NOVELSUncategorized

QANIN MIJI 9

IYAYE KU JI TSORON ALLAH, ‘YA’YANKU SUN FARA KAWO MIN QARARKU, KUKAN HANASU AURE AKAN KARATUN GABA DA SECONDRY WAI SAI SUN GAMA, TOH KU JI WANNAN BA KARANTARWAR ANNABI

BA NE, A MATSAYINKU NA IYAYE, KAFIN KU TURASU CAN KU ZAUNA DA SU KUCE WACCE KINA SON AURENE KAFIN KARATU KO SAI KIN GAMA?, BA KUMA KU DA KANKU BA, KU NEMI WACCE KUKA SAN YARINYAR BA ZA TA JI NAUYINTA BA, MISALI QAWA TA GARI, TA TAMBAYO MUKU ITA, IDAN AURE TAKE SO KU AURAR DA ITA, DOMIN YADDA KUMA KUKE JIN SHA’AWA A JIKINKU ITA MA HAKA TAKE JI, WATAQIL NATA MA YA FI NAKU SABODA YANAYIN HALITTA DA KUMA KASANCEWARTA MATASHIYA, IN YASO TANA GIDANTA MA SAI KU D’AUKI NAUYIN KARATUN NATA HANKALI KWANCE, AMMA SUN NUNA MIN DALILIN DA YASA SUKE FINGERING KUNA HANASU AURE KUMA SHA’AWARSU TANA ADDABARSU, TOH WALLAHI KE UWA KAR KI YARDA ‘YARKI TA JAWO ASHIK JIKINTA AKAN BOKO, QARSHE TA GAMA KARATUN ASHIK YA AURETA YA KORA MATA DUKKAN MAZAJEN AURE, SAI KUZO KE JUGUM ITA TAGUMI, ZAKI YARDA DA HAKAN UWA?

