KWARATA RETURN COMPLETE

KWARATA RETURN COMPLETE

  Dalili kuwa shine :• duk gero sunanshi gero. Yayin da aka sarrafashi zai tashi daga sunan gero ya koma wani suna na daban , misali , za'a sarrafashi zai zama fura , kunun kanwa , kunun tsamiya , wainar gero , tuwon gero , gumba , farin kunu , kunun zaƙi ke har danbun gero na gani kuma naci shi a bakina.... Amma duk miye silar zamar da duk wannan abubuwan dana lissafo ? Gero ne ! Shine duk aka sarrafa yayi duk abubuwan nan dana faɗa , tou haka take ga duk namijin daya baro gidanshi. Wasu mazajen zasu fito ne cikin soyayya da rashin jin daɗin sunyi nisa da ilayinsu , me yasa sukejin haka ? Kula , soyayya kissa kisisina kwarkwasa iya fira mai daɗi uwa uba kuma kindai gane ba........? Matansu zasu ɗauke musu tunani su kasance sunayin kewarsu da wa'ancan abubuwan dana lissafo har suje su dawo zuciyarsu da ƙwalwarsu baya barinsu su kalli wasu matan , ko kuma suyi tunanin kowa sai nasu , yana kasuwa ko office amma lissafinshi yana gida , burinshi ya tashi daga kasuwa ya koma dan kasancewa da shi wannan farin cikin dai. Dan haka zasu koma gida cikin farin ciki a taresu da soyayya kuma........ Kinga namiji ne ba , amma hikimar mace ta juyashi yasa ya zama wani daban..

 Wasu mazan kuma zasu fito gidansu da ɓacin rai. Su fito kasuwa ko wata ma'aikata , idan ogane a wurin aikin abu ƙalilan zakayi ya ɗaga murya , ɓacin ran gida ya shafeka wanda kai bakaji baka kuma gani ba , idan ɗan sanda ko alƙali kila ma idan makuyi sa'a ba yace ku duk ɗin ayi gidan yari daku , tou a fara faɗo mishi karatun da shi kanshi baida lokacin da zai tsaya sauraronku ko yayi lokacin fitar da haƙƙin mai gaskiya  dan haka zaice da mai ƙarar da wanda ake ƙarar duk a haɗaku a kaiku magarƙama. Shima mace ce ta juya mishi lissafi da kuma tunani , mazan haka suke sukan canja ne daga horon da matayensu suka basu , mai tunani ya zama lurasi , lusarin kuma ya zama jarumi. Ya danganta dai da horon da aka bashi daga gida , Sharifa anshe goruba a hannun kuturu ba abu mai wuya bane , tunda har ya ƙetaro iyakar matarshi ya fito sai ki bari matan waje su duma mishi wa² ? Shikenan ke kin haƙuri ? Ki bar musu ? Ke bakya da buƙata ? Sharifa tace ina da... Tou Yusra Jiddah da wata banzar yarinya dana manta sunanta duk kiyi ƙoƙari ki rabasu da Dikko , {{ banzar yarinya da ita Mai gilashi ke nufi itace Sharifa , }} taci gaba da cewa idan kin shirya kin kuma shirya ɗaukar huɗubata bisimillah , tashi sharifa tayi ta matsa kusa da Mai gilas kunneta ta kama tayi mata raɗa bayan sunyi alƙawari da kuma yarjejeniyar amana. Sharifa ta yadda ta kuma ansa , ta yadda da huɗubar *MAI GLASS...* abinda ta faɗa mata zamuji shi idan taje wurin Dikko ne. Dariya Mai gilashi tayi tana kallon Sharifa aka wani tafa , Mai gilas tace haka suke ai mazan iri ɗaya ne , kije ki jaraba. Wannan farashin da zakiyi tukuici sai buƙata ya biya.....

   Bugu:• bugun bala'e sukayi ma Amisty bayan sunyi nasarar cafke banza. Kuma dukan bawai irin na yara ba ko na susar jiki ba. Basu bigeta da wasa ba duka na tashin hankali sukayi mata , dukan da idan dai akayi ma mutum irinshi to sai mutuwa. Tafiya babu dawowa. Tunda sukaji zancen kuɗi sukaje wurin suka kafa tarko , duk wani da zai shiga ko fita a gaban idonsu. In banda wawanci da rashin lissafi kuɗin nan wai suna cikin motar Amisty idan taje wai inda zataje sai ta canja da kuɗin ƙasar tayi hidimominta. Haka sukayi mata duka kamar wanda ya tun kari fadar shugaban ƙasa rungume da bindiga.... Ita kuma bayan ta tabbatar kowa yaje ya kwanta ta sulale dan ta gudu saboda bata yadda kowa ya kwana ɗaki ɗaya da wani ba. Ƙarya tayi musu wai zatayi baƙo shine taga dare yayi zata wani ɓace abunta. Tafa ci ƙaniyarta yadda tunani baya zato. Suka ɗauke motar da kuɗin suka barta nan zube kamar asarar tsakar dare.

    Har gari ya waye ban samu nayi wani baccin kirki ba , haka kuma na kasa zuwa ɗakinshi , tsoro da fargaba kawai ke damu na , sai zantukan Ashiru dake tayimin luguden san zaman lafiya a zuciyata. Wannan dalili shine ya hanani san zuwa makaranta naji ni kamar wata mara lafiya. Ganin har 1 saura yasa na tafi ɗakinshi a tsorace , da sallama na shiga yana fitowa daga toilet ran nan nashi a haƙe fuskar nan tayi kalar ban tsoro dasa mutum ya shiga cikin yanayin firgicewa , ɗan rakuɓewa nayi cikin rawar murya nace barka da safiya , baimin magana ba bai kuma kalleni ba ya ɗauki wayoyinshi ya nufoni dan fita daga ɗakin..... Cike da tsoro na sake cewa Dikko ina kwana , ke........ Ya faɗa tare da yankamin wani irin firgitaccen mari saida na juya naje jikin bango dakel na haɗiye yawu lokaci guda zufa ya tsatstsafomin a fuska cikina ya juya yayi wani irin zakuɗa a tsorace na kalleshi , da ɓacin rai ya tambayeni wannan marin meya bayyana miki......? 

   Cikin kuka da marainiyar murya nace har yanzu jikinka da ƙwari , yace to ina nan a yadda nake , ban sauya ba ban kuma tashi a yadda kika sanni ba , dama idan baki manta ba na faɗa miki. Tou yauma na sake maimaitawa idan zaki kiyayi fushina tou ki kiyaye sai ki zauna lafiya , na warke ko ban samu sauƙi ba wannan bai shafeki ba saboda daga matar gida baki kau ba , ya nuna da hannunshi. Rayuwa da ƙaddara abokan juna ne , komai yana da ranar tashi daga aiki kama daga kifin gwangwani har zuwa mu "yan adam , kin gane ba ? Jeki........ Ya nunamin , tafi ya nunamin hanyar fita , ƙara yawan kukana nayi na taho daga inda nake na shige jikinshi ina cewa na bari Dikko na faɗa maganar ina ɗagowa dan kallon idonshi , sassauta murya yayi yana cewa bakijin magana , iskancin ki kullum gaba yakeyi , wai nine kike faɗa zaki zane ? Haba An mata....? Kayi haƙuri bazan ƙara ba , tou me nayi miki kika ɗaureni bayan ni ba mahaukaci ba. Ko abokin wasanki ne ni ? Ya tambayeni yana ɗagoni daga jikinshi , saida nayi shashshekar kuka nace bana so kana yawon dare ne , sai kuma ki ɗaureni ? Wannan wane irin hukuncin hauka ne ? Ai bana so kana fita na ƙarasa maganar ina komawa jikinshi. Murmushi yayi kaɗan a sakace yace An mata......... Ya ƙarasa maganar yana rumgumeni sosai. Cikin dariya yace wai wane mai bahaggon tunanin ne ya baki wannan shawarar ne ? Ɗagoni yayi kowa yana kallon idon kowa yace sai kawai tace miki idan kika ɗaureni zan daina fita ne ehem. Yayi maganar yana shan idanuwanshi. Suna shanyewa a hankali tare da murza su da salon duniyanci. A kasalance na koma na sake kwanciya , dariya yayi da murya mai kama zuciya ya ɗaukeni yaje ya kwantar dani saman gado , saida ya lulluɓeni ya sumbaceni yace jirani ina dawowa yanxu. Yayi maganar yana fita daga ɗakin........

 Bayan sati 1.

  Mijin Halimatu dai har yanzu baida lafiya. Jinya har ta kaisu asibiti zugar ƙawayenta kuma babu wanda ya bita sai Hadiza. Da ita ake yini akeyin komai sai dare suke dawowa gida ƙannen shi Abdul in maza suke kwana dashi. Da Halimatu ta tambayi sauran ƙawayenta me yasa basa zuwa cewa sukayi mazajensu basu yadda ba.....

  Har sati ya cinye Yazeed bai zo ba kuma bayayin waya da Jiddah. Shiru kuma har yanzu baiyi maganar turo magabatanshi ba tunda ya tafi waccan ranar sai yau yazo , duk an ɗaɗɗaure mishi jiki da tsumma an sagale hannunshi da igiya an sargafa igiyar a wuyanshi , wai Jiddah ta bashi mamaki shine dan ta tura mishi wata banzar 5million zata turo mishi ɓarayi suzo su kashe shi su ansar mata kuɗinta. Ai ba dole² yasa ta bashi ba , basai ta turo a kasheshi ba , tou ya basu kuɗin ta daina kiranshi kar yayi mata rashin mutunci , shi da ta ganshi duk cikar garin katsina babu ɗan iska kamarshi. Kuka Jidda ta farayi ita wallahi bata tura kowa ba , Yazeed yace ƙarya zaiyi mata ne ? Bafa a wata banzar miliyan biyar inta ya fara riƙe kuɗi ba. Me yasa a lokacin can da bai santa ba ba'aje an dakeshi ba ? Sai akan ita data bashi ne ? Tou ya fasa auren taje tayi da wani.

  Jiddah ta fara wallahi². Yazeed yace shi tama wani daina mishi kukan makirci yasan sharri irin na mata , haka taita bawa Yazeed haƙuri dakel ta shawo kanshi a yadda ya nuna kenan , saida ya sake buɗe fili akayi danbe Jiddah ta tura mishi miliyan biyu tace ta ba malamin ta anayin aiki , dakel Yazeed ya yadda ya anshi biyu , kuma ya tabbatar mata da kuɗin danbe ne ta biya , shi baya wani ra'ayi yana mata yayyafi ne dai dan ta rayu karta mutu. Tayi ma Dikko waya ya ƙaro wasu kuɗin......

 Dady kuwa ya bugu iya bugu a yadda yayi fentin gida da sabbin filawowi , Umar ɗan iska ne kuma baƙin mugu , da Dady yasa aka sauke fentina yace ya bada kuɗin ma'aikata zaiji da komai , ya anshi kuɗi masu yawan gaske a wurin Dady hada na toshiyar baki , Umar kuwa wajen gida kawai yasa aka gyara sauran fenti yaci kasuwa...

Duk satin nan Mai madubi bataje makaranta ba , naso zuwa gidanta Mai gida D ' K ya hanani , makaranta ma shine yake kaini yake kuma ɗaukoni , ga wayar ta idan an kira ba'a samu , sai na haƙura kawai.

   Har yanzu Dikko bai cire wayarshi a jirgi ba , kuma satin nan ya bigeshi bai fita , ko gidansu rabon da yaje tun ranar daya kwantar dani a gado yaje. Kuma ya taho da Papi saboda Nabeela ta tare gidanta. Banje ba , abinda yasa kuma saboda ciki shi yasa ya hanani zuwa.

 Sharifa da Aunty Bilki ganin ana neman a buga musu game over yasa ta samu Dady akan yayi ma Dikko magana yaje wurin Sharifa , ya kama waya ya rufe sati 1 kenan da kusan kwana 2 basa waya kuma basa haɗuwa. Tadaiyi "yar barikinta a gaban mijinta irin tamu ta mata , Dady kuma ya kira Dikko yace duk abinda yake yau yaje ya haɗu da Sharifa. Shi Dady gani yakeyi ita Aunty Bilki tafi Momy mutunci tunda tana san "yan uwanshi har take tunatar dashi akansu.

 Wani irin ihu Dady yayi tare da zubewa ƙasa somamme. Yayyen Hafsa suka rufa mata da duka wanda sune sukayi tsaye wurin nemota. Can abuja suka kamo "yar iska a wata asibiti wai tana jinyar Amisty tana so ta dawo taji ina kuɗi suke ? Shine suka tattaro su dukansu da Amisty da ita Hafsa..... Shine fa kawai ya wani some dan Hafsaf fa kawai ta tabbatar mishi da ɓarayi sun kwashe kuɗi , daga an faɗa mishi shine kawai zai wani zama mataccen bakin maƙabarta.........????

JAMILA MUSA…
[2/14, 12:12] ~M K: ⚜ BRILLIANT WRITERS ASSO ????
-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-

           *KWARATA RETURN...*
  _{{Kalu bale gareku matan aure}}_

Rubutawa…
JAMILA MUSA…

   *SAI NA AURI D ' K*

???? —— 8

 Saida sukayi mata lullusar fitar hayyaci sannan suka shafawa Dady ruwa ya dawo. Kamar ƙaramin yaro haka ya riƙa gumza , muuuuu , tutu² sai kace sabuwar mota ta haɗu da tsohon inji. Dady kayi haƙuri ka daina kuka , saida ya gama kallonsu sannan ya kalli Hafsa yace shin an kamo ɓarayin ne ? Suka ce a , a , luuuu Dady ya sake komawa suma. Haka sukayi ta dawo dashi daya dawo sai yace an kamosu ne ? Amma da ance masa a , a , sai ya sake somewa. A na ƙarshen ne ya wani babbanƙare ya riƙe yaƙi lanƙwasuwa baya gaba kuma yaƙi yayi baya kamar aljannun mata sun taso. Bayan ya tabbatar musu da cewa kada wanda ya sake dawo dashi idan har ba'a kamo ɓarayin nan ba. Babban ɗanshi yace Dady idan ba'a gansu ba fa ? A hankali ya maida kanshi ƙasa ya lumshe idanuwanshi cikin tashin hankali sannan yace ku barni kawai in mutu.....

  Cike da farin ciki Yazeed ya isa majalisarsu. A mota ya warware tsumman daya ɗaɗɗaure jikinshi yana dariyar ƙeta. Lallai Jiddah muguwar daƙiƙiya ce. Wato ita har ga Allah ma ta yadda anje anyi mishi dukan ? Ballagar mace uwarki tayi asarar aihuwa. Fita yayi daga cikin motar haka ya shiga cikin da'irar abokansu yaci gaba da fallasa Jiddah , wai wasu zawarun ballagazu ne. A kyauta yake shan iska babu wani damuwa. itama kanta a kame take kamar barden goyon daya yini baisha nono ba , da yaji gari yayi mishi zafi can yake tafiya yawon honey time. A can dai yake zubda ƙura ya dawo gida , ga kuma kuɗi kwance a account , ya nuna kwanciya da hannun shi yana ci gaba da cewa lallai Yazeedu babbar ƙaddarar mata ne ni. Ɗan yatsina fuska yayi sannan yaci gaba da cewa bafa laifi tana barbaɗa wuta a filin wasa D ' K ya kowa mata doguwar tafiya. D ' K...? Hmmm Dikko duniya sai Allah , ya faɗa yana riƙe haɓarshi da yanayin mamaki ya ƙurawa wuri ɗaya ido alamar tunani.

  Tambayarshi akayi ina ya samo zawara a arha haka ? Dariya yayi sosai tare da jinjina kanshi yace matar D ' K da suka rabu. Cikin dariya yaci gaba da cewa wai dan uwar biko shi D ' Kn yake bikonta dan ta ɗauki kanta alalan gero. Hmmm lallai iska tana wahalar da mai kayan kara , idan dai D ' K ne cikin ruwan sanyi zai kasheta bata san iskancinshi ba aradu labarinshi takeji. Tou kai meya haɗa ka da ita ne ? Waye ma ya sanar ma angulu a masai...... Ya ƙarasa yana ƙara gaggaɓewa da dariyar fita addini.

    Bayan wani lokaci ya nuna kanshi yace wai ni ? Nine zan aureta , in banda haukar mata da rashin tunani ni ? Wai ni Yazeedu nine zan aureta ? Gaskiya bata da lissafin rayuwa. In banda abunta bata duba can²nta ne ? Idan na aureta uwar me zan bata ? Filawa ai tafi kyau da gidan masu kuɗi , shanyar dusa kuma da kauɗar bushashen tuwo wannan kuma ai sai gidan talaka. Zanyi ta zuwa dai ina karantawa inyi gaba , wata irin azzalimar dariya ya sakeyi yana cewa bata san itama ta gidan neman hanyar tsira takeyi amma bata samu sa'a ba , hahahahaha kai yarinya bakiyi ma cikinki da gangar jikinki adalci ba , zo zo² zoki mana idan dai nine ni naci uwar ɗan tasha , dan bana tunanin duk cikar faɗin birnin jahar katsina kawai irina , banda mutunci kuma na tabbatar da cewa tantiri iri na a duk faɗin yankin katsina bafa za'a taɓa samu ba. Dan babu tantirin ɗan iska kamata , idan dai kinajin wasa ki tambayi Dikko ya baki labarina. 

  Fat , Fat , ² haka lumfashin Amisty ke halbawa tsakanin rayuwa da mutuwa. Yau duk abokan tashar nata babu wanda yake ɗakin da sunan jinyarta. Uwa ko uba nata kuma ? Basu da labarin halin da take ciki. Tunda ko tana da lafiyarta basa ganinta basa kuma jin labarinta , a gari ɗaya ake amma kowa yana nashi matsugunin. Wani bushashen ɗan sanda aka aje wanda koke mace idan baki da yunwa kina iya bashi kashin bala'e. Wai shine aka ajiye dan ya kula da Amisty. Idan ta dawo hayyacin ta , ta nemo musu inda takai musu kuɗin Baba. Likita ne ya shigo tare da malaman jinya bayan yayi ɗan abinda zaiyi aka taimaka ma tafiyar numfashin nata da iskar bature. {{ Oxygen }}.

