MUTUM DA DUNIYARSA 23 – 24

*_????MUTUM DA DUNIYARSA….!!????_*
_(ya dace ya gyara kansa)_
*_Bilyn Abdull ce????????_*
*_[23➖24]_*
…………..Abinda yabama Jiddah mamaki ashe Matar da suka had’u a jirgi
tafiyarsu d’aya, sai da suka shiga motar datazo d’aukarsu sannan Jiddah itama taga ta shiga.
Cikin Murmushi matar tace, “Kinyi mamaki ko? Na 6oye mikine dama danna baki mamaki”.
Fuskar juddah ma d’auke da murmushin take fad’in “Aiko aunty kinbani, nakuma gode”.
Y’ar dariya sukayi, wadda tasaka su Malam mustafa kallonsu. Jiddah datun d’azun dauriya take da zamansu kusa da ita tai k’asa da kanta, tana karanto sunayen ALLAH domin Neman sassauci da k’arfin zuciya.
“Kufa Mata inda kuke birgeni akwai saurin sabo”. ‘cewar malam mustafa idonsa akan matar’.
Matar tai murmushi cikin wani salo Mai nuna tsantsar so da k’auna tace, “Shiyyasa kuma zumincinmu keda k’arko”.
Jiddah dai dasu Uncle yahaya suna jinsu.
A haka suka k’arasa Makkah.
Sun isa wani k’ayataccen waje Wanda Jiddah ke k’autata zaton Hotel ne, dan yanada matuk’ar girma, Wanda ya d’akkosune yay musu rakkiya har ciki inda aka tanada musu masauki tunkan su Iso. Abun yak’ara birge Jiddah sosai.
Itada matarnan d’akinsu d’aya, Uncle yahaya da malam Mustafa ma d’akinsu d’aya.
Gaba d’aya Jiddah tama kasa cewa komai gameda had’uwar d’akin, sai kalle-kalle take. Matar tai murmushi tana kallonta “Dukda nima wannan ne zuwana Saudiyya na farko, na Lura kinfini k’auyanci k’anwata”.
Hannu Jiddah ya saka tana rufe fuskarta dan taji kunya, a haka tace “Aunty abunne akwai k’ayatarwa, gaskiya mahaifar Manzon ALLAH ta had’u, duk iya hasashenka saidai kayi amma tabbatarwa saikazo ciki”.
“Wannan gaskiyane k’anwata, ALLAH dai yasa mudace. Yanzu jeki fara shiga wanka dai”.
“To aunty”.
Sosai Jiddah kejin dad’in kasancewa da Matar, dukda kasancewarta Y’ar gayu hakan baisa ta nuna ta fitaba, gashima ta girmeta, dan ko aunty Nafisarsu ma zata iya girma, amma aunty Zulai itama zata iya girmarta.
“K’anwata Muna tare awanni masu yawa amma bamusan sunan junaba, ni sunana Siyama, Matar malaminku Mustafa”.
Sosai Jiddah tad’an waro ido waje, “Lah Aunty dama ina tare da Matar malam ce? Amma kinada kirki wlhy”.
Dariya sosai Siyama tayi (ina fata kun gane, k’anwar Aliyu) kafin tace, “Kanwata kinada abin dariya wlhy, k ya sunanki?”.
“Sunana Jiddah Aunty”.
“Masha ALLAH, ashema mamanace ni”.
Murmushi Jiddah tai kawai batace komaiba.
Kasancewar Siyama da Jiddah sai ya d’auke Mata kewar y’an uwanta da Ummanta, dukda k’asan zuciyarta Na begensu, dandanan suka Saki jiki da juna, harma hakan yabama Malam Mustafa da Uncle yahaya mamaki.
Washe Gari Malam Mustafa da wasu manyan malamai y’an Najeriya suka zauna da Jiddah, abin yabata mamaki dan tazatafa sukad’aine sukazo, Ashe harda malamin nan data ta6a gani a taron k’arama juna sani Na Abuja (Malam Abdul-ra’uff), tsuma jikinta yaytayi ganinsu duk maza a wajen, amma haka ta dake tana karanto duk addu’ar datazo gareta, sauk’intama d’an nesa dasu ta zauna, dukda AC dake wajen sai zufa takeyi, Malam Abdul-ra’uff ne kawai yalura da halin da Jiddah ke a ciki, dan haka saita bashi tausayi sosai.
