAH Yama iyayen mu Albarka yasa Sugama da Duniya Lpy wad’anda Suka Rigamu gidan Gaskiya ALLAH Yaji Kansu d gafara D Rahama , ALLAH y kyautata namu zuwan , ALLAH ya shirya mana zuriya Shirin islama ALLAH y kare Mana su daga sharrin fitintunun zamani_????????????????????????
[ad_2]