      Kallon agogon dake ɗaure jikin tsintsiyar hannuna nayi sannan na kalli inda yake tsaye jikin madubi yana murza hula , ta cikin madubin ya kalleni so ɗaya sannan yaci gaba da abinda ya shafeshi. Bakin ƙofa na koma na tsaya ina cewa gaskiya ba inda zakaje na ƙarasa maganar kamar zanyi kuka. Juyowa yayi tare da jingina da jikin madubi ya dafa hannunshi ta baya cewa. Nace miki bazan daɗe ba , tou kuma tunda kasan baka daɗewa ai ba buƙatar fitar ko...? A hankali ya fara tahowa yana cewa tou ki hanani fita da ƙafafuwa na in gani mana. Kwanciya nayi ƙasa a bakin ƙofa kaina na kallon sama na miƙe ƙafafuwana da hannuwana nayi irin kwanciyar gawa. Cikin kuka nace shikenan ka tsallake kabarina Dikko ka wuce. Da sauri ya maida ƙafarshi baya daya ɗago da niyar tsalleki ne ya wuce. Cike da shagwaɓaɓɓiyar muryarshi yace haba An mata wai miye kike haka dan Allah ? Ban tashi ba kuma ban daina kallonshi ba nace ba kace sai ka fita ba ? Kai da ƙafafuwan ka ? Tou gani nan kwance ka tsalle gawata kawai kaje abunka na ƙarasa maganar ina zarge hannayena a ƙirjina na rufe idanuwana. {{ hmm taf aradu idan wani namijin ne ba kabarinki ba ko makomarki ya gani sai yayi abinda yasa kanshi can ke ta matse mawa . }}

   Cire cingom in bakinshi yayi yana wasa dashi a hannun shi , bayan wani lokaci kuma yayi ɗan latse² a waya ya kara a kunnenshi. Saida na cikin wayar yayi magana Dikko yace Abbakar kuje , ya ƙarasa maganar yana ɗan shan idanuwan shi da suka canja launi. Ey ya faɗa yana komawa ciki. A , a kawai dai na fasa fita ne , kaina yanamin ciwo ya faɗa a dai² lokacin da yake zama gefen gado yana nuna kan nashi da yanayin damuwa. Ey , yayi bacci tun ɗazu. Babu damuwa saida safe. Ya faɗa yana ajiye wayar , ɗayan wayarshi ya ɗauka ya cireta a jirgi , data ya buɗe tare da antaya duniyar yanar gizo.

   Saida saƙonni suka fara shigowa ya ajiye wayar ya tashi yana rage kayan jikinshi. Tasowa nayi daga inda nake kwance na matsa inda yake nace yi haƙuri. Ba tare daya kalleni ba yace kawai ya wuce yayi maganar yana komawa inda ya ajiye wayoyinshi ya ɗauka ya koma palo , ƙasa² nayi dariya bayan ya fita a zuciyata nace shegiya ni , na ƙarasa maganar ina kwanciya a gado na ɗauki wayata na fara kiran Hajiya Mai gilashi. Wayarta a kashe har yanzu lallai duk yadda za,ayi in Allah ya yadda sai naje gidanta idan Allah ya kaimu. Allah dai yasa ya barni inje , wani sashi na zuciyata yace kawai cewa zakiyi ya kaiki , wannan shine gaskiyar magana , saukowa nayi daga saman gadon na fita palo inda yake.

Ya toshe ɗayan kunnenshi da abun sauraron magana , ya ƙurawa waya ido yana murmushi. Duk maganar da nayi kwata² ma bayajina sam² , zagawa nayi ta baya da niyar in ɗan riƙeshin nan irin idan mata suka tashi labbatar namiji idan suna san wani abu daga gareshi. Amma kafin in riƙeshi sai me…? Wani irin ruɗaɗɗen ihu nayi tare da faɗar da wayar daga hannunshi. A firgice ya juyo ya kalleni sannan ya tashi da sauri zai ɗauki wayarshi a lokacin har na zagoyo na rigashi ɗauka , bani wayata yayi maganar ranshi a matuƙar ɓace , kyarma jikina ya farayi saboda na tsorata da irin kallon da yakemin. Dakewa nayi tare da cewa idan fa naƙi bayarwa ? Sai in kashe ki………… Ya faɗa yana nuna shaƙewa da hannunshi saman wuyanshi , cike da tsantsar ɓacin rai nace ai yau nice zan kashe ka. Nayi maganar idona yana kallon ƙasa. Wani irin wulaƙantaccen kallo yayi min tare da nuna kanshi nine zaki kashen ? Kafin inyi magana Papy ya shigo yana kuka , ihun da nayi ne ya tasoshi daga koma ina yake yana bacci , cike da ɓacin rai Dikko ya jinjina kanshi ya matsa yaja hannunshi suka fita.

  Wuri na samu na zauna na shiga binciken waya. A raina kuma addu'a nakeyi Allah yasa Papy yaita kuka ya hanashi dawowa da wuri , dan abinda na fahimta baya so yanayin wani abu wanda bai kamata ba idan ɗan shi yana gidan. Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un , wata irin yamutsa kaina yayi da sauri na rufe idanuwana dan irin ƙazantar dana gani , tunda nake da Dikko duniya bai taɓa abinda naji na tsaneshi ba sai yau , wayyo Allahna ? Mayun mata wai ina ruwanku da mijina ne ? Kunzo kun daddaɓeshi sai kace ƙuda ya samu ruɓaɓɓen nama. Ga kira waya sai shigowa yake ba ƙaƙƙautawa , saƙonni sai kokawa sukeyi wurin shigowa , jikina na kyarma idona cike da hawaye na fara neman number Sharifa , dakel na gano ta ɗan iska wai "yar uwarshi ya rubuta a jikin numberta , kam bala'e wai duk ina , ina wannan iskanci ya faru ? Da wata ɓeranyar yarinya shegiya zata girmeni baifi da shekaru biyu zuwa 3 ba , ta ciko mishi saƙon nata itama da ɗanyayen kalamai daɗaɗa , sanyaya , Sharifa kuma ta rubuto mishi cewa ni na kirata na zageta , nayi mata gori wai ni injini ni Sultana wai nice nace wa Sharifa ita karuwan Dikkon ne , a taƙaice dai ita Yusra kaf a cikin kwaratan itace ta saman iska , kaf babu feƙaƙen ɗan tasha na sama a wayar nan sama da ita , guguwar "yar iska ce , dan kalamanta data faɗa tana tattaɓa wasu sansa na jikinta nida kunya ta haifa na rantse da girman Allah ba a baki ba a rubuce duniya ni bana iya rubutawa bare kuma azo fagen in furta. Karuwai.....?׳ hmmm karuwai na sha'aninsu idan suka samu mazajen ballagazanzun mata , a hayaƙe ya dawo saida ya wanwanka min mari ya anshi wayarshi. Cike da rashin tsoro nace kadaiji kunya kuma kayi asara daka kallar da idonka tsiranci haram , naji kunyar kuma naje na kalla haram ɗin naki ne ko nata ? Banyi magana ba na nufi hanyar fita , har na fita zuciyata ta hayaƙoni na dawo , 

     Nima dai a daren nan nayi ɗan ƙaramin hauka , haka na rufe idona naci gaba da zage² ba shi nake zagi ba su Yusra nake ta ɓaɓɓarkawa zagi , keda ke gidanki idan kinsan halin da nake ciki Dikko yasan ina nan ko yanajin abinda nake cewa ya basar dani yaci gaba da cht inshi hankalinshi kwance , inda yake saman kujera naje na kamo ƙafarshi na jawo da ƙarfi ina cewa saina faɗar dakai na ƙarya maka kashin baya , da ɗayar ƙafarshi yayi min wani irin kyakkyawan harbi a fuska saida hancina ya fashe. Shi kuma yaci gaba da latse² a wayarshi da yanayin shauƙi , baya nayi inajin juwa ɗakin na gani yana juyamin duniyar tayi shiru banajin motsin komai watan saurarena ya ɗan ɗauke shima numfashin an riƙeshi. Ina dawowa jin sauti na sake tafiya inda yake ina faɗar saina kashe ka , janye wayarshi yayi daga fuskarshi yana kallona da wani irin jarabben kallo , a kasalance yace wai nine zaki kashe....? Ya nuna kanshi , ey , An mata dukana ? Ey , har wannan shima zaki ? Ya nuna daddatsewa da hannunshi , gemunshi kenan , dai² lokacin dana iso kusa dashi , riƙeni yayi da yanayin mayata yace muje saman gado mu kashe kanmu nima saina kashe ki...... Ni ka sakeni , anƙi a sakekin ya ƙarasa maganar yana rufe ƙofofin hancina da "yan yatsunshi biyu , da hayaniya nace wai ba nace ka ƙyaleni ba ne iye ? Shima da irin magana na yace wai bana ce bazan ƙyale ba iye ? Ya faɗa a gajiye yana sauke numfashin jaraba yana min wani irin kallo.

   Kwacewa nayi , ya riƙoni da sauri yace ai ƙarya kikeyi yarinya , ina ne zakije ? Sai kin kashe ni..... Ya ƙarasa yana lumshe idanuwanshi tare fitar da numfashi cike da kissa , ƙiƙi² muka fara rigel². Ni ina so in ƙwace , shi kuma yana so ya riƙoni har ya sauko daga saman kujerar , saina tafi , bana sanka׳ na ƙarasa ina ƙara yawan kukana. Ai basai kinsha wahalar faɗa ba nasan wannan shekaru 3 zuwa huɗu da suka wuce. Jana ya farayi hanyar bedroom wai muje in kasheshi. Da Allah ka ƙyaleni kaji , ah ni bazan ƙyaleki ba aradu sai kin kasheni yayi maganar yana murmushi tare da kafe ni da mayataccen kallonshi.

Nanfa abun yaci tura naci gaba da ɓarin maganganu , tun yana kallona har ya fara rufe ido ya sake hannuna. Nan gori ya tashi tunda na lura yana da buƙatuwa dani , haka na warware kamar farfera na ci gaba da zazzaga ranshi mutunci ni matar da za’a sauke buƙata a kaina , ƙarshen film in nace tafiya zanyi , cike da ɓacin rai yace ina ne zaki iya zuwa ? Bayan baki da gidan da yafi wannan ya nuna ƙasa da ɗan yatsanshi na hannu dama , yana ci gaba da cewa kije mana ? Idan kin tafi zan mutu ne ? Ya nuna kanshi cikin tsatsanin fushi mai sa kaji cikinka ya juya na kasa kallonshi , dan kinga ina lallaɓaki ? Idan kinyi haƙuri baki je ba kin zama banza , ki tafi ya nuna hanyar fita , rage murya yayi da cewa ina da dubunki a waje sai me ? Ko an faɗa miki wai bana iya rabuwa dake ne ? Kullum² zakije sai na tafi gidanmu kaza² tou kije ko wani ne ya baki haƙuri ? Hmmm ke baki san iskanci na ba , nafi ki ƙaryar rashin kunya wallahi , inda duk kike zato na tuni na wuce wuri nayi gaba…. Idan kina nan wata zan kawo idan ma kin tafi haka dai zan sake kawo wata.

    Kina iskanci ana baki haƙuri tou an daina cewa kiyi haƙuri ki tafi duk gidan da zakije , ba burin daya fi duk macen da bata da lissafi tanayin faɗa da miji tace gidanmu zanje , fuuuu tayi yaji ya nuna da hannu , tou idan baki sani ba babu babban kuskure da yafi wannan jakancin , ko shi mijin dake aurenki bai san kuna da gida ba ? Ai yasan ba a sama kika faɗo ba , ya nuna yana ci gaba da cewa ai ina ganin idan yaso zaice kije gidanku. Mahaukaciya ma dake da Allah , fitarmin daga ɗaki yanayin fushi ya fara hawa kaina kafin inji miki ciwo , kuma na rantse da girman Allah idan kika fita gidan nan ko ina kikaje har can zan biki saina lalata miki fata , kaca² zan miki. Fita nace........................ Ya faɗa yana nuna hanyar fita tare da rufe idanuwanshi cike rashin mutunci. Fashewa nayi da kuka nace yi haƙuri don Allah , zo nan , ya kirani da hannunshi , tafiya nayi ina kuka ina kallonshi. Riƙeni yayi a jikinshi yana sauke ajiyar zuciya bakiji An mata , wai ni miye matsalar ne ? Kullum sai kin ɓatamin rai wai me nayi ne ? Haba An matana ya ƙarasa mganar yanamin kyakkyawan riƙo , cikin shashshekar kuka nace kaine , nine kuma ? Tou wai meye nayi da zafi haka ? Ka daina so na ai , haba Yarinya ke ko wani ne ya faɗa miki ai zaki ce a , a , duk duniyar nan wai waye yake dani idan bake ba ? Haba ƙaramar yarinya.... Duk kin burkeni na zama wani lusari sai anfani kike da soyayarki kina murzamin zuciya san ranki ya ƙarasa yana min kyakkyawan murmushi , shiru nayi ban mishi magana ba , kefa yarinya ce ? Kalli Dikko fa ? Akwai tazarar tsayi shekaru da kuma tunani , cikin dariya yace wallahi kin maidani kamar wani zararre ke ko tsoron Allah ma bakyaji ? Haba An mata , ɗagoni yayi daga jikinshi yace ai nasan ma kin yafemin ko ? Ey tou zo muje. Yana riƙe dani har toilet da kanshi ya wankemin fuska yana cewa dan Allah An mata ki daina ɓatamin rai gaskiya banajin daɗin abinda kikemin.

   Wai ke baki san ba'a ɗagawa miji harshe ba ? Baki san idan mijin yanayin zuciya yadda ake saukeshi ba ? Ba'a hawo namiji yayin da yakejin tuƙuikin ɓacin rai , komai yana iya faru a dai² lokacin da yakeyin fushi , Juyowa nayi na riƙeshi ina ci gaba da kuka , a wahalce yayi gajeriyar dariya cewa ai nasan baki iya tafiya ki barni wasa kike , ƙaramar yarinya. Wai miye ke damun kanki ne ? Meye nake miki wanda baya miki daɗi....? Ni kifaɗamin , faɗamin matsalata dake sai nima in faɗa miki matsalolinki kowa ya daina ɓatawa kowa sai a daina faɗan tunda kin gaji. Kinga ko a rigima kin fahimci ni nafi sangarta bana gajiya haka zakiyi ta hawoni ina baki kashi kullum kina fama da jinyar fata , kuma kinsan banayi zuciya in zaneki kuma in maƙalƙaleki anjima inyi ta warwarewa ya riƙeni yana nuna yadda yakeyi idan yana kwance dani , dariya nayi ina kallonshi. Shima dariyar yayi tare da ɗagamin gira yace wallahi kuwa , tou ni ina ruwana ? Gani ga "yar yarinta ina fa morewa , niɗin mai sa'ar rayuwa ne , duk da dai kince wai niɗin tsoho ne , amma a haka dai ai ina bada wuta a tsakiyar filin wasa ko ? Ya ƙarasa maganar yana ɗan taɓe bakishi tare dayin wasa da girarshi.

  Murmushi nayi ba magana amma har yanzu ina kwance a jikinshi , ɗan wayancewa yayi dai yaci gaba da yabona wanda nidai nasan a zuciyarshi ba haka bane ba , yana dai yabo na ne dan inyi farin ciki ya kuma sauke buƙatuwarshi yayi bacci da natsuwa. Koma dai bada gaske yakeyi ba ni naji daɗi , yana da kyau maza su riƙa farfaɗawa matayensu kalaman da zasuyi farin ciki su girmama musu kansu sai suji su suma ashe dai wasu manyan shegu ne , ta hakan ne zaka riƙa zaliƙo mata matsalolinta a hankali idan mai hikima ce saita riƙa gyarawa , irin dai kana yabonta kana cewa ai idan kikayi kaza kinga yadda kike bada haske ? Ko kike ruɗani ? Ko bana tare dake sai inyi ta tunaninki , kaza². Nan zaka ga ta warware tace you ai kaza da kaza ma da nakeyi kaza. Ni nayi farin ciki da yacemin duk nafi su Yusra kyau , gani "yar gayu kuma ni "yar yarinya su duk sun tsufa ma , ai haɗuwa ta ta wuce duk inda bana zato , shi a ganinshi ma yafi ko wane namiji sa'ar aure , bayan ni nasan Dikko ƙarya yakeyi , kuma wai da nace masa ba wani cewa yayi in kalli kaina a madubi fa , An mata kalli idanuwanki , ji lallausar bakinki ya nunamin saman lips ina , kalli nan ji can uwa uba kuma saikin dafe uztaz D ' K a gado. Kalamanki suna da daɗin sauraro bayan ni nasan duk lokacin da zai kwanta dani sai ankai ruwa rana , yanzu nan ya gama min faɗa ina ɗaga mishi murya , amma da yayi dai nayi farin ciki , 

Wai ni ina da kyakkyawar fata idan kuma nayi mata ado da lalle zan ƙara haɗuwa wai kuma lallen na hausa amma a zuba turare a cikin lalle dan ya kashe ƙaurin lallen , warware kaina yayi yana shafa gashin kaina wai na iya gyaran gashi ya mishi kyau a haka. Shiko banyi kitso ba yafi ibar mishi lissafi , haka na saki baki naita dariya kamar sakara ina cewa ai idanma nayi kitson warwarewa yakeyi , ey ai dama nima bansan kitso , saidai ina san wannan kitson kin tunashi ? Wani mai kyau ? Kai yayi miki kyau An mata , nifa nasan bana kitso harma gara kalaba , amma da nace masa ni banyi kitson nan ba , cewa yayi na manta yana ta nunamin yadda kitson yake. Yadda yake nunamin irinshi ni nasan ban taɓayin irinshi ba a tarihin rayuwata. Amma Dikko ya kafe kai wai nayi shi in tuno mana , saida na natsu sosai na gane irin kitson dake kan Yusra ne , dakel dai nayi yaƙe mai ciwo , shima zanen lallen a wurinta ya gani ai na gani itama lallen hausa ne akayi mata wani irin ado mai ɗaukar hankali.