Tambayoyi sukaita Mata domin k’ara tabbatar da nagartarta, inda tai kuskure suyi Mata gyara da fad’ad’a Mata bayani akan abun, duk kuma yanda abun zai iya kasancewa sun Mata bayani, tareda Addu’ar Neman dacewa.
Jiddah ta nutsu sosai domin kuma fahimta, Alhmdllh kuma ta fahimci kaso mafi yawa a ciki, inda kuma bata fahimtaba sosai takan kuma tambaya. Sunyi zama kusan Na awa biyu da Jiddah, Wanda ikon ALLAH ne kawai yabata damar kasancewa zuwa wannan lokacin batareda samun matsalaba, danma Malam Abdul-ra’uff dayaga sosai take a takure yay Mata addu’a cikin ruwa yabata Tasha, shinema takuma samun nutsuwar zaman wajen, bayan sun kamala zaman akad’anyi hotuna kafin su fito suka rankaya Massalaci.
Ai tuni Jiddah tafara hawaye ganinta gaban ka’aba, tashin farko Addu’ar shiriya ta farama mahaifinta, sai Ummanta da Uncle yahaya, kafin nan y’an Uwanta, ta d’ora da addu’ar fatan ALLAH yabasu mazaje nagari itada y’an uwanta da dukkan al’ummar musulmi.
Basubar massalaci ba sai la’asar, dan acan suka had’u da Siyama da Uncle yahaya.
*_Ranar Musabaqa_*
Yau dasu Jiddah suka cika kwana biyu a saudiyya ne ta kasance ranar musabaqar data kawosu, tunda safe suka tafi *Riyadh* inda taron zai gudana, duk yanda Zan fasalta muku abin bazaku fahimtaba, amma kowa ya k’iyasta a ransa.
Tarone Na taurarin al’ummar musulmai, dolene kaganka a wajen kaji kwalla ya cika idonka, Addinin isalama addini Mai nagarta da aminci, duk Wanda ya tsinci kansa a ciki ya godema ALLAH.
Sai Jiddah taga mu bak’ak’e y’an tsirarine a wajen, saima kayi duba na tsanaki zaka iya zazzak’ulomu, babu yaran da kakeji a wajen yana tashi sai larabci, Su Jiddah Matan an killacesune awani glass da zasu iya kallon komi ke gudana a wajen, ankuma kaimusu abinda zasu rimgajin magana shima, babu ruwansu da mazan. Hakan ba k’aramin farin ciki ya saka Jiddah ba, dukda dai tsorone fal ranta, dan ita yaran larabawannan sun tsoratata, tana tunanin Anya kuwa zata iya Kai labari a gasarnan?.
A k’asashen Africa gaba d’aya k’asa kusan biyarce ta halacci taron, sauran duk yankin fararen larabawane dawasu d’aid’aikun kasashen turawa..
Tun Jiddah Na d’ari-d’ari da y’ammatan kusa da ita har suka janye ra’ayinta tafara tanka musu, dukda larabcinta baikai nasu kwarewaba tana k’ok’ari itama. tuni hirar ilimi ta 6arke tsakainta dasu Ummusulaim. Sai hotuna suke musu, Jiddah bata ta6a damuwa da rashin wayaba sai yau, saitaji inama itama tanada ita ta d’auki hotunan domin tarihi……..
Tunanintane ya katse jin an Kira sunanta, d’ago kanta tayi ta kalli Aunty Siyama, Aunty siyama ta mik’a Mata wayarta.
“Aunty miya faru? Ajiye miki zanyi?”.
“A’a kema ki d’auki hotunan kodan tarihi”.
Godiya Jiddah taimata sosai, yayinda tuni Aunty Siyama ta juya ta fita wajen da suma aka tanadar musu kusada su Jiddah.
Suna tsaka da hotunansu wata sassanyar murya data fara jan k’ira’ar Al-Quran ta daki kunnuwansu. Kusan duk a tare suka kalli wajen, dan da hankalinsu duk baya wajen, shiyyasa basusan hidimar da akeba.
