NOVELSUncategorized

MUTUM DA DUNIYARSA 7

  *_????HASKE WRITER’S ASSO…._*

   *_????MUTUM DA DUNIYARSA….!!????_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_
                 *_Bilyn Abdull ce????????_*

                   *_[7…..]_*



    
…………..Kamar yanda malam Mustafa ya fad’a bayan awa d’aya malamin da zaima su jiddah jarabawa ya shigo, sallama yay suka amsa masa tare da gaisheshi.
      Ajin yayi shiru kowa yana kallon malam Sulaiman, yad’an tura hularsa baya yana shafa gaban goshinsa da nazarinsu, saikuma yay murmushi ganin duk sunyi tsuru-tsuru sun zuba masa idanu. Zama yay inda aka tanada domin zaman malamai kafin ya kuma maida hankalinsa Kansu.
        “Inaga nama canja shawara kawai, zanyi jarabawar da baki”.
     Kallon kallo aka komayi tsakanin su Jiddah, kowanne a sanyaye ya amsa da, 
     “Na’am ya mu’allim”.
Fita malam Sulaiman yayi, babu jimawa ya dawo shida Malam Shu’aibu da malam mika’il. Nanma su Jiddah gaidasu sukayi. Malam Sulaiman yabasu izinin fita waje su duka, zuwa wajen wata bishiyar dake gaban aji. Ahaka zasu ringa zuwa d’aya bayan d’aya.
        Da yawansu sun rikice, dan kowa baisan miza’a tambayeshiba, ga malam Sulaiman gwanine wajen iya zak’ulo tambaya.
         Amirar ajin mai suna Shamsiyya jamilu yasaka ta rubuto sunayen kaf y’an ajin tazo saman baranda tana kiransu d’aya bayan d’aya. Hakan kuwa tafaru, bayan tagama rubuta sunan kowa aka Fara, gaba d’ayansu dama su 38 ne a ajin, dan haka aka fara komai a tsanake. Kowa ya fito saikaga yana mazurai, nanfa cikin Jid

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button