KUSKURE Complete Hausa Novel

NAWAL CE dinga rarashin mama har t samu t saki ranta ,NAWAL nason mama kusan soyayyar uwa d ‘yarta ,kawai taki ba mama hadinkai ne su dinga shawarta duk matsalar su subiyu ba tare d Abban ta yaji ba ,mama t samu matsala nee NAWAL tun Tana karama ta hanyar so d sangarta d Abba y dinga nunama NAWAL tun Tana karama har girman t har NAWAL take ganin shawara ko neman mafita a wajen Abban ta ta duk matsalar d taxo Mai dashi tafi samun gamsashiyar amsa tunda zebarta taci karenta Babu babaka sabanin mama d seta tsage gaskia t Kuma nuna Mata karya a bayane t Kuma Bata umarnin bin gaskia hakan yasa take ganin kamar Abba y fi son farincikin ta a shirme irin na NAWAL fa …….
**********
Indo an gama had’a Mata kekenta har t Fara Aiki d shi a gidan Aunty Tana fahimtar yadda ake koya Mata komai ,kafarta t Fara sabawa d takun keken sosai …
Bayan t koma gida taje gidan su nawara Dan sanar d ita t Fara zuwa koyon dinki jaka d takalmin ….
Bayan sunsha Hira nawara nata tayata murna d nuna Mata t dage t koya yadda y kamata…
Har nawara take cema indo wai tayi mafarkin ankusa bikin Indo Amman batasan waye mijin ba biki Kuma ganga ganga cikin kankanin lokaci akayiomai aka gama tanata murna …
Indo t gama sauraron nawara t turo baki tace ke wlh bakya rabo d shirmenki ke wani lokacin kamar Yar gulma kamar Yar baiwa Kuma na rasa wane zan ajiye ki ?
Da dai wanan shirmen naki ze faru sai n barki a ‘yar baiwa ,Amman Ina! d kamar wuya gurguwa d Auren nesa wlh ko kusa ko Alama Ni saurayin d kikace n Fara kulawa m n canja shawara Sena gama koyon dinki na ,Aure cikin kankanin lokaci sekace Yar tsakuwa ko wata Irin hamshakiyar mace wacce Auren dama kawai take jira tab !
Nawara tayi dariya tace ,Allah y tabatar Miki Dani Yar baiwar ce ,
Indo tace b Amin b wlh kedai d bikin ki y saura wata 5 Allah y nuna Mana musha shagalin..
Nawara tace wlh wata kilama kiga kinrigani Auren ,Abun Allah Kuma shi yake tsara komai a tsare …
Indo tace ,Allah baze amsa ba ,bakinki dai Allah y shirye shi …
Ni Kinga tafiyata d surutun ki Mara tushe bare makama ..
Sukayi sallama t tafi ..
“SAFWAN yayi bacci sosai ya tashi yayi sallah ,Ammy Tana sawa azo a duba shi har zuwa tashin shi yanzu ,ranar Yaya ma ko fita beyi ba ,tare sukaci Abinci d k’anin nashi ,ba wani sosai SAFWAN yaci ba koshi, y ma su Noor salama Yana cewa Ammy y tafi ….
Ammy Ce Tama Yaya maga d y karbi makulin motan safwan din y driving Dinshi har gida kafin y barshi …
Safwan kalon su kawai yayi y saki wani murmushi gano Ammy Tana zargin ko ba a hayacin shi yake ba …
Bayan Yaya y Kai safwan gida safwan y dinga tuna Mai d afa neman Mai Auren Indo su d’auki maganar sa mahimmanci kafin faruwar wani Abu …
Yaya y dinga jujuya maganar faruwar wani Abu Kuma ,wane Abu kenan?
Y tmby kanin nasa Amman yaki cewa komai ,shi kwnshi baya iya controlling kanin nashi y zamar Mai maiwuyar shi’ani yau …
Seda yaya y tabatar safwan y sausautawa ranshi daga damuwa sanan y bar gidan ,Koda ze fita seda safwan y sake Mai mgn afa neman Mai Auren kafin faruwar wani Abu ….
Yaya fita yayi Yana cemai baridai zamu tatauna ….
Koda Yaya y koma y sanar m d Ammy furucin safwan ,itama t dinga tmby akan meyake nufi d faruwar wani Abu ,
Yaya y nuna mata indai b matsala ama safwan yadda yakeso na tsorata d bacin ran d y shiga yau dinan Dan n rasa gane kansa ,
Ammy tace kaje gida gobe in kunzo sekuji shawarar d muka yanke d Alhajin ku …
Yaya y Mata sallama y tafi gida …
*Maman shaheed*????
[1/6, 8:15 PM] Maman Shaheed: ???? *WRITING*????
BY
“`MAMAN SHAHEED“`
*KUSKURE* ????????♀_????????
