HAUSA NOVELKUWWA DA KUWWA Complete Hausa Novel

KUWWA DA KUWWA Complete Hausa Novel

Tana shiga tasameshi tsaye a gaban k’aton madubin da yaci ado da ruwan diamond ya cire rigarshi yana duba wasu abubuwa masu kama da k’ayoyi a bayanshi yana ganinta yayi saurin takowa ya iso wajen da take yana zuwa yarik’o hannunta yazaunar da ita saman gado sannan yatallabo fuskarta yana kallo yace ya ke kyakkyawar matata shin ko zani iya sanin dalilin shiga damuwarki?

K’ok’arin ‘boye damuwarta tayi sannan tace Ya kai mijina inason kasan cewa na shiga damuwa ne ba dan komai ba sai dan ina ji a raina kamar akwai abinda zai faru da rayuwata.

Wata irin razanannar k’ara sarki yasaki tare da saurin latsa zoben da yake a babban yatsan hannunshi nan wani abu me kama da computer yabayyana a gabanshi, rufe idanunshi yayi yafara karanto wasu d’alasimai da ita kanta Gimbiya Nuwaira batasan abinda yake cewa ba saida yad’au lokaci me tsawo yana karantowa sannan yabud’e idanunshi yasafkesu akan ‘yar computer sihirinshi ajiyar zuciya yasafke tare da kallon Gimbiya Nuwairah yayi murmushi sannan yace kikwantar da hankalinki babu abinda zai faru da rayuwarki dan akwatin tsafina bai gwada min komai ba bazan ta’ba bari wani abu yafaru da ke ba ya ke matata.

Murmushi tayi ganin yadda hankalin mijin nata yatashi yasa tace hakane mijina nima kawai raina ne yaban haka ammah nasan babu abinda zai faru da ni, saidai ko da ma wani abun ya faru da rayuwata ina so kakular min da Najla sosai dan kaine kad’ai wanda zata cigaba da samun gata a wajen….
Katseta yayi yace haba Nuwaira kidaina cewa haka zamu cigaba da rayuwa tare sannan Najla zata samu kulawa daga dukkan ‘bangarorin namu guda biyu.

K’wallah ce tacika mata idanu tace nasan haka mune kad’ai farin cikinta ina bak’in ciki akan wannan rayuwar da mutanen garin nan suke ta k’abilancin da ke tsakanin Fararen mayu da bak’ak’en mayu wanda ta dalilin hakan Saraunya Wailah da Najma suke nisantar da kansu daga garemu shin idan rai ya yi halinshi ya Najla zatayi da kewa babu wanda zai tallafa mata.
Ajiyar zuciya yasafke yace Nuwairah kidaina irin wannan maganar dan tana d’aga min hankali sosai babu abinda zai faru da mu sannan ita Najla bana da matsala da ita na san cewa zata kula da kanta ko da ace bamu raye.

Murmushi Sarauniya Nuwairah tayi sannan taciro wani zoben gold me kyau sosai daga dogon yatsan hannunta rik’o hannunshi tayi tasaka mashi zoben a tafin hannu sannan tarufe hannun tana murmushi tace ga wannan ka ajiyeshi ina da burin ganin Najla ta mallakeshi kamar yadda nima namallaka bana so ya’bace a wajena saisa nabaka shi ka ajiye wajenka.

Jin abinda tace yasa hankalin Sarki Nawar yakwanta nan ya amshi zoben yace zan ajiyeshi kamar yadda kika buk’ata har zuwa ranar da zaki nemeshi daga wajena.

Murmushi tasakar mashi tare da cewa nagode Ranka yadad’e,,, tana fad’in haka tamik’e tsaye tare da d’an rissinawa k’asa alamun girmamawa.

Jinjina kai yayi nan tajuya tafita tabar d’akin da kallo yabita yana murmushi har saida tafita sannan yamaida idanunshi akan zoben yana kallonshi,,,,, tunowa yayi wani lokaci da mahaifinshi Sarki Zabban zai mutu shi yamallaka mashi shi yace ya adanashi kar yasaki yabari zoben yasalwanta daga wajenshi har sai lokacin da yayi aure ya auri d’aya daga cikin jinsu na fararen mayu sannan zai mallaka mata shi wannan dalilin ne yasa yamallaka shi ga Gimbiya Nuwairah matarshi ta biyu, ajiyar zuciya yasafke a fili yace minene dalilin Nuwairah na bani wannan zoben tace inba Najla bayan ita namallaka ma shi? Ko dai akwai abinda yake shirin faruwa da ita?
Saurin girgiza kai yayi yace a’a babu abinda zai faru da ita saidai idan itace take tunanin hakan…..

Mik’ewa yayi yaje yayi ma zoben kyakkyawan ajiya sannan yasaka kayanshi na sarauta yafita yanufi fada.