    Wato duk duniya ita mace baka da abinda takeso sama da a yaba mata , suma mazan haka suke , haka kuke mana "yan rainin hankali , kuma so kuke a yaba ku kan nan naku yana muku wani girma kunajin ku wasu manyan "yan duniya , kuna wani ciccika fuska ku masu gida ana zugaku kuna wani karkace baki kuna dariyar ƙasaita kan׳ dariyar cikin izza da nuna isa. Yana da kyau mazaje ku riƙa gyarawa matayenku da irin yajuju wama jujun da ku kuke gani a waje. Kuma a hikimance , ba zagi ba duka ba gori wance ta fiki ko wane matar shi kaza² a , a , ba haka akeyi ba a hankali zakayi mata dan kune kaɗai kuka san a inda kuke shiga kuna gano irin wannan duniyanci. Bawai nace kuɗin "yan duniya ne , ina nufin irin matan da kuke huɗɗoɗi dasu. Ba kuma ina nufin tasha ko sakarci ba , kamar a kasuwa ko a ofisoshinku da dai sauran wuraren da kuke mu'amula dasu , tunda suna ɗauko wanka da gayu kamar zasu tashi duniya dan haɗuwa , su barbaɗo muku turare a ciko ido da kwalli ana firfira muku idanuwa. Ku saki baki ba aji kuyita gaggaɓa dariya irin wacce ko matanku bakuyi ma irinta. Tou karta burgeka kuma karta ruɗa maka lissafi da tunani , ka riƙe karka bari tayi wasa da tunaninka nata ƙarya ne zahirin tana gida , idan tayi nata sai yafi baka sha'awa akan na sharar bakin titi , wai su kun gane matsalarsu.....? Matsallar auren su ba a gabansu yake ba. Haka zasu shaƙe miki wuyan miji suyi ta ranfa dashi , idan kuma ta gaji da cin aljihunshi taci shi har babunshi saita tura wata itama taci gaba da gayar miki miji babu tausayi , itama idan ta gaji tayi gwanjonshi shi kuma zuwa wannan lokacin ya zama ɗan gari. Ma'ana ya gane hanyar yadda take , kafin ki ankara an firgita miki miji , wata macen ma su biyu ne a wurin miji amma dai lusaranci da hauka yasa sunyi sake sun barwa karnukan bisa titi suna ta mishi haushi , baki jin haushin ta waje wai ta gidan itace ta tsone miki idon tsabar hassada , kullum kika tashi da ita a zuciyarki baki da buri da kwanciyar hankali yadda zakiyi waje da ita , tou idan ta tafi ance miki shikenan bazai sake aurar wata ba ? Ba matan gida ya kamata kuyi hassada dasu ba yaƙi zakuyi da matayen dake matse mazanku a waje , ku kuma maza gaskiya kuma kuji tsoron ku tausayawa matayenku , ku kyautata musu , kuyi musu magana da sanyi² ku lallaɓa su , ku tarairayesu , ku ririta su ku jawo su jikinku da farin ciki. Kuyi kwanciyar aure dasu cike da soyayya da kuma nuna musu finsu buƙaturwa hakan , ku gode musu ku yaba ƙoƙarinsu ku basu ƙwarin guiwa ku jinjina musu ko bakuji daɗi ba , a hikimance zaku riƙa nuna musu yadda abun yake har su ƙware su anshewa ɗan tama doki. Wasu matayen sunfi wasu mazan gogewa ta wannan harkar da kuma gogewar rayuwa ta zamantakewar rayuwarmu tayau da kullum. Wasu kuma mazan sunfi matan , idanuwansu a tsaye yake tsakiyar kai , tou koma dai waye tafi gogewa ta gogar da abokin rayuwarta sai kuyi rayuwarku gidan aurenku da natsuwa.

Kuma bawai ina nufin kuna biyewa matan waje ko ku fahimci magana ta da wani yanayi. Ku fahimce ni da kyakkyawar fahimta amma aradu ku ƙyale gaibu ku kama zahiri , idan kuma ka nuna mata taƙi gyarawa kayi mata…… Ba cewa nayi ka ƙaro aure ba , nufi na a ƙaro miki kayan ado a ci gaba da baki kula ana ta kwantanci nuniya da gyara har ki gane ki gyara , dan kunsan mu mata ba kishi mukeyi ba hassada muka iya. Sanin sirrin kishi zahiri babu munafurci da yadda akeyin shi kanshi kishin aradu yana nan wurin maza. To kuyi kishi yayin da akafi matayenku ku tsaya tsaye da gaskiyarku kuyi gyara.

 Tou lallai fa idan taƙi gyarawa ka lallaɓa kayi mata ƙarin...... Haske , dan inda kuke shiga mu bama shiga wurin , irin matayen da kuke gani mu bama ganinsu , kuke ganinsu kune kuma kuka san inda kuke ganosu har sukeyin abinda kuke ganin mu bamayi muku irinshi , wata matar daga gidan aurenta maƙotanta sai familynka da nata ahalin su kaɗai ta shiga kuma ta sani , sai abokan arziƙi , kuma kila su basu da wayayyun idanuwa bare ta waye da wayewarsu. Sanin da daka santa dashi tun tana budurwa kafin kuyi aure shine dai har yanzu babu wani ci gaba , wata macen kuma da wayewar ido take zuwa gidan auren amma sai ta zama wata aljihun gefen riga ta daƙiƙance ta zama wata sai addu'a kawai. Tou kai da kake shiga kana fita kana zuwa inda ita bata zuwa kuna ganosu suna labbatarku da irin abubuwan da suke jan hankaliku ka sanar da ita mana , ka koyar da ita , idan ka faɗa mata raguwa kayi ne ? Kaɗan faɗaɗa mata kwalwarta ka buɗar mata da idonta dai² irin yadda ka gano suka ɗauki hankalinka. Ka wadata matarka da sutura dai² ƙarfinka ka wadata ta da kayan ƙamshi mayuka masu kyau hoda sabulun wanka ka ciyar da ita karka riƙa maƙalewa wurin mai indomie ko mai tsire da wasu lafiyayen kaji kabar matarka taita kokowa da tuwo , wallahi kuji tsoron Allah kuci irin abinda kuke ba iyalinku irin abun nan da kukeyi kuci daɗi ku barsu da marmarin irin abinda ku ya gundireku dan nacin cinsa da kukeyi wallahi zalinci ne. Cuta ce , ku kuma matan kuma muji tsoron Allah masu siyar da shinkafar miji kuna zubin adashe Allah yana kallonku tom.....

  Idan an gyara miki kema ki riƙa gyarawa mana , kar yace kije kiyi kisto two step , ki karkace baki ah ni wallahi bana san wannan kitson kaza² , to wane iri kike so ? "Yar rainin hankali. Ke harma sai ya faɗa miki kiyi irin style kaza ? Ashe ma baki san abinda kike ba. Idan akwai abinda yafi two step kiyi mishi mana , ke meye naki a ciki ? Ba shine yake so ba ? Tou ayi mishi mana a zauna lafiya ? Ko yace miki wallahi kaza na gani ya burgeni , kiyi irinshi , ke uwar tsiwa maimakon kice tou sai kice ah sai kaje can idon daya gano a wurinsu kaje kayi ta gani. Ƙalu balenki da bawa namiji wannan ansar idan ya fara gani tou fa lallai ƙaryaki ya ƙare , kenan kinma yadda yaje ya gano na wajen ko ? Shin wai mema kika tsaya yi har namiji yafi ki hikimar rayuwa ? Ke bakya kishin kanki ne eye ? Haba Hajiyata da Allah karki bani kunya mana. Ko ke baki so tou kiyi mishi idan dai shi zaiyi farin ciki mana , sai sunje sun kallo na wajen a ɗauke miki hankalin miji ayi yamma dashi a barki da ciwon tunani , idan shima ɗan rainin hankali ne kuna gari ɗaya fa da kinyi waya zaice yana abuja ko kaduna ina nan airport zan hau jirgi in tafi lagos , ke ya maida jirgin tana can ta ɗaukeshi an barki gadin gida , kar kuma mijinki yayi tafiya ki tuno cewa kila yana miki ƙarya ne baije ko ina ba , kulli inki ahir inji tsofi , ƙalubalen ki da zargi. Damuwa ta dameki daga nan sai neman shawarar abokai , idan kinyi sa'a da ƙawar kirki ta baki shawara ta gari , idan baki dace ba ta haska ki da malam tsibbu suma daga nan kasuwa ta buɗe , idan kuma kika hau layin maijin taushinki tasa ki , ki kakkaɓo auren , dama tana can tana ta yawon zawarci ita ɗaya ta rasa ƙawar cin titi tou ta samu abokiyar yawo , idan kuma ta ƙwarewa cin amana ta auren miji a barki da wallahi² , ke baki gane illar abun sai kin shiga makarantar , baza ki fahimci wuyar karatun ba sai an shiga second semester ku kula dai......

 Gadai Dikko yana faɗawa Sultana , wanda ita a ranta tasan ba haka bane ba. Amma taji daɗin yadda ya yabeta tare da nuna mata tasha gaban mata da yawa. Tou kai idan ka tashi faɗar naka kalaman ka faɗa mata su da gaskiya cikin soyayya. Ku daina haɗe fuskoki wa matayenku haka babu kyau , wani namijin idan kika ganshi a majalisa yafi kowa harshe dariyarshi tafi ta kowa , duk mai tallar da tazo sai yajata da surutu , sai matarka zaka rainawa wayau idan ka tashi shigowa gida ka haɗe fuska kayi ta wani gadarar banza wai kar ta raina ? You bayan ka manta kun haɗu a tsakiyar filin wasa ? Allah wani namiji idan ya shigo gidanshi kamar "yan fashi sunyo samamen dare. Ba "ya "ya ba iyayen suma kansu gabansu harbawa yake kamar an ɗorawa mutum wuƙa a maƙoshi.....

   Cike da soyayya mukayi wanka muka baro toilet in cike da tsantsar muradin san kasancewa da junanmu. Kuma har muka fito bai daina zugani ba sai dariya nakeyi ina watse baki kamar lefen wacce babu uwarta a gidan babanta , ina ta sakin layi , zuwa wannan lokaci gaba ɗaya na manta da wasu banzayen hotunan da na gani a wayarshi na fuskanci rayuwa mai daɗi da gusar da damuwa a wurinshi........

  Bayan kwana huɗu.

  Ni na rasa inda mai gilashi ta sake a cikin jahar katsina , na nemeta na rasa inda take , kuma har gidanta naje bata nan kuma Dikko da kanshi ya kaini. Wayarta ma a kashe. Daga gidanta gidan Inna mukaje kamar dai kullum yauma haka taita habaice² tana zagin Dikko wai bazai zauna mata a kujera ba , ƙiri² Inna ta koma wata zararra , shiko murmushi yayi kaɗan ya samu wuri a saman kafet ya zauna , nima kusa dashi na zauna. Haka taita zaliƙe²n da ita kanta bata san dalilin yinshi ba , taita zaginshi tana aibatashi saida ta gama kaf tace idan yaji fushi ya sakar mata "ya , shafa kanshi yayi ƙasa² yace ban gaji ba ya faɗa yana suɓaro baki a sakace , saida ta gama dashi ta juyo kaina tace kema ɗayar mara zuciyar kaza² nima taci gaba da sheƙeni har ta gaji tayi shiru , saida ta sauka ta gama da kanta ta rufe bakinta mukayi mata godiya mai gida Dikko ya sauke mata manya kuɗi muka wuce gidansu.

 Ajiyeni yayi ya tafi huɗɗoɗin shi , Momy kuwa sai ɗan zungurar min ciki takeyi tanasan ta gano wani abu ne daga gareni akan Sharifa. Shiru nayi nidai idan ta matsa min da tambaya saidai ince mata Momy ban sani ba wallahi , wai har yanzu munayin faɗa da Dikko ? Tambaya ɗaya takemin ni kuma ansa biyu nake bata , ah umm. Gajiya dai tayi ta ƙyaleni , har ɗaya saura na dare bai dawo ba saidai ya turo Ashiru ya maidani gida , wato yau ya samu hanyar tafiya wurin "yan iskan matanshi ko ? Ita kuma Momy harma ta yadda da ƙaryar da yayi mata wai ya fita da Dady. Dan da Ashiru yazo tafiya dani sai ta kirashi wai shi yazo da kanshi ya tafi dani mana , shine yace mata yana tare da Babanshi kenan dan karta dameshi. Tun a mota nake kiranshi , shine ya turamin da saƙo wai yana meeting , danma ya ɗaukeni kidahuma. Ci gaba nayi da kiranshi ƙarshe kashe wayarshi yayi. Ashiru ka kaini wurin Dikko , lafiya ? Ya tambayeni ? Lafiya qalau shine yace ka kaini. Mai gidan ranki ya daɗe ? Tou meye a wurin da bazanje ba ? Ai banma san inda yaje ba , daga haka bai sake magana ba , nice naci gaba da cewa amma ai a wannan motar yake a ina ka samoshi ka ɗauko motar ne ? Shiru yayi ya ƙyaleni , fita nayi daga motar ba tare dana sake cewa komai ba na nufi ciki , Papi yana kwance a palon ƙasa yana bacci saman kujera. Ɗaukarshi nayi ina taɓashi ya buɗe idonshi yana shashshekar kuka , ɓata fuska yayi a hankali ya rufe idonshi yana cewa Yaya.... Kila ya dakeshi ne. Me yayi maka ? Saida ya sake sauke ajiyar zuciya da yanayin bacci ya sake cewa Yaya.....

    Majalisar ɗinkin "yan matan tashi. Muji , yau da Jiddah ya fara zama sai kuka take masa wai Ya Yazeed yace zai aureta kuma tayi hidima dashi mai girma amma yana ta wani zamewa baya ɗaukar wayarta kaza׳ , shi Dikko ma daga farko bai gane wane Yazeed take magana ba saida tayi mishi bayani , tou shi Yazeed harma ya zama Yaya baida labari ? Hidimar da ta ita Jiddahr tayi ma shi Yazeed ya tambayeta , cikin inda² tace kawai dai kayi mishi magana muyi aure. Cikin rashin fahimta yace waike kece zaki auri Yazeed ? Ey , jinjina kai yayi tare da ɗan karkace kanshi ya tafi duniyar tunanin rayuwa irin ta gidan Yazeed.....

   Ƙaton gidane ginin zamani , ya tsaru gidan iya tsaruwa kuma anyi mishi ado da ciyayi masu kyau. Ɗakin mai gadi da ɗakin janareto , a gefe kuma ga wasu irin zabga²n motoci masu masifar kyau da tsada an jera wanda shi mamallakin gidan ne ya ciyosu a harkar wasan danbe. Ajiyar zuciya Dikko ya sauke a wahalce yana jinjina kanshi , duk duniya shidai baya so yaga mace tana wahalar rayuwa. Baya so yaga rayuwar mace tana tangal² , kallon Jiddah yayi sannan ya gyara zamanshi ya miƙe ƙafafuwanshi yana daga saman kujera ƙafa ɗaya saman ɗaya. Wannan inji haka ake cika shi da mai safe rana da dare har gari ya waye a cikin awanni 24 haka yake aiki ba'a kashe shi saida idan za'a zuba mishi mai ko idan ya lalace , duk fitulun gidan a kunne suke suma cikin awowi 24 da wasa ba'a kashe su dare ko rana addau² haka suke amma ɗakin matar gida ko kwan fitila bata dashi , babu wata cima a gidan ita kanta matar gidan duk haɗuwar gidan da tsaruwarshi wankau takeyi tana ciyar da kanta.

    Ga hausawa da wani irin hali wai sai kaje zuminchie wa ɗan uwanka amma ka tattara burinki baka kallon rayuwar gidan sai girman gidan , idan ka ɗora mata buƙatarka tace bata dashi sai zagi da gulma munafuka ta tattare komai ta hanamu , daga ita sai "yan uwanta sai iyayenta , ta shanyeshi ta hana ya bamu ko ya bata ta bamu ta hanamu , shin tana samu tana dashi ko bata da ? Kudai , a baku.........׳ kamar mutuwa. Shi Yazeed inuwar giginya ne shi , yana dashi da ya bawa matarshi gara yaje ya zuba harajin wasan danbe , gashi cikakken ɗan iska wata rana ma a gidanshi yake kai mata matan bariki , azzalimin namiji ne dan shi matarshi ta gida ma bai ɗauketa a bakin komai ba , "ya "ya ne ta kwarkwartsa mishi bi da bi a tunanin ta idan ta aihu da yawa ko zai gyara halinshi amma abun sai ci gaba yakeyi kamar ana daka mishi tsawar bakin iyaye. Ni a tunanina duk mai shi zai bada ne , kyauta dai bata kawo talauci. Haka kuma rowa bata kawo arziƙi , duk mai bayarwa baya rasawa , idan kuma ka samu kaci kai ɗaya dan kar ka bayar ka rasa ? Tou wata rana ma gaba ɗaya barin duniyar zakayi da kuɗin da duk tattalin da kakeyi karsu ƙare ko kuma ka tara da duk wani tsari naka na rayuwa , tou fa lallai duk zaka barsu ka tafi kai ɗayanka kaje wata rayuwa ta daban. Gara dai idan kun samu kuɗan taimakawa masu buƙatar taimako sai kuma Allah ya ƙara taimaka muku.

    Caf Yazeed cikakken ɗan tasha ne. Baida mutunci ko kaɗan , dan ko A C ɗakin matarshi da yasa daga farko daga baya ƙwaƙwulewa yayi taci gasar danbe. Amma saboda riya yabar iyalinshi da wahalar rayuwa , ko tace baya bata abinci tana cikin wahala , sai ace bata godiyar Allah , abinci buhunna² gasu na ajiye a store taci ɗin ma ta ci ƙaniyarta dan tasan ba nata bane ba kwalliyar gidane saboda mutane su gani suce yana da kirki , bayan wani lokaci kuma ya jera mutane layi ya rarraba musu shi sadaka.

  A anguwar sai zaginta akeyi ita marowaciya ne tabar "ya "yanta da yunwa sai azabar neman kuɗi kamar zataje dasu lahira. Wani faɗa da sukayi har iyaye suka shiga ciki tace har a c ya cire a ɗakinta da palo tace yasa musu fanka ya ƙiya , shine yace tana wurin gyara , ganin iyaye yasa yaje ya samo hoton a c n yazo ya maƙala mata , shima tayi magana yace ya gyaro itace ta lalace shi bata da tattali kaza² , aka haɗu aka bata rashin gaskiya , shi kuma ganin ya samu sa'a yasa yaketa gurje mata mutunci da wahala. Duk wanda ya kalli gidan Yazeed akace ansan sunan wani abu waishi wanki ko wankau ? Sai su "yan cikin anguwa sunce ƙarya ce , ita kuma tunda anguwar masu kuɗi ne take sa ana tattaro mata kaya tana wankewa ta goge tunda dama kayan "yan gayu ba wani datti yakeyi ba , haka azzaliman maza sukeyi dan rashin imani. Shine Jiddah zata shiga ? Allah ya basu zaman lafiya..... Allah ya rufawa An matarshi asiri da tana can tancin ƙaniyarta gata yarinya , wani hali nata ya tuno dan haka yayi taƙaitacciyar dariya , da tace wai ya tsalleke kabbarinta ya wuce , cikin dariya yace niɗin banza An mata , saida yasha dariyarshi Jiddah tana daga gefe tana kallon ikon Allah , shi yama fita daga wannan sabgar ya tafi kallon hotunan matarshi.

  Duk hoton daya kalla zaiyi murmushi a ranshi yace An mata rigima , wai Dikko ka tsalleke kabarina kaje kawai , haba An mata kar Allah ya nunamin ranar da zaki tafi ki barni a duniyar nan , bana fatan naga ranar da ni zaki shige cikin ƙasa ki barni , ina so in rayu dake har ƙarshen rayuwata in tafi in barki ki rayu rayuwa mai cike da farin ciki , gaki ga Papi da "yar ƙanwarshi ko ɗan kaninshi , burina yanzu a duniya bai wuce in mutu a hannunki ba , ina sanki׳ ki jarumata..... Hayaniyar dake tashi ne ya dawo dashi daga duniyar kallon hotunan da yakeyi....