Mamaki al’ajabi mai girma ya Kama Jiddah, ganin mamalakkin wannan murya ya fitone cikin jinsin bak’ak’e irinta, sosai ta shagala da kallonsa karatunsa Na ratsata da k’ara Mata nutsuwa, batama San sanda tafara masa video recording ba kamar yanda sauran mutane ketayi, ga wajen yayi tsit bakajin sautin komai saina fitar muryar *Sheikh Aliyu Abdul-ra’uff Maina*, abin birgewa da alfaharin duk wani Mai alak’a da wannan *TAURARO*.
Saida ya kai har k’arshen Suratul Al-Ahazab sannan ya dakata yana share kwallar data cika idonsa saboda yana karantawa zuciyarsa Na fassara abinda Surar ta kunsa, hakama masana aduniyar ilimi suna saurarensa da fashin bak’i a zukatansu.
Saida yaja doguwar Addu’a kafin yakoma ma zauninsa, Mutane dayawa ya birgesu dajin k’aunarsa, mahaifinsa kam shikad’ai yasan yanda yakejin d’unbin k’aunar Aliyu a ransa, dukkannin burinsa akan ilimin y’ay’ansa Aliyu ya cika masashi.
Taro yacigaba da gudana bisa bigiren abinda ya tara mutane, dan anfara gudanar da gasa cikin nutsuwa. Wajen tsit yake bakajin komai sai sautun karatu dakuma gyara dasu Aliyu keyima yaran dan sune alk’alan Musabaqar.
Lokacin da aka ambaci Nigeria sosai cikin Jiddah ya juya, dak’yar ta iya janyo numfashi da karanto addu’a sannan tasamu mik’ewa zuwa inda kowa ke zuwa ya zauna.
Tunda ta fito ya kafeta da kallo ta k’asan ido, tashin farko yabata maki d’ari bisa d’ari a 6angaren tafiyar Nutsuwa, harta k’araso wajen yana kallonta, amma bazaka ta6a fahimtar hakanba saishi da yakeyi.
Cikin hashen larabci balaraben malamin yafara Mata tambayoyi kafin yabata izinin tsunduma ga abinda ya ajiyesu.
Sura kawai ya za6omata a cikin Al-Qurani tunda tace ta sauke a hadda ma sai abinda ba’a rasaba.
Aliyu daya d’auke kansa kamar bashine kemata kallon k’asan idoba d’azun yana saurarensu, jin Surar da Sheikh Mohammed Ali ya cafko mata saida yad’an d’ago kai ya kallesu, aransa kuwa yana ayyana shikenan sun fad’i, danshifa bai tabbatar da yarinyarnan zata iya wani abun kwarai ba, dan sanyinta yayi yawa……….
Tunaninsa ya katse lokacin da nutsatstsiyar muryarta mai zak’i da sanyi tafara karatu cikin Suratul Al-Furqan kamar yanda aka bata Umarni.
Wani irin sanyi da nutsuwa suka ratsa zuciyar Aliyu, ya lumshe idanunsa yana mai fassara Ayoyin daki-daki.
Gurin yay tsit ita kawai ake saurare.
Itadai Jiddah kanta na a k’asa bata kallon kowa a cikinsu, karatunta kawai take idanunta na zurarar da hawaye. Bata tsayaba sai da aka dakatar da ita, aka kuma d’akko mata wata surar.
Hawayenta ta share jikinta Na cigaba da tsuma tafara karanto suratul Al-Hujurat, nanma tayi nisa sosai aka kuma tsaidata takoma Suratul Al-Mutaffifin, aka sake maida Suratul Al-Ma’arij, ayanzukam sosai Jiddah take kuka a wannan sura ta al-ma’arij, saboda abinda take magana akai Na azaba ga wad’anda suka bijirema gaskiya da Ni’ima ga masu ruk’o da gaskiya, tsoratarwa da ranar hisabi da sakamakon kowa, saida takai har k’arshenta sannan aka maidata suratul Al-Zumar, nanma tayi nisa aka tsaidata aka dawo da ita Suratul Al-Ibrahim, tanayidai tana shartar kwallanta aka kuma maidata Suratul Al-‘Imran.
Daganan aka tsaidata, