Hausa Novels

Lu’u Lu’u 45

Zaune tayi kusan Ayam d’in tace “Ina zuwa.”

Ruwa ta kai hannu ta d’auka dake gefen gadon cikin jug na tangaran fari k’ar da shi ta zuba a hannunta sannan ta shafa mata a fuska, a hankali ta fara motsawa har ta bud’a idonta, ajiyar zuciya suka sauke inda Juman ta d’an bud’a idon Ayam d’in, jim tayi tana kallo sannan ta kawo hannunta ta kalli tafin hannunta.

Murmushi ta saki hakan yasa Ayam kallonta Umad ma haka, cike da jin kunya yace “Mah, me ya sameta ne? Ko farmaki ne aka kawo mata ?”

Mik’ewa Juman tayi tsaye ta zagaya bayanshi tana murmushi tace “Farmaki ne.”

Hankali tashe yace “To amma daga ina haka?”

Gimtse bakinta tayi ta matsa kusan Kossam da ita ma ta zabge sakamakon mutuwar na ta mijin, cikin kunne ta rad’a mata magana hakan yasa suka saki murmushi duk da halin alhinin da suke ciki, matsawa Kossam tayi kusanshi ta kama kunnenshi ta murd’e tace” Ja’irin yaro ashe abinda ka zo ka yi kenan? To farmakin daka kai mata waccen daren ne ya bayyana kan shi.”

Juman da Bilkees duk k’yalkyalewa sukayi da dariya, shi kuma sam bai fahimci inda suka dosa ba dan haka ya kallesu da mamaki yace”…

 

*Ku yi hak’uri da wannan, sannan kuyi hak’uri da ji na shiru kwana biyu, matar yayana ta haihu shiyasa.*

 

*Alhamdulillah.*

The post Lu’u Lu’u 45 first appeared on 2gNovels.com.ng.

[ad_2]

Previous page 1 2 3

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button