    Salati yayi tare da fiddo duk girman idanuwan shi ganin Sharifa da wata irin bahaguwar shiga ta jahannama ga fasinja. Rankatakaf su Ashiru suna wurin , shi wallahi kunya ma abun ya bashi , gata ta shigo full battery wato cake take. {{ tana cikin maye }} tasha wasu irin zaƙo²n akaifu ansha girar ido atach har tsakiyar baya , wasu irin "yan kunne girman round insu yakai girman ɗan hannu sai ibar hayaƙi take tana barbaɗashi sama yana bin iska. Jiddah na riƙe da ita sai zazzabga mata mari takeyi wai ranar da Ya D ' K yai mata liƙi ita Sharifar wai tanayi ma ita Jiddah gwalo wai an saketa , tun ranar nake nemanki shegiya ƙazama , shine fa aka cakume rigima. Dikko kuwa lallaɓawa yayi yai layar ɓata bai yadda kowa yaga fitarshi ba. Har baya ganin gabanshi ya shiga mota dakel. Shi gaskiya bawai zaice yana san Sharifa ba , ah tunda dai zai aureta ya kamata ta kasance mai tarbiyar da kamun kai. An mata har hannunshi ta zauna kafin suyi aure amma kullum tana cikin hijabi , gaskiya yana san matarshi ta kasance mai sirrinta jiki yayin da wasu mazan da ba muharramanta ba suke a wuri. Baifa isa yace baya auren Sharifa Dady zaiyi damuwa. 

   Taya za'ayi shi matar da zai aura ta kasance haka ? Irin wannan dressing ai ba nan akeyi ba , ko a gidanka kayi irin shigar ai zaka saka hijabi idan mutane suna zuwa , tirr mtsww... Gaskiya zai faɗa mata ta daina yin haka shi baya so. Haka ya iso gida da tunani barkatai a zuciyarshi , bayan yayi parking yake ƙara hasko yadda ya ganta zuciyarshi na daɗa soyuwa da ɓacin rai , kai a , a gaskiya a , a , haka ya shiga ciki ranshi a matuƙar ɓace kawai dai yaji babu daɗi yana tayin damuwa har zuwa safe. 

  Dady kuwa an kaishi asibiti. Bayan likitoci sunyi bincike²nsu suka tabbatar wa da iyalinshi cewa ya samu shanyewar ɓarin jiki , ai uwar Hafsa cewa tayi ita bada ita sa lallen kaza ba , dan ba zata wani iya zaman jinya ba. Da sauranta zata taga gaba tayi aurenta ta gurji sauran shekarun da suka rage mata , wallahi bata zama tayi ta kwasar ƙazanta , Dady ya karkace baki yadda masu irin lalurar suke magana yace baya sakinta , tace bara ta kira inda za'a ansar mata tikitinta na saki a hannunshi tunda ba tare aka haifesu ba , wayarta ta ɗauka tana cewa zaka ga yadda za,a ansar min idan kazo musu da rainin hankali ƙarfin shari'a ba wani ruwanshi da shanyewar jiki zasu tafi dakai su calika ka. A taƙaice dai sun rabu kuma dan rashi inami ta tattara duk ɗan sauran abinda ya rage na ƙaddororinshi tayi gaba dashi wai karya cinye tattalin arziƙin kuɗi "ya "yanta su tashi a hoto , yadda ya nannaɗen nan idan ta zuba mishi ido sai ya cinye kaf kuɗin a wurin jinya.....

  Haka taje asibitin da Amisty take ko tausayin Amisty bataji ba , ta ɓanɓare abun ƙarin lumfashin , Amisty ta fara rawar kyarawa , Momy tace kuɗina suna ina ? Faɗamin gidan uwar da kika kaimin kuɗina ko ki tafi lahira tsaye....... Ha׳ Amisty keyi , dariya Momy tayi cikin rashin imani tace rayuwa ko mutuwa.....? Amisty ta nuna rayuwa watom ta mayar mata da abun , mayarwa tayi tare da jaddadawa Amisty kwana biyar ta bata ta haɗo mata kan dukiyarta idan ba haka ba zataje gidan yari , akwai wani sabon d p o da aka kawo acan sabon gari police station inyamuri ne zata haɗata dashi , zatace idan ya anshi kuɗin ya ɗauki one miliyon haba kundai san inyamurin mutum da kuɗi.....

  Halima mijinta da sauƙi sosai anma sallomoshi ya dawo gida , yana dawowa kuma da zancen ƙarin aure yazo , fitina ya tashi da rashin kunya nan fa ta tattara ƙawaye ana neman mafita. Kowa da irin shawarar da yake kawowa gashi lokaci ya ƙure ita tanayin mamaki a inama ya haɗu da matar da har zasuyi aure.......? Ɗaurin aure ranar juma'a yau saura kwana 4 , wace ce zai aura.......? Wace ce.....׳ ita..........??? A iya sanin da tayi mishi bashida budurwa dan kullum saita zindire wayarshi tayi bincike amma ba wani alamar soyayya , ashe suma maza sun iya munafurci....? Hmmm maji dai.

   Hafsa abun yaci tura alhamdu ta kakarewa malam. Itama tana can sun jagalgaleta sun kaita asibiti saboda ciwon hannunta. Sai masifa takeyi itafa lafiyanta qalau duk wanda ya taɓa mata magani zatayi ma mutum uwar watsi..... Gata nan dai suka watsar a asibiti kamar asarar noma , muje gaba daga baya maji me likita yace..........?

   Jiddah data ishi Yazeed da kira cewa abokanshi yayi ya tafi hutun honey time , ƙaraurawar nasararshi ta doka zaije ya buga lamba tara ya dawo.......

    Shi kuma mai gida Dikko da yayiwa Sharifa faɗa dan toshewar basira sai taje ta faɗawa uwarta Mai gilashi , raɗa ta ƙara yiwa Sharifa tunda ita daƙiƙiya ce. Mai gilashi tace ta dage karta sa shakku fatan nasara.

    A tsagina kuwa , yau tunda na tashi jikina yayi min wani irin sanyi , gani nan dai ni ba mara lafiya ba kuma ba lafiyayya ba , yau komai ya kasa shiga cikina saidai in bi wannan kujera inbi gado. Gajiya nayi nacewa Papi yaje yace Yaya banda lafiya. Babu wani ɓata lokaci shi yazo , Pa-Pi kuma bai dawo ba.

     Gabana ya tsuguna ya riƙe cikina da duka hannayenshi cike da tausayi yace meye ne ? Yayi tambayar yana kallona. Fashewa nayi da kuka tare da ɗora fuskata a saman kanshi nace nidai banajin daɗi inajin wani abu yanamin babu daɗi kamar zan rasa wani abu a rayuwata , murmushin ƙarfin hali yayi sannan ya da dawo kusa dani ya zauna. A hankali ya jawoni jikinshi yace babu wani abu da zai faru sai alkairi , ummm ? Ki daina biyewa tunanin zuciya zataje tasa ki shiga ruɗun rayuwa , ba gani ba ? Ya nuna kanshi Kalli kuma ina tare dake , meye zai faru ne ? Munayin zaman lafiya kuma ni nakine ke kaɗai. Tou tayama kike tunanin zaki rasa wani abu mai muhimmanci bayan ni ina tare dake , ai kinsan bazan taɓa rabuwa dake ba har abadan duniya , ki kwantar da hankali ki daina wahalar saƙa tabarmar kabar da bata dace da zamanki ba gimbiya Sultana. Idan kinayin kuka hankalina tashi yake tsikar jikina duk ta mimmiƙe , hawaye basayin kyau a wannan kyakkyawar fuskar. Kuka bai dace da rayuwarki ba. Ke kiyi shiru bara ni in miki kukan tunda kina so kiga hawaye a fuska yana zuba. Ah ai sai inyi ke ki huta , baki san ba'asan mai ciki tanayin damuwa ba ? Ko so kikeyi ki haihu ne ? Yayi maganar cikin sigar zaula. Nace ey , hmmm kima ƙara dagewa kina da sauran kwanki zai kai 90 da Allah kiyi shiru ya ƙarasa yanamin hararar so, tou naji kawomin wayata , tashi yayi ya ɗaukomin wayar , bayan ya bani ya zauna ya sake riƙeni. Kowa dai daga ni harshi muna saƙa wani abu a zuciyoyinmu. Wayar Inna na kira babu daɗewa ta ɗauka , bayan gaisuwa mukayi fira da ita lafiya lau babu wani zage²n nan , kuma na haɗata da Dikko shima suka gaisa cikin mutunci , tace ina Pa-pi ? Yace ya fita yanzu. Wai jiya ba'azo dashi ba.

  Me yasa shi ba'asan kawoshi ne wai ? Dikko yace insha Allah Ashiru zai kawoshi bayan la'asar , har sai wannan lokacin ? Kubar shi bana so tunda ba zaizo min yini ba. Ashirun ne baya nan idan ya dawo zasu zo insha Allah , har suka gama wayar babu wani alamu na rashin mutunci kowa ya ajiye waya da farin ciki.

      Ni kuma kuka naci gaba dayi , yace bari fa ganin ina baki haƙuri ni kinsan abu kaɗan yake ɓatamin rai kodai kiyi shiru ko in tafi ko kuma ke kibar ɗakin nan sai ki zaɓa , nidai gaskiya bazan yi shiru ba , kasan yadda nakeji ne wai ? Sannu yaimin tare da tashi ya fita nima na miƙe nabi bayanshi har ɗakinshi......









  *ZAINAB ABBAKAR MATAWALLE. Ina godiya sosai da saƙo uwar gidan KWARATA...*

06/02/2019

JAMILA MUSA…
[2/14, 12:12] ~M K: ⚜ BRILLIANT WRITERS ASSO ????
-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-

           *KWARATA RETURN...*
  _{{Kalu bale gareku matan aure}}_

Rubutawa…
JAMILA MUSA…

   *SAI NA AURI D ' K*

???? —— 9

    A palo na sameshi zaune saman kujera. Ci gaba nayi da kuka na nufeshi. Hankalinshi yana saman wayanshi yace so kike dai in zaneki ko ? Kusa dashi na zauna nace baka san ya nakeji ba. Riƙoni yayi da hannun da wayar take riƙe cikin tausasassar murya yace baki so in zaneki ne ? Yayi tambayar yana kwantar da firgitaccin idanuwanshi masu saukar da kasala. Kaɗan na kalleshi a kasalance na ɗaga mishi kaina alamar ey. Yace to shikenan jeki ciki ki kwanta ina zuwa. Miƙewa nayi na riƙo hannunshi ina janshi , ba tare daya kalleni ba yace ya wai meye kuma ? Ban bashi amsa ba naci gaba da jan hannunshi , taƙaitaccen kallo yayi min sannan ya tashi muka shiga ciki tare.

    Cike da farin ciki Yazeed ya isa gidan Rabiya. Yau ciki aka shiga kasancewar ita matar gida bata nan. Yazeed kuwa tun a waje ya ɓalle botiran gaban rigarshi yana nuna yanayin haɗama. Kai tsaye ɗakin da aka bawa ita Jiddah a ɗakin ta wuce da Yazeed , suna shiga ya rumgumeta suuuu suka sulale saman gado gaba ɗayansu sunayin farin ciki tare da nunawa junansu kowa yayi maraicin kowa.

   A gaggauce dai aka shiga gabatar da wasa. Ya nemi yaddar gado da kuma sa'ar makoma sai addu'a na gaba ya samu nasara mai girma. Danshi a tunanin shi a filin wasa ake. Wasan yau yafi ko wane wasa martaba da mutumci a wurin Jiddah , kasancewar an samu wadatuwar fili da tsaftatuwar muhallin da akeyin wasan. Yazeedu kuwa ya ɓata manyan awowi kuma ko wace awa minti da seconds ya bada lafiyayyen naushi mai zama a zuciya har abada. Jiddah ma ta mayar da martani domin ita dama tuni Yayanta ya gogar da ita kuma ta ɗauki karatu.

 Rabiya kuwa tunda Yazeed da Jiddah suka shiga ita ta iso gidan , biyosu tayi tana lafiya ? Ina ne zataje da namiji ? Duk babu wanda yaji bare kuma yasan tana magana , suna shiga suka turo ƙofa garam har aka bige ma "yar sa idon banza goshi. Ai bawai Jiddah taji kunya ba ita Rabiya itace taji kunya dan haka ta koma ɗakinta tana neman mafita.

Taya zata iya furtawa Momy wannan zance ? Shedar zina wahala gareshi. Shin wai waye ma yace mata suna aikata saɓo ? Kuma ita bata kamasu sunayi ba , tou dan kawai sun shiga ɗaki ? Ta yuwu wani abu ya faru , sai saƙawa takeyi tana warwarewa lokaci² kuma tana kallon agogo kamar mara aikin yi har Yazeed ya fito , sai yanzu ta gane Yazeed. Shi ɗaya ya fito Jiddah bata biyoshi ba , tou meya faru ? Me sukeyi a ɗaki tsawon awowi 2 har zuwa 3… Ta shiga 3 zafa a samu matsala…..

   Saida Yazeed ya wuce itama ta fito ta nufi ɗakin Jiddah. Kwance ta sameta riƙe da wayarta tana ta latse². Da hannunta ta nuna da yanayin karta shiga haƙƙinta cikin warwarewar haruffa tace am Ji-dd- , ah Jiddah am dama nace lafiya naga Yazeed ya fita ? Ba tare da Jiddah ta kalli Rabiya ba tace lafiya qalau kawai kaina ne yake min ciwo ta ƙarasa maganar tana nuna kanta. Ɗan yatsina fuska tayi tare da ajiye wayar ta taci gaba da cewa gashi gida ba kowa kawai sai nayi ma Yaya D ' K waya ina buƙatar magani , shine fa ya aiko abokinshi ta ƙarasa maganar tana watsa hannunta....

  A ɗan tsorace Rabiya tace Dikkkkkkkkkko ? Ta kira sunanshi da mamaki cikin jan kalmomi wurin faɗar sunan tare da warware kaf ilahirin gininta. Ummm Jiddah ta faɗa tana jinjina kanta alamar gasgatawa. Rabiya tace taf Dikkon ? Jiddah tace shifa. Fuuu Rabiya ta fita , murmushi Jiddah tayi tare da cewa ai nasan idan na shigo dashi a tafiyar dole zai fito yayi masifa ya tilassa ayi auren , ba jiya naje muyi magana ba shine ya basar dani yana waani dariyar banza , An mata rigima , rigimo. Dariya ta sakeyi kaɗan tare da nunawa da "yan yatsunta sati biyu cif zanyi nayo waje. Wata 3 idda a cikin wata na huɗu zamu tare a sabon gida. {{ G R A }} a wata na biyar kuwa Caca zata kama gabanta , Pa-Pi zai zama nawa , wama ya sani ko jinina ne aka kai can.....? Da yanayin tunani tace babu shakka Pa-Pi nine uwarshi shine yake ƙwaƙwata , oho dai hakan ma bazai hana in kasheshi ba.......

 A tsagin Rabiya kuwa tunani takeyi , meye tsakanin Dikko da Jiddah ? Wane irin magani ne ya bada a kawo ma Jiddah ? Ciwon kan ƙaniyarta ? Karfa su maida ita wata gwanjon bisa titi , tana can tana huɗɗoɗinta suyi ta wucewa ba tare da tasan so adadin da ake wucewa ba. Anya Dikko yana da gaskiya ? Kardai zagayewa yakeyi idan bata nan.....? Har zata kira Momy ta fasa kawai ta kira Dikko. Babu daɗewa ya ɗauka ko gaisuwa babu tace yazo yanzu²n nan tana nemanshi. Magana yayi sannan ta bashi amsa da cewa kawai kazo nace idan kuma ni inzo tou... Magana ya sakeyi ita kuma tace shikenan kayi sauri ina jiranka.

    Dan Allah kaje tare dani. Cikin faɗa yace wai ina ne zanje dake ? Saida nayi kalar ban tausayi da marainiyan murya nace dan Allah. Baimin magana ba ya ɗauki wayoyinshi , shikenan tunda bara ka fita dani ba Allah yasa ka dawo ban..... Bakiyi me ba ? Gyara bakina nayi ina kallon ƙasa , bai sake kallona ba yace zo muje. Da sauri na wuceshi na tafi ɗakina , hijabi kaɗai na ɗauka ko wayana ban tafi da , nayi waje. Pa-Pi shima biyoni yayi yana kuka jaije.... Kafe kai yayi shi bazaije da Pa-Pi ba , shi kuma Pa-Pi riƙeni yayi idan ba'a zuwa dashi nima babu inda zanje. Dikko yace ka sakarmin mata kaji ? Yayi maganar yana zaro mishi ido. Da ita zanje kaine bazan tafi dakai ba. Riƙeni yayi Momy karci tafi ci barni. Dikko yace kai so nawa ka tafi ka barta ɗan rainin hankali sakarta nace maka. Kamar an matsi bakinshi yace kaicuwa jakuje....? Ya faɗa da yanayin tsoro ! Yaci gaba da cewa kuma fa'a cuwa da Pa-Pi ya ƙarasa maganar yana ma Dikko wani irin kallo haɗe da murmushi. Kete Momy ce cinyi kuka , jinjina kanshi yayi sannan yace cima Yaya ce yayi kuka ya ƙarasa yana dariya. Nuna kanshi yayi sannan na nunamu yace ni kuma can muku dayiya wayyayi. 

 Yadda yayi abun ne yaba Dikko dariya , yace ni kuma wallahi in zaneka. Dariya Pa-Pi yayi cewa kowa ce yayi kuka wayyayi. Yana ƙara yawan dariyar wai zaiga Yaya yanayin kuka. Wata irin mummunar faɗuwar gaba naji lokaci guda wata irin zufa ta ketomin , murya a sanyaye nace ma Dikko nidai na fasa zuwa. Dariya Pa-Pi yayi tare da cewa wayyayi Momy taji tsoyo. Dikko yace keda Allah manta dashi taho muje yayi maganar yana jan hannu na , kinga sai kirana takeyi zo muje kinji....? Ƙwacewa nayi nidai kawai kai kaje , cikin rarrashi yace ke An mata haukan Pa-Pi zai tsorataki ? Da Allah zo muje yana ci gaba da jana. Fizgewa nayi nidai na fasa , cikin ɗaga murya yace kada Allah yasa kije kuma tunda har kika ce zaki kika fasa , idan na fita sai 2n dare zan dawo.

   Jiki a sanyaye na kalleshi. Ɗagamin gira yayi tare da kwantar da idonshi na haggu , a hankali ya fidda sautin sumba cikin natsuwa da salo mai tada hankali yana ƙara riƙe ganin idanuwanshi , duk iya masifar sa idonka bara ka gane abinda yayi ba , wannan karatun daga ni saishi kaɗai muka fahimci yaren juna. Ajiyar zuciya nayi kaɗan cikin ƙarfin hali , shi kuma ya ɗagamin hannu ya wuce. Tunda na fasa zuwa ya tafi da Ashiru....