9
“mene ne fareedah….”?
Cikin muryar kuka tana girgiza masa kai tace
“fa’eez…”
Muryarsa na rawa yace
“bai kamata mu damu da Fa’eez ba fareedah, domin shi ma ba mune damuwarsa ba, fareedah duk halin da muka shiga shi ya jefa mu a ciki, ya hanani aure yayin da ke kuma ya jibgeki a gida ba tare da yana baki hakkinki ba, fareedah ina da qarfin sha’awa, na kasa jurewa, ba zan iya ba kamar yadda kema na san kin zo maqura, ya kamata mu haɗu mu tausaya wa kanmune fareedah, mu ceto rayuwarmu daga hallaka, domin zai yi wuya wannan stage ɗin da muke bai cutar da lafiyarmu ba, matuqar ba mu kawo mafita wa junanmu ba, ina me tabbatar miki, shima fa’eez ba haka kawai yake riqe da sha’awarsa ba, yana can yana holewarsa ne mu kuma ya takuramu ya hana mu jin daɗin rayuwarmu, ki min izini fareedah in kawo mana mafita, na miki alqawari ina tare da ke cikin kowani hali, kin amince”?
Yace tare da cigaba da sarrafa wasu sassan jikinta, idanunta a rufe ta gyaɗa masa kai, shiko ya samu dama tuni ya fara kunce wa fareedah kai da abubuwan da tunda suke da fa’eez bai taɓa kwatanta mata su ba duk da su.e burinta, sune mafarkanta da hasashenta da fatanta a rayuwar aurenta, sai gashi  hafeez qanin mijinta shi ya zage yana aikata mata hakan, har da ma abubuwan da ba ta taɓa sani da su ba, hakan ya taimaka matuqa gurin ficewar fareedah a hayyacinta tare da rura wuta irinta sheɗan, cikin qanqanin lokaci ta sallama kanta wa hafeez tare da gagarumar gudumawa daga gareta, hafeez kuma abin nema ya samu dan haka duk wata hikimarsa da abubuwan da yake gani a BF sai da kwancesu ga fareedah a ranar
Kamar yadda fa’eez haɗuwarsu da Tina ya ji bai taɓa jin daɗin kwanciya da mace kamarta ba, haka lamarin yake gurin fareedah, tunda take da fa’eez bai taɓa bata lokaci ya kore mata dukanin sha’awarta tare da kawo mata nutsuwa ba kamar hafeez, ta kai maqura gurin gamsuwa da hafeez a shimfiɗarsa, sun ɗau lokaci suma sosai suna tare, ita fareedah sai a yau ɗin ne ma ta san ashe tana da qarfin sha’awar da za ta iya nisan zango a shimfiɗa, a yaune ta san asalin haqiqanin kalmar satisfaction a shimfiɗa ita kam, toh balle hafeez da yau ne gamuwar farko
*
Ruqunqume suke da juna a yanzu da hankalinsu da nutsuwarsu suka dawo jikinsu, tamkar hafeez zai mayar da fareedah ciki haka ya kanannaɗeta, ita ma kuwa tayi luf a jikinsa sosai tamkar shi ne mijin na asalin, dan ita ma ta gaji sosai saboda rashin sabo
Maimakon fareedah da ta yi kuka a farkon lamarin, yanzu hafeez ne ya fashe da kuka yana sake ruqunqume fareedah a jikinsa
Da qyar ta iya magana a hankali tace “hafeez…”
Sake ruqunqumeta yayi yana kuka tare da zuba mata kisses a kunne
Hakan yasa ta sake narkewa ita ma a jikinsa tayi shiru, sai can yace
“fareedah ki ceci rayuwata dan Allah, ki taimakeni, ki agajeni kar ki saka rayuwata cikin garari”
“me ya faru hafeez…”?
“fareedah, tun farko ba sha’awarki na fara yi ba, qaunace da soyayyarki fal zuciyata, fareedah tun zuwanki gidan nan ba da daɗewa ba na kamu da qaunarki, sai nayi ta yakiceshi saboda ba yadda zan yi in sameki, amma abun ya gagara, har ta kaini da kishin yayana a kanki amma a ɓoye, akwai ranar da sai da nayi kuka cikin dare akan kishinki fareedah, damuwar da kika ga ina yi akanki ba wai kawai ta qanin miji bace, ta soyayyace da qauna, wallahi ina sƙnki fareedah, ina qaunarki, a dalilinki mata suka daina burgeni, kiyi tunani, tunda kike kin taɓa jin ina hira da budurwa, fareedah duk ke kika hanasu daraja a idanuna, ba wai umurnin faeez bane kawai, shiyasa a baya na ɗaga hankalina akan ya bani damar aure ko zan samu sauqi cikin qaunarki fareedah, amma na san duk wacce na auro gangan jikina kawai zata samu ban da zuciyata domin tana gareki”
Shiru yayi kaɗan sannan ya cigaba da cewa “wannan abinda ya faru yanzu a tsakaninmu, ya sake zubamin dafin qaunarki cikin zuciyata fareedah, sannan a gefe guda ina jin zuciyata tamkar tayi bindiga saboda kishin fa’eez, nayi baqin ciki da takaicin kowacce kusanta da faeez ya miki a baya, na yi baqin ciki fareedah”
yana kaiwa nan ya sake fashewa da kuka sosai, hankalin fareedah ya tashi jin waɗannan furuci daga bakin hafeez, ga wani masifaffen tausayinsa da ya ratsa mata sassan jiki, cikin mutuwan jiki ta fara shafa kansa tana hawaye, da qyar ta iya buɗe baki ta fara magana
“hafeez dan Allah kayi shiru, bana son wannan kukan”
A zabure ya ɗago da fuskarshi ya haɗa da tata yana rage sautin kukansa yace