( _’yar Aiki Ko Matar Gida_)
_shafi n talatin d biyar_
“Safwan kwana yayi Yana tufka d warwara akan Al’amarin burinshi y zeyi y Aure Indo duk d ba digon sonta a cikin ranshi ,Kuma yanada dama iya sakin t d’aga baya ta samu Wanda takeso ta aura daya baya shi Kuma y sake auran wata matan d yayi yanaso fiye d son d Yama NAWAL…
Da wanan tunanin y kwana ..
Bayan Alhj su safwan y dawo gida ,Ammy taje sukayi magana t fahimta dashi akan safwan ….
Alhj yace a rabu dashi ,shirme yake wane irin zama zeyi d ita d betaba cewa Yana sonta ba ko so yake y yi Auren huce takaici d y’arinyar mutane ?
Kudubafa d kyau ,duk Wanda y goyi baya akayi abinan in ya cutar d Yar mutane t rashin Bata kulawar d namiji zeba mace yasani Yana da kamisho na Alhaki….
Ammy tace ,toh Alhj mude nemi zabin Allah ,wai baka Lura d tashin hankali d matsanaicin bacin ran d y shiga bane ,karfa wankin hula ya kaimu dare ,muduba matsar sa da Abun da yake bukata matuk’ar beci karo da addini ba Alhj..
Alhj y numfasa yace abari zasuyi mgn d safwan din …..
*******
Indo ta dage tanata koyon d’inkin ta hankalin ta kwance …
Inna nata samata Albarka d nuna Mata d rage tayikokari ….
Indo na gidan koyan dinki wani yaro y shigo gidan Ammy lnna wai Ana Kiran lndo a waje ….
Inna tace waye? Yaron yace shima besanshi ba ,da har zata Aika a Kira indon sai t tuna wani Abu tace aje ace Bata Nan ….
Saurayin badan ranshi yaso ba y bar kofar gidan su Indon,
Bayan Indo tadawo cin Abinci Inna take Gaya Mata ,indo t turo baki …
Inna t dinga Mata nasiha Akan ba wakanci tsakanin ta dlwane namiji ,rabuwa lpy shi yafi komai sauki ,duk taji tayi naam d gargad’in Inna t Mata Alk’awarin kiyayewa Kuma …
Adaren ranar inna tayi mafarkin kwatankwacin irin na nawara wai Anzo neman Auren Indo Anzo neman ma wani Wanda tsabar son d yakema indon har yakai shi g kwanciya a Asibiti Rai a hannun Allah ,akazo Ana magiya d rokon Inna d Indo su Amince Kar saurayin y mutu ,Indo kuwa juyin duniya Taki Amincewa ganin Taki yadda yasa Inna ma Bata amince ba kardai rashin Amincewar yasa saurayin rasa ransa iyayen sa suka shiga mumunan tashin hankali d kuka dangin saurayin suka dora Alhakin hakan Akan Indo da Inna ,ba indo ba har Inna sai d sukaji da sun San ze mutu d sun amince d bukatar su ,sunata kuka Suma …
Koda Inna t farka cikin kid’ima ta farka Tana tariyo Abin d y faru a mafarkin tanata addu’a…..
Koda t tashi d safe Abun Yana ranta t umarci Indo t siyo Mata kosai tayima yara kanana sadaka ..
Ta zaunar d Indo takebata lbr mafarkin d tayi ,Saida jikin indon yayi sanyi taji kamar gaske ,gani zata shiga damuwa Inna t sanar mata mafarki ai ba gaskia bane d kwantar da hankalin ta Addu’a d sadaka suna kawar d abubuwa da dama ,indon tace to Inna ALLAH ya amsa ,Inna tace Ammin ……
“Bayan safwan y tashi d safe y shirya a dadafe Dan ji yake jikin shi wani iri ,y tafi office ganin jiya beje ba …
Koda yaje gani daya zakamai ka gano damuwa a tare dashi ….
Amman in abokanen aikin shi sun tmby shi sai yace musu lpy ,gashi y kasa aikakomai ….
Can zuwa wani lokaci zazzab’i y Fara Shirin rufe shi ….
NAWAL dai t rarashe mama ,mama t cire komai aranta gudun Kar hawan jinin t y tashi ayanzu ma tanajin ta wani iri so take tace NAWAL tamata bp haushin d suka kunsa Mata yasa take ganin gwanda t tafi asibiti Likita y dubata sosai ….
Dan haka t shirya t Kira Abban NAWAL tace zataje dubiya asibi yace Mata adawo lpy Tama NAWAL sallama zataje dubiya asibi ..
Duk yadda NAWAL taso su tafi tare mama Taki , haka Dole NAWAL t hakura ,mama tayi tafiyarta likitanta t dubata tsaf y Bata magani y umarceta d ta rage damuwar d ke cunkushe a ranta tamai Alk’awarin insha Allah zatayi iya kokarin ta ,y Bata sati biyu t dawo asake gwada ta ..