  Dariya Pa-Pi yaci gaba dayi yana riƙe da hannuna har muka shiga ciki. Saida muka zauna na tambayeshi wai waye yace mishi zamuyi kuka ? Zama yayi kusa dani yace wai a cikin wayar Yaya ya gani , cike da ɓacin rai nace dan ubanka a wayar aka ce zamuyi kuka ? Kallona yayi ya ɗaure fuska shima da yanayin fushi yana hararata wai saiya faɗawa Yaya nayi zagi ya zaneni , shima ai jiya Yaya ya dakeshi da yayi zagi wa kare.... Tsoki nayi sannan nace ya tashi ya bani wuri. Ƙin sauka yayi saidai ya juyamin baya wai yama fata dani. Kaje ka ɓatan. Ba'a ciyyawa dake.... A palo na barshi na koma ciki , kasancewar zufar da naji inayi dole tasa naje nayi wanka. Ina fitowa kuma masassara tace gata nan zuwa , dakel na iya shafa mai kaɗan sannan naɗan kashe masƙin man da fauda , kayana na saka na kwanta.

    Dikko jin kiran waya yayi yawa , ya fara faɗa wai ita Rabiya bata da haƙuri gashi yana tafiya zuwa wurinta amma ta dameshi da kira. Wannan ɗan abun harya hasalar dashi danshi baida wahalar fushi amma yana saurin sauka. Cike da ɓacin rai ya ɗauki wayar a inda take ajiye amma sai yaga Inna ce take kiranshi. Ɗauka yayi da sallama ba Inna ce ta ansa sallamar ba mijinta ne ya ansa dakel yace kana ina ne ? Saida Dikko ya kalli hanya sannan ya faɗa masa ta inda yake. Tou wai kazo gidan Kaka dakai da Sultana. Lafiya Dikko ya tambaya ? Umm ai na tura maka saƙo ka duba , a , a , wai meye ne....? Baiyi magana ba ya ajiye waya.

  Wai Allahna , Inna ta tafi itama..... Lahaula walaƙuwat illabillah shine abinda ya furta. Dakel ya nunawa Ashiru ya koma gida , taya Ashiru yaci suka dawo gida , dawowarsu ne shi Dikko ya shigo ya samu Sultana tana wanka , ɗakinshi ya koma yana tunanin ta wace hanya shi zai iya furtawa Sultana wannan saƙo....? Ita ya zata kalleshi ? Saƙon mutuwa baƙin saƙo ne , har abadan duniya baraka manta da wanda yazo maka da wannan aike ba. Ya juya ya rasa yadda zaiyi , ko Ashiru bai faɗawa ba. Wane hali An mata zata shiga ? Zatayi kuka kamar zata cinye ranta ya sani , shima kuma za shiga tashin hankali , duk duniya a wannan rayuwa idan akwai abinda ke tada mishi hankali yake firgita mishi tunani yake sashi ɗimuwar rayuwa da manta shi ɗin ko waye wallahi bai wuce tashin hankalin Sultana ba. Shi kaɗai ya isa yayi mata amma idan wani ya taɓota bayan shi ? Tou fa lallai zaici gari da yaƙi..... 

     Kira ne yake ta shigowa a wayata babu ƙaƙƙautawa. A wahalce na miƙa hannu na dakel dan ɗauko wayar dake saman bedsite. Kafin in ɗaukota a hannuna tuni ta tsinke har wani kiran ya sake shigowa ya fita. Saƙo ne ya shigo dan haka ban fara duba rashin kiran dana samu ba na fara da saƙon.

    _Ke Sultana an faɗa miki uwarki ta mutu baki tahowa ? Tou ta mutu can wurin siya ma ɗanki abun wasa , mota tayi ƙoli² ta dakota da ƙasa sannan tabi ta kanta ta wuce. Ba wata tsiya nake kiranki ki bani ba bare kijamin aji ke surukar gwamna..._

  Yayar Inna ce surukar Sultan wanda zan aura da farko tasa aka fasa auren ya auri "yar ta. Duk me ya kawo wannan dogon bayani tou ? Salati nayi na sanar da mahalicci na daya isa da rayuwata. Dakel na iya gano number Dikko a wayata na fara kiranshi komai bana iya gani kasancewar inaji na a cikin wata irin baƙuwar rayuwa. Shikenan na zama marainiya gaba da baya , babu uwa ba uba , Allahu Akbar , tabbas ubangiji shine mai iko akan komai da kowa.

 _Kema ɗayar mara zuciyar_ 

  Itace kalmar data fara dawomin a cikin kaina , ina hango Inna palonta a daren jiya......

  _Me yasa shi ba'asan kawoshi ne wai ? Har sai wannan lokacin ? Kubar shi bana so tunda ba zaizomin yini ba._

   Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un , wani irin ihu na kurma , na fara magangu na sakin layi , kai... Wai Allahna , innalillahi wa'inna ilaihir raji'un , nayi kuka sau adadin yadda naji ciwon mutuwar Inna a zuciyata , haba Inna sai kuma kema ki tafi ki barni ? Shikenan ? Tou wai mema yasa kika je siyen wani abun wasa ? Waye ya aikeki ? Haba Innata meya sa²..... ? Kema shine dai kika tafi kika barni ? Gaskiya nadai zauce nayi maganganu marasa daɗin rubutawa. Dikko yayi maganar shi banama jinsa dan gaskiya bana iya gane abinda yake cewa. Kukan da nakeyi ne shine ya tayar mishi da hankali shima yaita kuka kamar ƙaramin yaro wai zai mutu. Shi baya so yaga inayin damuwa , in rufa mishi asiri nasan bashi da lafiya , shima yaji ɓarin maganganu kamar aradu ta faɗo. 

    Ko a gidan rasuwa haka naita bori ina ihu mai tayar da hankali duk wani imani , babu wanda ya damu dani bare yace ke daƙiƙiya ki gyara kalamanki ko kiyi ma mutane shiru , Kaka ce kaɗai take rarrashi na , sai Pa-Pi daya riƙeni yana ta ihu wai waye ya dakeni. Yayar Inna ni bansan abinda yasa bata ƙaunana ba , bansan me nayi mata ba ta tsaneni da zafi haka. Ko waye ya rasa yayi kuka , nidai a duniyar rayuwata banga abinda yafi rashin iyaye raɗaɗi da ciwo ba. Inajin yadda aketa faɗar yadda mutuwar Inna ta kasance. Wai bayan tayi waya dani a yadda shi mijinta ya basu labari.

    Baiwar Allah ashe abinda tayi mana jiya ya dameta. Ta faɗawa mijinta cewa gaskiya Dikko jajirtaccen namiji ne , kaifi ɗaya ne ita a yadda ta fahimta , tsaye yake babu munafurci a lamarinshi. Idan zaiyi kawai zaiyi idan bayayi ko za'a mutu zai tsaya a wurin. Wai tace masa idan yaji fushi ya sakar mata "ya , shine yace bai gaji ba , wai me yake nufi ? Ta ɗauki biro da takadda tayi rubutu akai , bayan ta gama sukazo gidan Kaka dashi da ita. Yace shi baisan abinda ya kawota ba , haka kuma baiji firarsu ba. Yau kuma tace a kawo mata Pa-Pi , wai shine taje ta sissiyo mishi abun wasa wai tasan Dikko zaiyi farin ciki dan ta goge damuwar data saka mishi a daren jiya. To shine fa ta gama sissiye²n tana zuwa wurin motar ta mota yabi ta kanta ya wuce.....

   Ni ɗaya a wurin Inna , banda Ya banda ƙani haka nake ni ziƙau ina , ba uwa ba uba ba Yaya ba ƙani. Ga "yan uwan Inna ni basa so na , ahalin Babana kuma gasu dai ga yadda suke , "yan uwan Dikko sune suketa bani haƙuri , bawan Allah shi kuma ya kasa zaune ya kasa tsaye sai turowa Rabiya saƙo yakeyi wai An mata tayi haƙuri ta daina kuka , bayan wani lokaci kuma ya rubuto cewa wai shi yana nan bazai tafi ya barni ba insha Allah , hmmm haka dai yaita rubuce² har akaje aka rufo Inna aka dawo.

  Duk ahalin Dikko sun tayani zaman makoki har Momy. Mai gilashi da zugar ƙawayenta "yan tasha amma banda Halima tayomin gayyarsu zuga guda. Akayi ta gulma na wai ni na tara karuwai a wurin rasuwar Mamana , Nabeela ma tazo kuma tayi kuka kamar yadda taga inayi itama , ta tausayamin sosai , tamin sannu da rashi. Sati ɗaya nayi a gidan Kaka nan nake kwana , Dikko kuma idan yazo sai dare sosai yake tafiya dashi da Pa-Pi.

   "Yan uwan Inna kuwa bawai ta mutuwarta suke ba , abinda ta bari kawai suke ta lissafi. Babu kunya bare tsoron Allah suke farfaɗo suturunta kowa yana cewa ya kamasu , ita surukar Sultan itace take maganar kayan ɗaki wai dama wallahi ita kafinta yayi mata ha'inci kullum tana fama da "yan ƙwanƙwashe² gado ba kirki , kujerun ma duk sun rubza kaza². Shin aisai ta kwashe ita da zata tsaya tsaron duniya.

  Ranar da akayi addu'ar 7 a ranar na bar gidan saboda wulaƙancin da sukemin. Da zan tafi ne Kaka ta bani wata takkada cewa Maryam gashi mahaifiyarki tace a baki. Meye a ciki ? Nima bansan ko ta miye ba , tadai cemin zata turoki ki ansa , amma itama kanta gaskiya batayi tunanin zaki anshi takardar bata a raye ba. Ansa nayi nabar palon. Dikko da kanshi ya ɗaukeni muka koma gida.

  Nidai babu wanda a cikinsu yayi min magana game da duk wani abu daya shafi Inna. Basa gabana dan ni basu ne damuwata rashinta shine ƙaton ciwon dake damuna. Suke san abun duniya wanda har ya gusar da imani daga zukatansu , ana kukan mutuwa suna lissafin abinda zasu gada. Tun a mota Dikko kemin nasiha har muka je gida. Da kanshi yayi ma Pa-Pi wanka ya kwantar dashi. Duk inda na juya Pa-Pi sai yayi ta kallona sai kuma ya kalli Dikko.

   Har bacci ya fara fizgarshi ya buɗe idonshi yace cinci abinci ? Murmushi nayi kaɗan tare da nuna mishi da kaina alamar eh. Shima murmushi yayi ba tare daya sake magana ba ya rufe idanuwanshi yaci gaba da bacci. Nima saida nayi wanka sannan naɗan taɓa fura. Saman gado na koma na warware takaddar da Inna ta bayar a bani , Dikko kuma yana tacan gefen Pa-Pi yana latse² a wayarshi...... Ga abinda Inna ta rubuta a takadarta.

 _Aminci Allah , yaddar Allah wadatar zuci zaman lafiya da kwanciyar hankali su ƙara tabbata a gareki ɗiyata...._

Sultana ki gafarceni a rayuwa. Nasan bakyajin daɗin abinda nake miki… ? Ni wallahi duk abubuwan da nakeyi ma Dikko dake banyi da nufi ba. Saidai ina hasko miki rayuwar gaba. Ke ɗaya na haifa a duniya baki da Baba haka kuma baki da “yan uwa da kika fita ciki ɗaya dasu. “Yan uwana kuma bakya gabansu , daga ni saike muka rage a duniyarmu , ina neman yafiyarki dan Allah , ki yafemin kuma insha Allah bazan sake ba…

         _Amma ki san wani abu a rayuwa. Nifa ba san Dikko ne banayi ba , a , a ni iskancin shi ne gaskiya bana so. Idonshi ya waye da yawa. Ni gaskiya a tsarin rayuwata bana sha'awa ko muradin namiji mai buɗewar ido da gogewar rayuwar irin na Dikko , amma ya za'ayi tunda haka Allah ya rubuto ? Nidai ina neman yafiyarki karki ɗaukeni a matsayin uwar data fi san kanta akan "yarta. Ban hanaki zaman aure ba haka kuma ban tilasta ki kashe ba. Saboda aure dai sunna ne mai ƙarfi daga cikin sunnonin Manza Allah S. A. W , kamar yadda ayoyi da dama suka nuna mana:•_

   _Allah {{ S W T }} yana faɗa a suratul rum cikin alqur'ani mai girma. "Kuma daga ayarSa ne ya halitta daga garemu mataye domin mu samu natsuwa daga garesu. Kuma ya sanya tsakaninmu ƙauna da tausayi , haƙiƙa wannan aya ce ga ma'abota hankali. "Wannan aya ta tattara duk wani ma'ana na aure a cikinta. Saura namu farfasawa mu auna mugani , shin ma'anar aure da abinda yake cikinsa kuwa kamar yadda Allah ya nuna mana hakan mukeyi. Da farko Allah ya ambaci ma'aurata da ababen samun natsuwa duk anan ya kawo jinsin mata ne. To amma ai mun sani idan har macen bata samu natsuwa ba ? Shi kanshi namijin natsuwarshi ragaggiya ne. Tambaya anan ta ina ma'aurata zasu sami kwanciyar hankali.......?_

Hah. Ci.. Nayi tare da yin murmushi mai ciwo na goge hawayen dake bin idona. Ina ci gaba da kuka. Naci gaba da karatun takardar Inna…..

Na farko:• a samun natsuwar aure shine hadafin yinsa. Bai taɓa yiwuwa aure ya kasance an ginashi kan wani hadafi sannan ya zamo ɗorarre. Wannan shi yasa Annabi {{ S A W }} bayan ya zayyano kaso na matan da ake aure. Ƙarshe yace “na hore ku da ma’abociyar addini. To haƙiƙa abun nufi anan shine ba wni hadafin da zai haifar maka da cikakkiyar kwanciyar hankalin aure sai hadafin tarayya domin Allah…

  _A cikin aure mai kawo natsuwa kenan. Haƙiƙa a yau munyi sake tare da watsi da haƙƙin junanmu ta yanda takei har wasu abubuwan ma an shafesu daga rayuwar auren sai wajen mutane jefi² mun barwa turawa wanda kuma mu addininmu ne ya koyar damu su. Ina horonki da ki zama mai biyayya , ki zama mai kunya da juyawa abin duniya baya. Kiyi kara ki zama mai haƙuri. Rayuwar gaba ɗayanta haƙuri ce , ki guji yaɗa sirrin mijinki wa kowa da koma waye. Kar kiyi abinda bakiyi shawara da mijinki ba , ki kiyaye fushin shi ki guji ɓata masa rai da gudun duk abinda baya so idan har bai tsaɓawa Allah ba. Haƙuri׳ ki zama mai haƙuri da biyayyar aure kinji uwar masu gida. ?_

   _Ki kiyaye munanan kalamai. Karki kuskura ki jiyar da kunnuwan mijinki ɓatattar magana daga gareki. Magana mara daɗi ko muni kiyi ƙoƙarin kare kunnuwan mijinki dasu. Kar kiyi masa:• ƙarya. Ki kula dashi , ki zama mai tsafta , kar kici amanar shi , banda zargi ki guji abokai , karki raina masa iyaye. Ki kiyaye kuma kisan yadda zakiyu ma'amula da "yan uwansa._

_Kinga wa'anan abubuwan da zan lissafo su ? To ki kiyayesu domin sune ke taka rawa wurin rusa aure matsawar ba'a kiyayesu ba._

   _Rashin ilimin zamantakewar aure , al'adu , rashin binken halin miji , rashin binciken halin mace , matsalar iyayen miji , rashin tsafta , matsalar dangin miji , rashin iya magana , rashin iya ciyarwa , rashin iya kwanciyar aure , rashin adalci , auren kisan wuta , cin amanar aure , ƙawaye , zafin kishi , sata , gulma , wayar miji {{ phone }} , rashin lafiyar miji wajen gamsar da iyali da itama rashin lafiyar macen wajen gamsar miji , sharrin boka. Ke kina tunanin ni bana sanki ? Taya ma zaki yadda ki fara wannan tunanin ? Tunda kike a duniya kin taɓa ganin uwar data haifa "yarta tace bata santa ne....? Ni ina so ne ki goge da rayuwa ke ɗaya , ki kuma iya haɗiyar baƙin ciki da magance damuwa dan ki zamar da kanki garkuwar rayuwarki. Domin idan yau ina nan gobe bana nan , yadda kike ke ɗayan nan babu abokin shawara ko na bar duniya barakiji wahalar rayuwa da kowa ba. Ina so ne kawai in auno iya girman soyayyarki a zuciyar mijinki. Na gani kuma ni nasan yana sanki dan nayi masa wani abu a abuja. Wallahi nayi tunanin yadda ake faɗar rashin mutunci zaizo ne kawai ya sakeki. Sai baiyi ba kuma nima baimin rashin kunya ko kallon banza ba kamar yadda nayi tunani... Wallahi inajin kunyarki ne , abun nan da nayi muku banyi da nufi ba , yayi ta damu nane banji daɗi ba , shi yasa na fara rubutun neman yafiya kafin mu haɗu dan mashala.Tou dake dashi duk ina san ganinku domin na nemi gafararku , sai kuma kema zamuyi zama na musamman...... sai mun haɗu kafin inyi tafiya_

     _Fatima Salis Abbakar {{ Inna }}_

  Wata irin ƙara nayi tare da cewa da yaushe ne zamu haɗu ? A ina me zaki ce man ne iye ? Cike da tashin hali ya kallo inda nake yace haba An mata wai meye kike haka ne ? Cikin muryar kuka na raunana murya tare da cewa ƙarshena yazo. Wannan kalma dana furta shine yasa Dikko kakkafawa , wani irin birkitaccen ihu na ƙarayi tare da matsawa inda yake , sautin ihun yasashi ɗaukewa gaba ɗayanshi. Da gudu na fita na gayyato Ashiru , cikin tashin hankali muka dawo tare dashi , shi ɗakin Dikko ya wuce sannan yazo ɗakina , haka yaita mishi shaƙe² harya dawo. Ɗan gajeren tsoki yayi tare da cewa insha Allahu saina mutu tunda dai baki bari in zauna lafiya. Fita Ashiru yayi ni kuma na matsa kusa dashi ina kuka , a gajiye ya jawoni jikinshi idonshi cike da hawaye yace wallahi bana san kina ihu , ki ƙyaleni in huta dan Allah. Kwanciya nayi a jikinshi nace na bari. Gefenshi ya nuna min in sauka daga jikinshi in kwanta , sauka nayi na kwanta ina kallonshi dakel ya lumshe idanuwanshi cikin yanayin jigatuwa kiyi bacci , rufe idanuwana nayi hannuna a saman gemunshi.