“Fareedah, idan fa’eez ya dawo ki ce ya sakeki, kar ki sake amincewa da shi ko na qanqanin lokaci, na miki alqawari duk rigimar da za a yi sai kin dawo matata, wallahi tunda har yayi saken da na kusanceki toh ba zan taɓa haqura da ke ba, kece daidai ɗina, ni ina da lokacinki fareedah, zan nemo halak ɗina in riqeki kuma ba zan taɓa nisantar shimfiɗarki ba a kowani irin yanayi, sai na tabbatar babu abinda na rageki da shi a cikin zamanmu, ba labari bane fareedah da gaske nake yi, gaskiyar zancene daga zuciyata”
Shiru fareedah tayi ba amsa sai kuka ita ma ta fashe da shi domin hankalinta ya tashi da yadda ta ga hafeez ya rikice mata, ta san akwai rigima a gaba
A kiɗime ya fara rarrashinta duk da shi ɗin ma ba kukan ya daina ba tare da wiping tears ɗin kan fuskarta da tongue ɗinshi cikin salon da ba shiri fareedah tai shiru sannan ya cigaba da cewa
“pls fareeda ki amince ki kasance tare da ni, nine nake miki son gaskiya, ni ne zan iya samar miki da farinciki, ni ne zan iya gamsar miki da sha’awarki ba faeez ba, ki tausaya min, ki tausaya min fareedah”
Ganin ya sake rikice mata yasa ta fara rarrashinsa amma har cikin ranta qaunar faeez ce ta mata katutu saidai tabbas ta san babu wata ranar da qaunar take mata
“ina tare da kai hafeez, ka kwantar da hankalinka, zan yi yadda ka ce”
“da gaske tareedah”? Yace yana kallon cikin idanunta, lumshe idanu kawai tayi ta gyaɗa masa kai amma maganar ba har cikin zuciyarta take ba
Sake rikice mata yayi da sambatun soyayya da qauna yana yaba mata ta kowanne ɓangare, abin da ba ta samu daga faeez ɗinta kenan
Haukar sambatun da yake yi ya daina ya raɗa mata wata magana a kunne, wacce ta sanyata ture bakinshi daga kunnenta ta rufe fuska, amma ga dukkan alamu maganar ta daketa, kalmomin my swanpy sun tsaya mata a rai, kunyar da ya ga ta jine yasa shi cikin rashin tsoron Allah ya ɗauketa kamar baby yana dariya ya shige da ita cikin toilet ɗinsa, ya haɗa musu ruwan wanka yana ta riritata da tarairayata da furta mata kalaman soyayya dan kalmomin I love you my swanpy har ta gaji da jinsu, haka suka yi wanka tare kamar miji da mata yana ta janta da wasanni ita ma tana biye masa domin sheɗan yana ta raya mata cewa yanzu haka gaskiyar hafeez ne, shi ma faeez ɗin yana can yana jin daɗin rayuwarsa, haka suka kammala suka fito a tare yayin da yake ɗauke da ita.
Ba ruwana wallahi, na ga duk sunan da na sanya a cikin book ɗin na soyayya sai anyi ta tambayata ma’anarshi, toh swanpy dai idan ka kuskura a matsayinka na saurayi ka je gidan su budurwa ka kirata da swanpy, toh wallahi idan babanta tsohon malamin makarantane zai ci ubanka da kyau har sai ya ji dalili kiran ‘yarsa da swanpy????, ni ko maryam ba ruwana dan ban aikeka ba, sunan na mazajen aurene
**
Lulluɓeta yayi da blanket ɗinsa sannan ya sumbaceta a kan hanci yace “my swanpy ki yi bacci ki huta, minti ishirin kawai nake so ki ban yanzu zan fita in dawo”
Murmushi kawai ta masa tana binsa da kallo, hancinta ya ɗan ja ya haɗe fuska cikin wasa yace “saura kuma in dawo in samu kin fita sarkin aiki”
Dariya tayi ta ja blanket ɗin za ta rufe fuskarta yayi saurin riqewa yana dariya yace “I realy love you my Reedah”
Kallon juna kawai suka yi ba tare da tace komai ba ya tashi ya fara shiryawa a gabanta, saidai kafin ya kammala shirin har bacci ya kwasheta, cikin baqaqen yadi masu kauri ya shirya, komai ma baqine har hular kansa sannan ya juyo ya tako inda take, ganin tayi bacci sai ya qura ma fuskarta idanu, ajiyar zuciya ya sauke ya manna mata kiss tare da sake faɗin ina sonki swanpy, sannan ya shafa fuskar ya tashi ya ɗebi wayarsa da key ya fice daga ɗakin tare da rufo qofar ya sanya key ɗin a aljihu, ɓangaren mai aikin gidan ya nufa ya sameta tana kwance sai game take yi a waya abinta, yoh ba aiki, fuskarsa ya haɗe yace “ki tashi kiyi duk wani aikin da kika san fareedah tana yi a gidan nan kafin in dawo, kar kice zaki mata abinci dan ba za ta ci ba” yana gama faɗin haka ya juya yayi ficewarsa ya bar mata qamshi Oud collection ɗinsa a gurin sai tashi yake yi
An fara kiraye kirayen sallar azahar ya dawo gidan, hannayensa ɗauke da ledoji iri iri, a hankali ya turo qofar ya shigo bayan ya buɗeta, har yanzu bacci ya ga take yi, dan haka ya ajiye kayan  a kusa da gadon ya shige toilet gudu gudu ya ɗauro alola ya fice masallaci cikin kuzarinsa sosai
masu bin littafin Jininane inshaa Allah da yamma zan sake next page, na gode
ISLAM IS MY IDENTITY

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button