 

da dare ko da Sarauniya Nuwairah taje apartment d’in d’iyarta ganin duk ranar bataga giccinta ba duk hidimar da ake banda ita koda tasan Gimbiya Najla bata cika son shiga cikin taron jama’a ba ta fi so take’be kanta.

tana zuwa d’akinta tasameta kwance baccinta kawai take abun ya bata mamaki sosai nan ta ajiye kayan da takawo mata saman gadon sannan tashiga tadata ahankali tabud’e idanunta takalleta,  murmushi tasakar mata tace ‘yata ya kamata kitashi kishirya kinga lokacin tafiyar mu wajen shagalin bikkin ya kusa ga kaya nan na kawo maki wanda nasa aka k’era maki da lu’u lu’u dan ina so shigarki tafi ta kowa kamar yadda kika zarce kowa wajen kyau.
Murmushi Gimbiya Nalja tayi sannan tace toh ummah.

Idanu Gimbiya Nuwairaj tazuba ma kyakkyawar ‘yar tata tana kallo daidai lokacin hawaye suka gangaro daga idanun sarauniya nan hankalin Najla yatashi sosai tayi saurin tashi zaune tare da rik’o hannun mahaifiyartata tace Ummana lafiya kike hawaye ina fata dai ba wani ne ya’bata maki a garin nan ba?
Girgiza kai tayi tare da goge hawayen ta tace ko d’aya ya ke ‘yata ina jine a jikina kamar akwai abinda zai faru da rayuwata a wannan ranar.

Wata k’ara Najla tasaki wadda tasa saida d’akin ya amsa cikin d’aga murya tace babu abinda ya isa yasameki ummana ni kariya ce a gareki duk fad’in garin nan duk wanda yanemi yata’ba min ke sai na shayar da karnuka na jininshi zan iya ja dakowa a kanki.

Murmushi Sarauniya tasaki tare da shafa kan d’iyar tata cikin jin dad’in kalamanta tace babu abinda zai sameni na sani d’iyata kawai dai a jikina ne nakejin haka.
Ajiyar zuciya gimbiya Najla tasafke tace hakane ummana kidaina zubar da hawayenki aduk lokacin da kikayi tunanin wani abu zai sameki kiyi tunanin ina nan ni kariya ce agareki.

Murmushi Sarauniya tayi tana kallon d’iyartata cike da jin tausayinta chan sai tamik’e tace bari inje in ida shiri kitabbatar kin shirya kafin lokacin tafiyar.
Murmushi Najla tayi tace toh Ummana kar kidamu zan shirya saidai muhad’e chan kar kujirani.

Sarauniya tace toh shikenan Gimbiyata duk yadda kikeso haka za’ayi zan sanar ma mahaifinki abinda kikace.

Murmushi Najla tayi a karo na biyu, sarauniya har ta juya zata fita sai kuma tasake juyowa takalli Najla sannan tajuya tafita.

 

Najla na ganin ta fita tad’auko kayan da mahaifiyartata takawo mata takalla tayi murmushi tabbas ta san mahaifiyarta ta yi namijin k’ok’ari wajen tanadar mata kayan,  murmushi tasaki ahankali tace ina k’aunarki sosai Ummana nan ta ajiye kayan takoma takwanta tacigaba da baccinta.

 

Wajen k’arfe sha biyun dare dajin Sanzar da suke kira bak’in daji cika yayi mak’il da fararen mayu kowa kagani ya ci ado cikin kaya mafi kyau da tsada a tsakiyar dajin suka kunna wuta wadda saboda cinta saida tahaske dajin su dukansu zagayeta sukayi wasu na bin bayan wasu nan babban malaminsu na fararen mayu Boka Ambar yasa aka yanke k’atuwar shanuwa aka tsiyaye jininta a cikin wani k’aton bokitin tsafi sannan aka cillata cikin wutar wata irin k’ara wutar tayi nan tak’ara tururuwa daidai lokacin Sarki Nawar da Saraujiya Nuwairah suka tunkaro wajen nan gabad’aya jama’ar fararen mayu suka duk’a sukayi sujjada banda Boka Ambar da yaruntse idanunshi yana karanta wasu d’alasimai takowa sukayi suka iso wajen da yake nan suka tsaya gefenshi tare da runtse idanunsu har lokacin sauran jama’a basu d’ago daga sujjadar da sukayi ba, ahankali Boka Ambar yabud’e idanunshi yad’auki wannan bokiti me cike da jinin shanuwa da yatsafe nan yamatsa wajen da sarki Nawar yake tsaye ya ajiye bokin bud’e idanu Sarki Nnwar yayi yasaka hannuwanshi cikin jinin ya yi kusan minti ukku sannan yafiddo hannuwan yashafa jinin a saman kanshi sannan yajuyo yashafa ma Sarauniya Nuwaira ita a gashinta, bud’e idanunta tayi ahankali tasakar mashi murmushi, maida mata martani yayi yace ina Najla ya akayi har wannan lokacin bata zo ba?
Saurin juyawa Gimbiya Nuwairah tayi takalli bayanta sannan tace bansan dalili ba bansan me yasa har yanzu bata zo ba munyi da ita zata zo ta ce kar mu jirata ita kad’ai zata zo.
Jinjina kai Sarki Nawar yayi yace ammah kuma har yanzu shuru meyasa Najla zatayi mana haka.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button