   Bayan wani lokaci mai nisa ya sauke ajiyar zuciya tare da sauke hannun Sultana daga jikinshi. Wayoyinshi ya ɗauka ya fita a ɗakin. A gefen gado ya ajiye wayoyinshi bayan yaje ɗakinshi sannan ya wuce toilet kai tsaye. Wanka yayo ya fito ɗaure da rigar wanka yana tunane² , shi kaɗai yasan yadda yakejin rayuwarshi da kuma yadda yakeyinta a daddafe. Taƙaitaccen tsoki yayi tare da zuwa wurin wayoyinshi dan ganin mai kiranshi , Sharifa ce. Ɗauka yayi ba tare daya bari tayi magana ba yace yana zuwa....

    Ajiye wayar yayi ya matsa wurin madubi. Kamar mace yaita ƙwasƙwarima , yana gamawa yabi kayan da zai saka ya bulbulesu da tulare shi zaije zance. Kallon kanshi yayi sosai a madubi shi kanshi yasan haɗaɗɗe ne shi ɗin. Murmushi yayi kaɗan tare da ɗan shafa gemunshi da bayan hannunshi na haggu sannan yayi kallonshi na gefen ido mai tabbatar da shi ɗin cikakken ɗan duniya ne. 

   Taf yauma Sharifa ɗif take ta ibi wuta sosai. Har bata iya tafiya sai layi takeyi , ga wasu irin kaya data saka kuma ko breziya bata da , kaf halittar surar ƙirjinta babu wanda baka gani kawai kamar buɗe yake. Full light yayi a dai² lokacin da yayi parking. Dogon kallo yayi mata daga cikin mota inda sukayi zasu haɗu dan yau ba g r a aka haɗe ba. Wasa yayi da fitilar mota ta nufoshi tana rangwaɗa , tana isowa ta wani kama murfin mota ta inda yake ta buɗe , rufe ta da faɗa yayi wai ita wata irin jaka ce ? Haka ta ratso duniya ta taho kowa yana kallonta ? Irin barinkinta zata yi mishi wai Dikko zata runguma , ƙara ƙufulewa yayi dan duk duniya ya tsani ana taɓashi , turata yayi baya da ƙafarshi cike da ɓacin rai yace Dikkon zaki kaiwa hannu eye ? Cikin hayaniya yace kai...... Lallai kin isa yayi maganar yana buɗo duk girman idanuwanshi. Ƙara nufoshi tayi da sauri ta ƙara ƙaddabeshi , ta ɗauka shiru zaiyi ya fara aiko numfashi kamar yadda Mai gilashi ta faɗa , sai taji karatu yasha ban². Da tsiya² ya fitar da ita jikinshi dakel. Kafin ya fito mota ta ƙara komawa ta cakumeshi , kai........... Da Allah ki daina riƙemin jiki , riƙo fuskarshi tayi tana matsar da nata kusa da nashi. Tureta ya ƙarayi da ƙarfi tayi baya. Da sauri yasa hannunshi aljihu ya ciro cingom kasancewar warin sigari da sauran wasu kayan mayen da yaji warinsu daga bakinta zuciyarshi ta tashi.

  Tsalle tayi ta anshe cingom in tasa a bakinta wai yaci daga bakinta , kakarin amai Dikko ya farayi yana matsawa gefe tare da riƙe bakinshi. Caɓoshi tayi ta baya , aiko kamar jira yakeyi ya kakkaɓota ya fara kwallo da ita , saida ya bata kashin bala'e ya shige motarshi yai tafiyarshi ya barta kwance a hanya tana kuka.

   Tsoki yayi tare da ɗaukar wayarshi dake wata ƙara zutt². Yusra ce , reject ya latsa yana gunguni. Cike da ɓacin rai ya koma gida duk saima yaci uwar matan nan dan ubansu , kawai ma dan ana magana dasu zasu ɗaukeshi wani daƙiƙi ? Bari har itama mai turo kanta tsirara zaici uwar ubanta ta sake zuba mishi banzayen hotunanta a waya saiya kasheta..... Ya faɗa yana kaiwa gado harbi da ƙafarshi. Dama su mata ma basu da wayau jira suke ayi musu magana su fara rainawa mutane wayau. Kamar shi ? Sai kace wani sa'ar wasansu ? Shi waccan jakar yarinyar ma zata wani daƙune ? Jinjina kanshi yayi da damuwa yace sai kace wani jaririn da yazo inda aka daɗe ana addu'ar samun shi , kai wallahi ya raina kanshi da har shi wata daƙiƙiya zata runguma. Tuno yadda Sharifa ta kasance a jikinshi da yadda harma ta samu damar tallabar mishi fuska , duk yana ina ? Aikin me yakeyi ina zamarshi ? Aiko wallahi da bai daketa ba har abadan duniya da baida kwanciyar hankali , tsoki yayi tare da cewa duk dai haka ta moremin wallahi...... Balgazar mace. Haka yaita masifa shi ɗaya a ɗaki dama tusa hali bare anci wake. Fushin mutum ɗaya ke sa idan yana fushi yake haɗawa kowa da kowa , wanda yasan anayi da wanda baiji bai gani ba , ai kuma kunsan laifin wani yake hucewa akan kowa. Yau duk wata macen dake cikin wayarshi Sharifa taja musu anyi blocking insu , anyi adding nasu zuwa blacklist. Wato shi harkarshi ba baƙin ciki bajin haushi sabgar Katsinawa.

   Dikko shine ya shiga yai ruwa yai tsaki aka ɗaura auren Jiddah da Yazeed. Rabiya ta labarta mishi komai tsakaninta da Yazeed iyakar abinda ta gani , hankalin Dikko kuwa ya ɗagu domin shi yasan waye Yazeed. Sadaki da lefe har kayan ɗaki shine yayi dan Yazeed yace bashi da kuɗi , Jiddah ta faɗawa Dikko ita ta bada kuɗin aure. Shine Yazeed yace ɓarayi suka sace kuɗin. Andai ɗaura aure amarya ta tare a gidan angonta...... Ita kuma tana lissafin kwanakin fitowarta da ko nawa ga wata zata koma gidan Dikko.

    Hafsa. Duk maganin da akayi ma Hafsa a asibiti hannu yaƙi ɗauka bare asa ran samun sauƙi har zuwa matakin warkewa. Bayan dogon bincike likita ya tabbatar Hafsa tana da ciwon shiga. Cire hannun shine maslaha inji malamin asibiti dan idan ba'a cire shi ba matsalar zatafi haka injisu. An cire mata hannu dai² gaɓa.

 Amisty kuwa kafin ta gama warwarewa Momyn Hafsa tasa aka cafketa. Bayan tasha shegen duka aka tambayeta kuɗi tace babu , a yadda su "yan sanda suka fahimta Amisty tana da damuwa a ƙwaƙwalwarta. Haka suka gogawa Momy bayani dole tasa suka saketa dan Amisty ta samu ɗimuwar tunani. Amma duk wannan bai ishi Momy ishara ba saida ta siyar da gidan iyayenta da gidan Amisty na Qerau. Amisty dai ga hauka ga kuma yawon haya.... Bariki kuma ta kama gabanta , sheɗan ya fita a kanta ya sake sheƙa. Duniyar yanzu ba Amisty take buƙata ba zamanin wasu ne. Haka takeyin juyin ɗan mangwaro ita duniya dawowa take daga rakiyarka da zaran ta raka ka sai ta dawo ta sake raka wani halakakken wanda sheɗan yayi ma tusa a zuciya.

   Halima dai ba kowa bace wannan amarya sai ƙanwar Hadiza. Wata garɗamemiyar budurwa ce takai shekaru 27. An tura anyi ciniki amma bata samu shigewa ba , anyi addu'a an bada sadakar ƙuli da alawa amma abu ya gagara dan haka ta shiga ta fita har gidan uwayen mijin Halima ta basu labari irin uƙubar da take ba ɗansu. Nan fa dangin miji suka fara cacai² , akai ta faɗo baƙin halinta , raina dangin miji uwar miji raina miji da baƙar rowarta. Itama dai Hadiza ta kawo nata sharrin ta raɓa da "yar ta² barikin dai ta samu aka siyi kanwarta. Shima Abdul haka aka ɗaurashi kunsan maza basa wuce tayin mace kamar almajiri ne da sauran abinci... Cikin ikon Allah yaga yarinya kuma tayi mishi. Gata "yar kyakkyawa kamar Rabi'atu Aminu Maman Dee. Mai kunya da laushin magana kamar Asmeenat Zeeyan. Mai kyawun kallo da iya murmushi kamar Aunty Musa Qerau. Ga iya wanka mai ɗaukar hankali kamar Hauwa Musa Qerau. Ta iya adon lalle mai burge kamar Zainab Abbakar Matawalle haka ta iya gyaran kai kamar Fati M Ga magana da salon ɗaukar hankali bakinta kamar Ruƙayya Sharif Maulaya hassan. Kai tafa haɗu haɗuwar haɗewa , idan zatayi kallo tanayinshi ne da salon bugun zuciya kamar Rabi Musa Qerau. Bari dai in daina zugata haka nan karta kamo Halimatu Musa {{ Uwa }} haɗuwa.

Abdul da yaga yarinya tayi mishi sosai dan haka suka antaya a duniyar munafukar soyayya. Ita kuma Hadiza kullum tana liƙe da gidan Halima tana ƙara kakkaɓowa "yar uwarta sirrin gida. Har daren ɗaurin aure duk suna tare da Halima sunajin hukuncin da zatayi wa amarya. Da taji saita dokawa "yar uwarta waya suyi shawara su san hanyar da zasu hudowa lamarin. Ina wanda ya raba faɗa bai kallo ba , sun haɗu sun haɗa ƙarfi da hikima duka ɗaya zasuyi su zare Halima a gidan miji idan tayi wasa saboda sunyi mata ƙofar raggo , ita bata sansu ba , su kuma suna tare da ita suna shirya mata gadar zare.

   A kusa da gidan Halima Abdul ya kama haya ya ajiye amaryarshi Amina. Tunda bai shirya aure ba hawoshi yayi kai tsaye. Anan fa akayi uwar watsi , Halima ta fara bori da wallahi² data tabbatar amarya ƙanwar aminyartar ce. Nanfa fitina ya ɓalle suka kashe santa aikata ruwan bala'e babu ƙaƙƙautawa , Hadiza ta biya kuɗi ta ibo hayar "yan daba tace duk matar data sake cewa tuf ko ta leƙo daga gidanta idan dai ba Allah sa alkairi ta fito ba aradu su yagewa koma waye baki. Dan su sunaso suyi hidimar biki cikin natsuwa , a gefe kuma ga masu DJ sunata wulakanci da waƙoƙi na habaici umarni daga Hadiza , c b n gidan kuɗi. Can naga sabbin kuɗi suna wali bisa iska. Shagali wanda ko a bikin Halima basuyi irinshi ba. Hadiza kuwa a yanzu zasuci na ƙurya da bakin gado. Ballagazar mace ga ƙarsheki.

Tunda Mardiyya ta haura katangar maƙabarta ta ibi santa. Mota tahau ? Da ƙafa taje ? Oho , candai Yola ta yadda zango , hauka tuburan marar gane matsayin ido da ciki. A gidan mahaukata aka ajeta shine suka shiga neman "yan uwanta , bayan an samosu aka danƙata wa iyayenta , sai suyi ta magani har a dace , wa gari ya waya ? Ruwa ya ƙarewa ɗan kada bai gama wanka ba.

 Amarya Jiddah kuwa an wani saki baki aci kazar amarci. Ai a ranar ango bai kwana gida ba. Tou dama me zai tsaya yi ne ? Abinda za'a tsaya danshi ayi murna da ɗoki ai ansanshi tun a gida. Saboda shi dama za'aci kazar tou yabi ya wuce , anyi karatu an tusa feji , allonta kawai take wankewa gwargwadon yadda ta biya karatun. Sati ɗaya da "yan kwanaki ta fara zance tafiya , Yazeedu yace ina ? Ai yadda baya tare da D ' K a yanzu gara ma yayi ƙoƙarin riƙe auren "yar uwarshi yasan ya mishi sauƙin gani. Haya² ta taso da rashin kunya ya nannagawa banza duka na fitar misali. Wannan shine horonta duk idan ta sake zance saki....

 Duk wannan sa'a da Sharifa ta gwada na shawarar da mai gilashi ta bada taga ta faɗi ? Bata daddara ba. Dan haka ta faɗawa Mai gilashi Dikko ya rufeta a waya. Mai gilashi tace mafita na ƙarshe kizo makarantarmu ajinmu ɗaya da matarshi kashin bala'e zaki bata , daga nan idan kika daki matar zai nemeki danjin dalili , sai ki faɗamin ni kuma zan baki shawara na ƙarshe. Idan kika daketa zataje ta faɗawa mijinta , tana faɗa mishi shi kuma zai nemeki danjin ba'asi. Yana kiranki ke kuma ba ɗauka zakiyi ba sai ki kira ita Aunty Bilki ki farfaɗa mata maganar da zan faɗa miki idan kinyi dukan. Daga nan zatace kizo gidan gwamnati. Idan kikaje government house sai ki kira Dikko ki faɗa masa cewa kinga kiranshi bakya kusa ne sai yanzu. Zai ce me matata tayi miki kika daketa ne ? Sai kice ai ina nan gidanku ma. Fuuuu zai tako mota yazo , ai kinsan dai dama bawai wani can² yake santa ba suma nashi familyn basa santa. Ai nanfa za'a haɗu a bata rashin gaskiya duk idan kinyi dukan zan faɗa miki abinda zaki ce ya haɗaki da ita Sultanar.

  Sharifa tace amma kina ganin wannan ba matsala ? Mai gilashi tace haba Sharifa idan da matsala harna faɗa miki kiyi ? Matsalata ai taki ce. Dole mu haɗu muyi maganin matsala kodan ci gabanmu. Sharifa tace idan aka faɗi fa ? Mai gilashi tace shikenan sai ki sake ƙawar shawara. Sharifa tace tou shikenan. Batayi tunanin matsalar da hakan zai haifar ba......

      Hmmm su kuma zugar gidanmu duk abun nan wai sai yau suka zomin gaisuwa. Ƙwansu da ƙwarƙwata babba da yaro babu wanda aka rago har iyaye , jimillarsu dai su sattin da wani abu. Kacaniya kenan , gaskiya nayi farin cikin ganinsu sosai har farin ciki na yaƙi ɓoyuwa. Haka suka shigo wurjanjan kamar an ɓalle garken shanu. Kowa da irin siffarshi. Kai gaskiya Baba ɗan bala'e ne , wannan kwanyaman "ya "ya inama amfaninsu ba ɗaya na zaɓe. Haka suka shigo palo sukaita hayaniya , har bakajin maganar wani. Abinci nasa aka kawo musu. Ɗiff kowa ya ɗauke wuta suka fara caccaka. Gayam². Gurum² taunar nama. Abinci kuma nakai karo suka ci gaba da surutu......

       Da hada "yan gidan Baba ƙarami zamu zo sukace basu zuwa. Cacai² gardama ta buɗe , bafa haka sukace ba ku faɗi gaskiya ni nafi san abinda mutum ya faɗa ana faɗinshi. Daga maida magana sai faɗa , har ana neman bugawa. Haƙuri na basu dakel dai suka haƙura , duk lemunan da aka kawo musu kowa cikin jakarta tasa abunta wacce bata da jaka ta matse abunta a hannu. Tashi sukayi wai zasuje su zagaya gida dan kar suje wata rana anayin labari su kasa ƙarda komai. Kamar wata geliya haka nabisu babu inda basu shiga ba a gidan sai ɗakin mai gidan ne kaɗai basu shiga ba. A store kuwa buhun garin kwakin nan suka jawo , kalluba suka cire ba tare da izinina ba suka hau rabo , wai wannan ai kiran tsiya ne wai meya kawo fir'auna aljanna ga gidan wuta. Haka dai sukai ta zambaɗa iskanci suna maganganun irin nasu na "yan cikin lungu. Duk abinda suka gani yayi musu a store sukayi gaba dashi. A ɗakina kuwa cewa sukayi in basu zazzagar kayan sawa. Fa'iza kuwa cewa tayi saidai wasu a basu kaya wasu takalmi wasu jikkuna , kuma wai waye ma nake bawa kwance gasu ? Duk zasu sakamin numbobinsu idan zamu koma sabon gida a basu kayan tsohon gida , weldrop na buɗe na fiddo musu kaya sukai ta zaɓe. Ciki kuwa hada rigunan da Dikko ya kawomin tsaraba suka ɗauka. Nan dai suka yini sai dare suka tafi nayi musu hasafin kuɗi masu nauhi suka kama gabansu....

  Kwanan "yan gidan biyu da zuwa Dikko yana kallon hutana na a waya ya karkatomin waya wai insa mishi wannan rigar yau. So ɗaya na kalleta nace na bada ta. Sake zuƙo hoton yayi yace wannan kalli. Ba tare dana kalleshi ba nace wannan ɗin. Haba yarinya wasa kikeyi , wallahi da gaske na bayar da ita , cike da ɓacin rai yace waye yace kika bayarmin kayata...........?

     Kar kuji Dikko yana da kuɗi kuce ya tsaya akan wani banzar riga yana surutunshi. Duk iya kuɗin namiji ke mace yafa kamata da Allah ki riƙa abu da lissafi. Tunatarwa ne. Duk irin kuɗin mijinki baifa kamata haka ba gaskiya , ta yuwu kila a jikin wata ya gani tayi mishi kyau ya siyo shima kiyi mishi gayu. Bawai nace ba'ayin kyauta ko karki bayar a , a abunda dai ina nufi a ɗan riƙayinshi haka dai da lissafi.

   Domin shidai Dikko a saudiya yaga riga jikin wata "yar budurwar balarabiya. Shine ya hasko idan tashi matar ta shiga a irin rigar itama zata bada irin abinda waccan ta bayar , ina fatan dai kun ɗan fahimceni. Shine ya shiga shima ya samota kalarta da komai da komai dan ayi mishi ado a gidanshi shima. A ita ga matar mai kuɗin banza idan na bayar gobe ya siyo wani. Ita ya siyo domin ke..., bashi da tabbas idan ya koma siye ya samo irinta , ta yuwu a canja kala ko kuma a samu banbancin company. Shin ba'a shiga haƙƙi ba....? Saboda haka idan dai namiji ya siyo abu ya kawo miki lallai yana da dalilinshi......

      Ai na baka ya rabaka da abunka. Ni kike faɗama wannan maganar dan kin ɗaukeni abokin wasar ki ? Yayi maganar cikin fushi yana tashi zaune. Ni zan siyo miki abu ki bayar dashi ? Nayi miki magana zaki faɗamin na baki ya rabani da abuna....? Yayi maganar yana saukowa daga saman gado , miƙewa nayi da sauri. Cikin firgitacciyar murya yace idan kika fita sai nai miki shigar bulet.........

















  08/02/2020

JAMILA MUSA…
[2/14, 12:12] ~M K: ⚜ BRILLIANT WRITERS ASSO ????
-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-

           *KWARATA RETURN...*
  _{{Kalu bale gareku matan aure}}_

Rubutawa…
JAMILA MUSA…

   *SAI NA AURI D ' K*

???? —— 10

   Shafin nan daga farkon shi har can² karshenshi. Sadaukarwa ne gareku "ya "ya masu albarka. 

ABDULRAHMAN B ‘ K LAWAL
&
JA’AFAR B ‘ K LAWAL

Ina roƙar Allah subahanahu wata’ala da ya albarkaci rayuwarku. Ya jiɓanci lamurranku ya jiƙanku ya ɗaukaku darajarku yasa ku gama da duniya lafiya. Ina roƙon ubangiji da yasa kuyi kyakkyawan ƙarshe. Allah ya dafa muku ya kareku da kariyarSa , ya tsareku da tsaronSa a duk inda kuka shiga yasa albarka a rayuwarku ya ƙulle idanuwa da zuciyoyin duk wani gurɓatacce daga gareku. Allah yasa ku dace a gidan duniya da ƙiyama. Allah yai muku albarka don darajar fiyayyen halitta Sallallahu Alaihi Wa’alihi Wasallam. Ameen ya Allah. Duk mai san manzan Allah S. A. W yace amin….. Duk wanda yace amin , ya Allah kasa ya gama da iyayenshi lafiya. Idan kuma sun rigamu gidan gaskiya Allah ka jiƙansu ka sadasu da rahmar ka , kasa can ya fiye musu nan har Babana…. Allah kasa sun huta. Mu kuma ka kyautata namu ƙarshen idan ajalinmu yazo Amin.

      Idanuwa na cike da hawaye nace ai dama ba fita zanyi ba haƙuri zan baka. Na ƙarasa maganar ina ƙoƙarin durƙusawa ƙasa. Tausasa murya nayi cike da ladabi na furta kayi haƙuri insha Allah bazan sake ba. Komawa yayi ya zauna danshi yana da karyayyar zuciya , ko yana furta sai na kasheki.......... Saina kashe² idan dai zanyi kuka ko yaga na ɓata rai zaice An mata bakijin magana kaza². Da lallausar murya ya furta gaskiya banji daɗi ba. Kuma karki sakemin irin haka daga yau...? Nace tom. Duk abinda ni nawa ne ? Idan dai har nine na siyoshi da hannuna koma miye ko mene ne ko wane iri ne karki kurkusa ki yanke hukunci ba izinina na faɗa miki. Na sake cewa tom. Ni kwanaki da zan aske ya nuna gemunshi ba kuka kikayi ba ? Shiru nayi ina kallon ƙasa kamar mijin da matanshi suka ritsa a ɗakin "yar aiki.

   Ke me yasa kikayi kuka ? Cewa kikayi in rufa miki asiri ko ni ina so idan kika ga masu gemu kiyi ta kallonsu ne ? Cikin ɗaga murya yace tou da irin wannan dalilin da zaisa ki kalli wani mai gemun a waje , tou nima irin wannan dalilin ne yasa na siyo rigar nan. Ko an faɗa miki niba mutum bane ba ? Ance miki ni nawa idon bai iya kallon mata ba ? Ko an faɗa miki ni banajin irin yadda kike ji ? Ko an faɗa miki niɗin dutse ne ni da banajin yanayi a jikina iye ? Ya faɗa yana nuna kanshi da ɗan yatsa. Tou irin abinda kikeji idan kika kalleni da yanayin da kikaji idan kika shafa fuskata ko kika zo kika rumgumeni , duk irin yanayin da kikeji idan kina shashshafa ko ina a jikina ni nafiki na wuce na zarce ki jin irin wannan yanayin. Ko sai ke kaɗai kike so a burge ki ? Wannan ai rashin adalci ne, zalinci ne. Ji nakeyi kamar ince miki ban yafe ba. Fashewa nayi da kuka nace Allah ya isa zakayi min ne ? Cikin ɗaga murya yace dan in nuna miki girma da ciwon da naji wallahi akan bayar da rigar nan da kikayi ? Yau da kin sameni akan tsini duk wanda ya tsaya miki da sai nasa kin anso rigunan nan.... Cikin shashshekar kuka nace dan ci baya ? Kece kika ci baya mai shiga haƙƙi miji. Har wasu banzaye sunfi mijinki mutunci , "yan gidan namu ne banzaye ? Suɗin , duk wacce kika gani a cikinsu idan ta dafe kan mijinta shiru zakiji. Irinki ne masu duhun tunani mutane ke rabawa da miji. Kila ma kin basu labarin ni na siyo sai su ɗauka , ke baki iya sakawa su bara su riƙa sakowa suna burgeshi , kina can kwance kina yarinta za'a buga wasan a barki da hauka. Idan ma kika ɓatamin rai na hasala da yawa duk shegiyar dana sake gani a gidan nan saina bata kashin bala'e. Me yasa nake baki kuɗi ? Dan kiyi rayuwarki karki shigamin rayuwa kije kiyi huɗɗarki da mutanenki ko na hanaki ? Ko nace karkiyi ? Ban takura miki ba ban shiga rayuwarki ba An mata , na barki kiyi sabgar gabanki dan kema ki zama mai "yan ci kamar yadda ko wane ɗa yake da "yanci , amma kin ɗaukeni kamar wani lusari ko an faɗa miki tsoro yasa na barki kike abunda kika ga dama ne ? Bana san na matsa miki ne ke kanki idan na takura miki rayuwar gidan nan bata miki daɗi. Nawa ne ba naki ba.

Ko kayanki ne ba nawa ba iye ? Ke kika siyo su ne ? Nine na gani ya burge na siyo domin ki , ki saka nima inji shauƙi inje irin yanayin da kike shiga idan kika kwanta jikina , ke wai bakya gane komai ? Komai sai an fito ɓaro² an fallasa miki saboda kina da jakin kwalwa. Da kinga na fara sauke²n kaya baki da zama lafiya. Kar in bada miki wannan , kina so kiga na saka wannan , ke wannan yana miki kyau. Ko nace bana sanshi sakani gaba kike kitaimin kuka ke mai idon fitar da hawaye. Shin yanzu ke ba da kanki kike fidda kayan dake baki ra'ayinsu nawa ki bada su ? Duk yadda nake san abu idan kika ce baki sanshi dole haƙuri nakeyi dashi. Duk yadda bana san abu idan kika cemin kina so haƙuri nakeyi. Sanyaya murya yayi yace duk dai dan in burgeki. Amma da yake baki da adalci babu abinda ya dameki inyi farin ciki ko kishirya haka. Ki burgeni ko karki burge kedai kanki kika sani burinki in miki kiji daɗi. Wannan shine rayuwar farin ciki.....? Ya ƙarasa faɗa yana kaiwa katifa duka , baki da adalci sam² kullum baki da burin burgeni saidai neman hanyar musgunamin. Tou daga yau tunda iskanci ne abun naki na rantse da girman Allah kika sake ɓatamin rai saina lalata miki fata.... Tom. Zazzaro ido yayi yace karki cemin tom akan komai kice bazaki ƙara ba.......... Ya faɗa yana rufe idanuwanshi. Da sauri nace bazan ƙara ba insha Allah. Hanya ya nunamin in fitar mishi daga ɗaki. Da sauri na fice na barshi yana ta mita.....

 Tsaye take a kitchen tasha ado kamar zataje gasar wanka sai fitar da wani irin sirrintaccen ƙamshi takeyi. A gabanta kuwa kiret in kwai ne take ta dandaƙa ba sassauci. A gefenta kuma "yar matsadiyar wayarta iphone ce keta rero waƙoƙin turanci ita kuma tana rakiyarsu da bakinta. Wata irin zundumemiyar ashariya Yazeed ya ciko bakinshi da ita ya zundumawa Jiddah dake ta farfasa kwayaye....... Wandon jikinshi kuwa sai riƙonshi yake a hannu yana ƙoƙarin ɗaure belt dan wandon ya tsaya. Kuturmar dumadu.....? Kwan zaki cinye dan uwarki...... ? Waye yace miki anacin ganyen filawar da aka jera dan ƙawata ƙawar gida ? Cike da masifa Jiddah tace kai kaima dan uwarka ! Ko an faɗa maka shiru² tsoro ne wai iye ? Idan baka so inci kwai kawai ka bani sakina inyi gaba ai muma a gidan namu anacin kwan. Cike da ɓacin rai Yazeed yace kin taɓa ganin majiyyaci a maƙabarta ? Ai asibiti shine majiyyaci yake zuwa dan ganin likita , shine zai dubashi ya gano ciwonshi ya bashi magani sai ya samu waraka da izinin Allah. Maƙabarta kuwa gidane na matacci , wannan gida da kika ganshi nahir jinyace daga gareni idan kuwa har kika fita a gidan nan gawarki ce aka fidda. Ni bana aure dan saki saidai inci uwar fatar mace tai iskanci. Aurena yana nan ram² baya girgiza no saki an no barkono yaja yaji da bakinshi. Ni nan da kika ganni matakin iskanci na taka bansan iyakar nahiyoyin rashin kunyar dana ƙyetara ba. Ɗan iska ne ni na nunawa a satilayit banda mutunci ga muni banda kyau ko nai wanka..... Da ke a tunaninki na aureki domin kisan wuta ? Nine ma zaki kashe wuta dani ? Tou yanzu na kunnu nayi ta ci gaba da ci daga nan har a tsaida ƙiyama. Bana sanyi bana siƙewa bare kuma kiyi tunanin zan mutu.

     Ai wannan auren ko auren da aka daura a coci bai kaishi ƙarko da aminci ba. Yaci uwar auren coci ya zarta na kotu kuma. Yadda bakya tunani auren ya wuce inda kwalwarki bata iya hasasowa saboda ya linka auren zobe dan auren Yazeedu auren kabari ne. Kuma haka gidana yake idan an shigo ba'a tafiya saidai idan za'a tafi kabari , nunawa yayi da hannunsa yana ci gaba da cewa wannan nasan zahiri ne tafiya ɗaya ba dawowa. A bakin tarihin rayuwarki waye kikaji ya shiga cikin ramin kabari ya fito ? Tou ba'a fita sai ranar da ƙiyama ta tsaya , wato ranar yauma tubalasra'il. Ranar girbe abinda ka shuka , ranar da uwa bata gane ɗanta miji idan yaga matarshi zaisha kwana. Tou gidan nan maƙabartarki ne a nan kabarinki yake idan kinga kin fita a gidan nan mutuwa kikayi dan ƙaniyar iskanci. Ya ƙarasa maganar yana shaƙe wuyan Jiddah tare da cewa biyamin kwai na....

  Yana shaƙe da ita yaci gaba da cewa shin bana faɗa miki abincin gidana adon idon duniya ne ba ? Dakel tace e , Yazeed yace amma kika ce kinji kin yadda ko ba haka nayi dake ba ? Cikin jin zafi shaƙa tace haka ne. Riƙe wuyanta yayi da hannu ɗaya yace duk kwai ɗaya dubu ɗaya na siyo abuna. Kuɗin mota da kuɗin kunna gas a gidana ba ranar sanwa ba. Bakina dana ɓata wurin ciniki , kin yanka albasa ba'a kan ƙa'idar ma'ikata ba. Zagin miji wanda babu shi a kundun tarihin musulci zunubi ne mai girma , domin wanke kai daga wutar Allah neman gafara da biyan kuɗin diyya dubu ɗari. Cin zarafin miji kin daƙile min guyuwa akan ƙalubantar ciyarwa kince gidanku akwai abinci. Domin samun sassauci kwanciyar kabari cikin salama zaki biya dubu hamsin domin wanke kai daga bugun mala'eku. Naira budu tamanin na neman yafiya ne domin kiyi kwanciyar kabari cikin salama. Da hannun da bai riƙe wuyanta ba ya fara lissafun kuɗin a wayarshi.

  Yana lissafa kuɗin yake cewa yau kuma anyi buking ina a wasan danbe ki biya kuɗinki da wuri ki yanki tikiti tun kafin ƙarfina ya ƙare. Ki bada budu goma tunda ke ta gida ce , zan siyar miki dashi ne akan farashi mai sauƙi amma ba haka ake siyarwa ba dan kada jibi ince miki dubu talatin ki fara wallahi² , cikin wahalalliyar murya tace bana so. Basai kinyi muradi ba kuɗin gado da katifa na yafe miki tunda ke matar gida ce. Kuɗin kwai naira dubu talatin. Cikin kakari Jiddah tace ai ba duka naci ba , damuwarki ne wannan inji Yazeed yaci gaba da cewa + naira dubu biyar ta-ra akan kin tari numfashin miji yana magana kina sako mishi baki..... Duka abinda kuɗinki suka kama dubu ɗari biyu da tis'in da biyar , amma ɗari 3 zaki bayar hada ladar lissafi dubu biyar , ya ƙarasa maganar yana sakin wuyarta ya turata can baya. Riƙe wurin daya shaƙa tayi tana ta tari , ƙuhul² kamar sakin mayu.

   Wai wannan wane irin zalinci ne ? A fusace ya nufi wurinta ya ɗaga hannu yace zan....... Da sauri ta duƙe. Wayarta ya ɗauka ya miƙa mata tare da cewa maza inji alart. Jiddah na kuka tayi ma Yazeed transfer. Dariya yayi bayan yaga tabbacin kwanciyarsu a asusun bankinshi ya rumgumeta yana sumbatar ta. Ina sanki haɗaɗiyar matata abun alfahirina bugun zuciyata , gaskiya yafa kamata azo a ƙulla hanyar neman wasu kuɗin kafin asusunki yayi shiru , ya faɗa yana fita daga kicin in sweetheart kisha shagalinki lafiya , lambar lokacin ki shine. 0 3 4 9 am. Wato yana nufin lokacinta da zai bata na katin danbe da ta siya shine 03:49am ya yada mata katin yayi gabanshi....... Kuka Jiddaah tai tayi tana Allah ya isa. Saida tasha kukanta har ta gode Allah ta kira Nabeela ta rattafa mata komai tayi ƙari akan abinda yayi mata ta kulle da cewa kuma yace baya sakinta. Abunka da ɗan uwa Nabeela taita kuka ta kira Rabiya ta faɗa mata. Rabiya ma taita tsinewa Yazeed wai zata faɗawa Dikko wallahi sai an kaso auren nan , yasan ashe Yazeed tsinannen Allah ne yasa aka haɗa auren saboda cuta irin nashi kaza² , taya Yazeed zai kulle yarinya a gida ba abinci yana bata gwale² sai duka ? A yinin ranar haka sukai ta yaɗa magana tsakanin su "yan ɗakinsu.

  Daga baya suka bawa Jiddah haƙuri tare da tura mata kuɗi ta siya abinci kafin a samu mafita saifa Yazeed ya sakota ɗan iska mara mutunci anyi masa rana zai yiwa mutane dare. Rabiya da kanta tazo har gida taba Dikko labari , mugu yaji mugunta yasha dariya harta zarce musali. Saida yasha dariyarshi sannan ya turawa Sultana saƙo tazo palonshi , bayan naje yace Rabiya ta maido labari baya. Ran Rabiya kuwa ya hayaƙa taita zagin Dikko , waishi wane irin ɗan iska ne ? Ta faɗa mishi ciwo yana ta wata dariyar iskanci ? Cikin dariya yace bakinki ko nawa ? Fuuu Rabiya tai zuciya ta ɗauki jakarta , Dikko yace Hajjaju tsaya da Allah , naƙi in tsaya tunda kai ɗan iska ne. Allah ya baki haƙuri karki tafi. Tsoki tayi ta tsaya a bakin ƙofa , daga ni harshi duk fita mukayi , jingina yayi da ƙarfen bene ya ɗora hannuwanshi ta baya ya rakuɓe kamar mijin ɗiyar soja da yayi dukawa ita a barek kuma itace da gaskiya , haɗe rai yayi yana kallon Rabiya nima kusa dashi naje na tsaya ina kallonshi. Gyara bakinshi yayi shima ya kalleni. Murmushi nayi shi kuma ya sake gaggaɓewa da dariya.....

Rungumeshi nayi nima ina dariya , safko hannunwan shi yayi ya riƙeni. Wai anci ƙaniyar iskanci mata na buking in mijinta , ita da haƙƙinta a nuna mata fin ƙarfi , kam balasti nan taff ya jinjina kanshi da mamaki cewa "yan iska duniya basa ƙarewa ko kunyar faɗa ma baiji ba tirrr. Dariya itama Rabiya tayi amma badan ranta yaso ba , haka dai da damuwa , ciki muka koma duk a palo muka zauna. Dikko yasa aka sake karanto labarin ni da bana nan naji da kaina. 

  Shi kam Yazeed ma baida mutunci ko tsoron Allah bayayi ? Taya matarshi zata siyeshi dan yayi kwanciyar aure da ita ? Duk a raina nayi magana , tun daga wannan bansan inda zance su yaci gaba da tafiya ba , hankalina da tunanina kuma ya koma karatun rayuwa ta , ta baya. A gajiye na kwanta jikin Dikko ina ƙara hasko rayuwa da yadda ita kanta rayuwar tayi min hajijiya.

  Maganganun Dikko da kuma dalilinshi na sawa a karanto min rayuwar gidan Jiddah. Shima wannan duk hikima ce , yana so inyi gyara ne a inda nake da matsalolin zamantakewar aure. Sai zan tukan Inna , taƙaitacciyar jiyar zuciya na sauke dakel a hankali na furta Allah ya jiƙanku iyayena yasa kun dace da kyakkyawar makoma. Saukeni Dikko yayi daga saman jikinshi zaije ma Rabiya rakiya. Nidai ban bisu ba nace ta gaida gida ina daga kwance..... Duk inda kake ka godewa Allah kuma ka nuna haƙuri da jajircewa. Bazafa a gane matsalar ba sai tafiya tai nisa. Allah ka rufamin asiri ka ƙarawa mijina haƙuri da halina , Allah kasa in daina mishi abinda baya so.

  Tun daga wannan rana kamar anmin allurar natsuwa haka na zama wata baiwar Allah , har abun ya dami Dikko danshi a tunaninshi ko banji daɗin maganarshi akan "yan gidanmu shiyasa nake fushi ? Me yake damuna ne ? Ko banda lafiya ? Idan yayi min wani abu banji daɗi ba inyi haƙuri kuma in faɗa masa miye bazai sake ba. Nace masa babu komai amma hankalinshi ya gagara kwanciya. 

     Ko yau a makaranta burus² nake kamar garin kwaki bai jiƙu ba. Shima daya kawoni makaranta dai ranshi bai mishi daɗi ba , wai shi baya san wannan fushin da nakeyi , dan Allah in saki raina mana , ya zanta haɗe mishi rai shi bayajin daɗin gani na a irin wannan yanayin , ko na gaji da ganinshi yaje hutu idan naso ganinshi saiya dawo ? Nace ba komai , tou kiyi murmushi mana An matana...... Yayi maganar yanayin murmushi mai tafe da yaudararren kallonshi. Kaɗan na yaƙe bakina tare da kwantar da kaina gefe kaɗan nayi mishi ɓarawon kallo kamar liman yaga wawan zama , so kike dai in koma gida da baƙin ciki ko ? A , a , tou wai meke damunki ne ? Ba komai , cike da ƙunar zuciya yace An mata wai yaushe kika zama munafuka ne ? In banda munafurci ni zaki riƙa munafurta ? Me nayi miki ne iye ? A kwana biyun nan kina ta ƙoƙarin riguzamin farin cikina laifin me na aikata ? Gaskiya ce na faɗa bayan nan miye aibu na iye...? Babu , hmmm yayi tare da gyara zamanshi yace jeki....... Fuuuuu na fita ban rufe motar ba. Bin bayanta yayi da kallo. Banyi tafiya mai tazara ba na dawo raina a duƙunƙune nayi ma motar shigar bulet nima. Da sauri yaɗan ja kanshi baya. Kusa dashi na tsallaka na dafa hannuna a jikin gilas in murfin motar da yake zaune ɗayan hannuna kuma a saman kujerar da yake , na sakashi tsakiyata kenan , wasa nayi da girarena sannan na kakkaɓa mishi ido da logo mai ibar yanayi muuuuuu muah nayi masa a bakinshi. Wahalallen murmushi yayi tare da fitar da sautin numfashi a gajiye yana ƙoƙarin riƙoni na sauka a wurin na zauna saman kujerar mai zaman banza sannan na fice daga motar..... Murmushi yayi tare da rufe murfin motar yaja yai tafiyarshi.

     Cass² coss..... Gaba ɗaya class in idon kowa ya koma kan Mai gilashi. Tana tafe tana wata irin girza mai tada hankali ta huro kwan cingom ta ciki ta hankaɗe kanta sama ga ƙaton gilashinta ya cinye rabin fuskarta. Duk lokacin data ajiye ƙafarta domin taka tazara wurin tafiya sai kaji kacau , tana ɗagawa zakaji ta sake wani irin kuka cauu coss , buɗe hannayenta tayi kamar zata rumgume wani take cewa. Aini kwarƙwassa ce tashi mai gida da gidanshi. Turnuƙuƙiy faɗan ibilas yaron idan baka sha duka ba kasha ƙura. Zama tayi a saman decks ta fara kirara kanta tana coka ma wani malami zagi. Malamin dake cikin ajinmu yace mata ta fita.....? Sch bag inta ta ɗauka ta fara tako. Wai su sune jihar katsina , kuma taurari a cikin duk wata jaha dake nigeria , tana alfahiri da karuwancinta domin shi ya kaitagacin nasara , tana alfahiri da tarihinta tana bugun ƙirjinta da zuwa nahihohin afirika da tayi ta silar kasuwancinta , duk wanda ya nemi ya ƙalubalantar mata sana'a zata sa a ɓatar dashi a gari. Malamin yace ta fita karta mishi ranshin kunya.....

  Saida ta fita gaban aji ta kallo "yan kilas tace. Duk ɗalibi ko ɗalibar dake ajin nan wai tasan asalin kowa da tarinhin rayuwarshi har principal , shima malam dake tsaye tasan ko ƙafa nawa ne da ɗigo nawa na gidanshi {{ ƙarshen sani kenan }}. Kuma duk marecen ranar lahadin ko wane sati yana bi ta wurin gidan "yanci yana wucewa. Malam ci gaba yayi da rubuta babu a saman allo. Tsoki Mai gilashi tayi cewa idan yace ƙarya ne sai in faɗa mishi cikin motar da yake zuwa.... {{ furuci ne na "yan tasha , tana nufin karuwanshi , shi ya gane yaren amma "yan aji basu fahimci yaren ba sai mu damu ka ɗan karanta karatun bariki }} yo ai mu munsan komai wallahi shiru kawai muke muna ƙyalewa , wallahi babu wanda ya isa yasa naci gurasa inta wani wahalar da kaina wurin neman kayan haɗi ni ba mayunwaciya ba , ra'ayi ne abun ba muradi ba , bana ra'ayinta ne kwata² bare inci ta wahala tayi ta gurjemin makoshi , masu ra'ayi sai su siya suci ko ba ƙuli nasu ra'ayin ne ansa a haka tunda duniyar tana da faɗi biyan buƙata ga masu buƙata. Ba dalili na tattauna goro ni banci sigari ba , "yan aji...... ? Iye , shin ana dole ? A , a , gaba ɗaya suka ansa matsuwa da rashin wadatuwar muhalli kesa masu bada gidajen haye faɗa girman gidajensu dan suyi kasuwa. Amma a tunani na ra'ayi ne rayuwa ɗaki ɗaya da wani , babu abinda zaija min haɗiyar kwaɗo ina kallon kifi. Kuma bari mutum ya sake kai ƙarata yaga yadda zansa shi biya karatun bebe dan a tafiyar ai ba dole , kuɗi mutum yake bayarwa a bashi ɗaki a hotel idan har aka samu matsalar ruwan bayi ko rashin wadatuwar hasken wutar lantarki ƙorafi yake a canja mishi wani. Da lafiyata bani rayuwar tsohon gida bare rufin daya sha "yan dabaru ya faɗo ya kasheni. Kallon rainin wayau tayi mishi tare da cewa wutar lantarkinka bata da haske idan an hana kuwwa ai ba'a hana tsalle ba. Ka , taga ni anan nasan inda zan tarfaka.Tana faɗin haka tabar ajin. Shi kuma malam ya fara zage² yana fidda mutane waje.

  Nima gaggaɓewa nayi da dariya , na farko dai su matan aure ba'a dukansu kuma ba'a zaginsu , ƙa'idar makarantar ne saida a haɗasu da mazajensu suja musu kunne idan kuma aka wonasu da yawa za'a koresu daga makarantar. Ci gaba nayi da dariya sosai ina kallon Malam domin dai maganganu ne masu zafi ta faɗa mishi a hikimance irin tasu ta "yan tasha. Kenan shi malam yakai tayin kasuwarshi ne wa Mai gilashi taƙi yadda , kamar yadda take nufi bai da gudun tafiyar dokin da take so , shine taƙi ansar tayinshi shi kuma yakaita ƙara yana goga mata laifin ƙarya..... Kallona yayi tare da cewa nima in fita in bar mishi aji. Ta window Mai gilashi ta leƙo tare da cewa fito in baki labarin yadda yake tafiyar da nashi dillanci. Cewa yayi in zauna. Ƙin zama nayi na fice waje nima , ina tahowa yace zan faɗawa mijinki kin fara abokai marasa tarbiya. Daga waje Mai gilashi tace shima Malamin baida ita.....

   Har na fita waje ina dariya , dariya Mai gilashi tayi tare da cewa ɗan iska tsoho ɗan nakusa exp kai..... ? Ɗan an rubutamin best before ritayar..... Ta ƙunduma wata irin ashariya ta "yan tasha masu lasi. Leƙowa yayi yace mu tashi daga nan. Kallona yayi yace wallahi saiya faɗawa mijina iskancin da nakeyi. Mai gilashi tace kafi zuciya sauri kuma duk saina tona muku asiri , ni zan turo nawa shugaban har makarantar sai yasa an rufe munafikan banza kuci tuwon gidanku kuci na kasuwa , na makarantar ma dan haɗama duk sai kun cinye ku uwayen zalama. Ƙara kakkaɓewa nayi da dariya , nan ma magana ce mai jimla ta faɗamishi. Baiyi magana ba ya koma ciki ita kuma ta fara magana...

   Izzar karuwanci ake gaya miki Sultana. Karuwanci na ni bana matsuwa bane ba. Na ƙara isa ne da neman suna sai inji nakai wata shegiya. Ga ciyamomi , sanatoci ministoci ham shaƙan "yan kasuwa kiga an nuno kamilin mutum a talabijin yana ta wani bubbuɗe ido dana ganshi nasan na shanye rubutun nayi gaba. Nayi mu'amula da mutanen dani bana iya lissafosu adadin yawansu amma ina da jerin sunayen duk namiji daya haɗa ƙirji dani , sassauta murya tayi cewa idan aka fiddo dubun maza a garin nan ai inaji ɗaiɗaiku ne banja zariar wandonsu ba...... Tsoki tayi cikin takaici tace amma har yanzu gwamnatin jaha bata san da zamana ba. Fashewa Mai gilashi tayi da kuka tana cewa Allah yasa kar in mutum ban shiga cikin talabijin ba , a nuno ni a matsayin tantiriyar karuwar data buwayi kowa a gari. Nidai kawai a jinjina min shine burina , idan ba da list ina zan tafi ba saina faɗo sunan kowa ta yadda lungu da saƙo idan na wuce ansan nima nakai jajirtacciyar karuwa.

 Kidai ci bugun banza , dan duk wanda kika faɗo sunan Babanshi da sunan kin zare inajin kafin ki fito daga gidan talabijin ɗin katsina gaba ɗayanta ta haɗu. Yadda ake sara na nuna cewa saidai kiji ance attakabir wallahi gunduwa² zasuyi miki gawarki ma kanta baratayi kyan gani ba. Jakarta ta buɗe ta ɗauko leda mai layi² tana cewa sai ince duk subi layi....... Idan zasu sassarekin ? Ke ana maganar arziƙi kina san kawo min mutuwa wallahi , mtsww anshi nan ni kinji.

Ansa nayi na buɗe , wasu irin duwatsu ne masu masifar kyau kalar burgewa. Meye wannan ? Jigida ce banza. Jigida haka kuma ? Ey mana , irin ta saman ƙuguna ce , sirrin jaka sai kin ɗaura a ƙugunki. Ke ina kika samota ne ? Karki ɗaukeni wawiyar layi kinji. Buɗo idanuwa tayi sosai tace wanna jigidar babbar sirri ce , idan na fara lissafo miki "yan wasan data ciyomin zakisha mamaki gwargwadon yadda kikayi ɗimuwa. Ba katako bane banza duwatsu ne na sirrin rayuwa. Kinga wannan jigidar idan basai ta hana mijinki fitar dare ba kice bamai madubi nake ba. Da ɗan yanayin tsoro nace jigidar magani ce ? Kusa dani ta matso sosai tare da cewa magano.... Maganin ƙaniya... ? Ba'a wanka da ita na farko kenan , sannan na biyunsu ba'a kwanciya da namiji da ita. Maɓalli gareta kawai ɓallewa zaki idan zaki shigar jami'ar gadon aure. Amma mu masuyi dan kasuwa muna kwanciya da ita ne dan ƙararta itace ke buga kwalwar maza a taƙaice. Idan dai kin kwanta da ita tou lallai karkiyi wanka da ita domin kina bata ruwan wanka ta tashi aiki.....

  Kuma da kikeji tanayin ƙara bawai itace da kanta takeyin motsin ba , kece zaki cire ƙyashi ganda hasda da baƙin cikin rayuwa kiyi tafiya da isarki. Tashi tayi tai tafiya lafiya lau , tace kinji kukan tane ? Nace a , a , tace an kallo ni ne ? A , a , wani yasan na wuce ? A , a , tou tsaya kiji sharrinta. Wata irin girgiza tayi tare da fara bada matakala. Wani irin kuka jigidar ta farayi coss׳. Sake tafiya tayi tace cakas² cas² , ta saman inda muke ta diro ƙasa cosssssssssssssss.. Cissssssss duk malaman dake kusa da inda muke a cikin aji saida suka leƙo. Dariya tayi tare da cewa ai da gayyarmu muke komai idan mutum yayi kuka muna da tsumman goge hawaye..... Aikinta ga maza ne bayan shekaru biyu take tashi daga aiki. Kyauta na baki wannan idan tayi miki kinji kina muradi saiki riƙa bada kuɗinki a siyo miki.

  Zata fara bani labarin abinda ya haɗata da malamin dake cikin aji , da Alhajin da suke gidanshi aka aiko ana kiranta. Tashi tayi ta tafi ni kuma nabi jigidar nan da kallo. Tunani na farko daya zomin shine wasiyyar Inna , da tace kar inyi wani abunda mijina banyi shawara dashi ba. Shin da yaddar Dikko zan ɗaura ko kuwa da yaddar zuciyata....?

  Har aka tashi makaranta ina tunani. Yau ba Dikko yazo ɗaukata ba Ashiru ne. Kuma dana koma gidan faɗa. Har an faɗa mishi abinda nayi a makaranta. Shi mutuwa zaiyi , ina zai saka kanshi , kinsamin ciwon zuciya sai na tafi na bar miki gidan nan , badai zaki barni in zauna lafiya ba ko ? Idan nayi miki faɗa kiyi zuciya dani kaza². Duk haƙurin dana bashi rufe idonshi yayi bai saurareni ba. Yaci gaba da masifa shi saiya haɗa kayanshi yanzu²n. Bazaki sake gani na ba sai kiyi duk iskancin da kika dama ? Kuma idan ya kama yarinyar nan sai ya kasheta............. Tou shikenan kaje ka kasheta , kuma wallahi sai nayi kuka , wayyo............ Allahna na kurma wani irin ihu na nufi ɗaki da gudu. Jin ya daɗe bai shigo ba nasan yayi zuciya. Fitowa nayi har yanzu yana nan zaune a inda yake. Daga sama ban sauko ba nace ai sai ka tambayeni me nayi kuma shi malamin me yayi min ? Kawai anzo an karanta maka ƙarya da gaskiya ka hau ka zauna. Gani ina da hawan jinin masu juna biyu. A asibiti ance na rage yawan damuwa da ƙuntatuwa. Kullum saika ɓatamin rai ga ciki kuma , shin dakai da cikin duk sai kunsa na mutu. Idan kin mutum ko baccin rana nayi in huta da halinki. Ƙaramin yaro yafiki daɗin zama. Mtsww. Shigowar Abbakar palon yasa nayi shiru. Shima bawan Allah a bindige yake da ganin idonshi yaji bala'en mace. Dikko bai kalleshi ba nima kuma ban koma ba ina daga sama duk ina kallonsu.

   Magana yayi ƙasa² , banji abinda yace ba saidai shi Dikkon yayi murmushi mai ciwo. Ƙara kasa kunnuwa nayi amma duk iyakar masifa ta banji abinda suke faɗa ba , saida suka gama ƙus²ɗinsu Abbakar ya fita. Yana fita Dikko ya fara faɗa. Wai ashe Abbakar shima ɗanyen kai ne mahaukacin banza baima san matarshi tafi wannan wayau ba ? Wai me yace ne ? Tsoki yayi sannan yace wai matarshi zai kawo kiyima nasiha. Nace mishi tou wallahi ya rufa ma kanshi asiri karma ya kuskura matarshi tasan hanyar gidan nan idan kuwa ba haka ba tou fa lallai zamanshi da ita ya ƙare. Fashewa nayi da kuka cewa wannan baƙar shedar kayi min kuma.......? Ƙarya nayi ? Yanzu ba tsayawa kikayi daga nan kinamin rashin kunya ba ? Na tambayeshi shin tana baka abinci ? Yace min ey , tana maka sannu da zuwa yace ey , tana wanka tana wanke ido tana gayu ? Ey. Rashin kunya take maka ne ? A , a , nace tou idan dai ba tauye haƙƙinka takeyi ba ka koma kaita haƙuri nima haƙuri nakeyi , nace mishi gaki nan rashin duka yasa kwana biyu kin warware. 

   Shiru nayi na juya mishi baya ina magana ƙasa². Tsoki ya sakeyi tare da cewa Allah dai yaso ban faɗa mishi haka ba , cewa nayi dai yayi haƙuri bance kema fama nake dake ba. Kawai dai haƙuri na bashi cewa mata ai lallaɓasu akeyi , ni abinda ya ban takaici wai ke kallon mai hankali yake miki , har yana tutiya zai kawo matarshi tayi koyi da halinki , baisan nima ƙurmusa min takaici kike ba , yadai kamata kisan abinda kike gashi nan har za'a fara baki gabata. Kace ya kawota in mata nasihar. Ki fara ma kanki sannan kiyi ma wani , yana faɗin haka ya fice daga palon.......

     Mai gilashi daga inda aka kirata tana gama abinda take gidansu Sharifa ta wuce. Anan palon gyatimar Sharifa aka zazzage kolin rashin wayau. Daga uwar har ɗiyar dan ɗimuwar tunani Mai gilashi duk ta maidasu wasu lusarai.... Mama wallahi matarshi ce duk take ta shige da fice. Yadda yake san Sharifa kika ga gaba ɗaya ya ɗauke wuta tabbas wata irin gagarumar jifa ce , sai kunyi da gaske kun ƙara miƙewa dan wannan tarayyar da babu "yan al'adu ai nasan da tafiyar bata yuwu ba. Tayi maganar dan bugun cikinsu. Ai nan uwar Sharifa ta saki baki taita hawa gefen layi , ina shi Malamin naku ne Mama ? Sharifa dake full charge tace yai tahiya tayi maganar cikin muryar mashaya tana layi. Cikin faɗa na duniyanci Mai gilashi tace gaskiya Mama kuma da laifinku. Laifin meye nawa ni a ciki ? Saboda Allah Mama kuɗan ƙiyasta dihun kai da wayayyar rayuwa , maza fa yanzu idonsu kallon rana yakeyi , akwai wanda baya san mace ? Taya Sharifa zata riƙa zuwa zance da hijabi dan Allah ? Su wa'annan "yan duniyar ai bakya nuna musu hijabi ba domin wayayyar rayuwa zaki fahimtar dasu kin iya , cake take dan haka maganarta bata fita.

Mai gilashi tace da Allah rufewa mutane baki muyi magana da magabata. Shiru Sharifa tayi Mai gilashi taci gaba da cewa Mama ni ina da Malami acan Zandar aiki yake kamar yankan wuƙa , saidai shi aikinshi sai an ɗebo fitina zama ɗaya yake buga aiki fitina ta koma tayi bacci. Malamin shine kika ga ya ɗauremin ƙugu nake baza hajar iskancina kasuwa². Kuɗin mota dana aiki duk ni zan bayar idan buƙata ya biya saiki bani abu na. Mamar Sharifa tace wane irin malami ne sai an jawo fitina yake aiki ? Izzar aiki ake gaya miki Mama , su bala’en suke kwantarwa dan dai kawai su nuna muku jajircewar su a wurin iya aiki , kuyi shawara sannan ku taro bala’e ni zan tsotse muku duk dafin masifar bala’en. Miƙewa tayi ta jawo Sharifa suka fito waje. Wuri suka samu dan ɗan keɓancewa gefe tace ke jaka bakuzo kun daki matar Dikko ba , sautin maganar kaɗai ke fita amma bakajin maganarta. Mai gilashi tace idan kunga dama kuzo ku daketan , tana faɗi haka tayi gaba abunta.

Previous page 1 2 3 4Next page

Leave a Reply

Back to top button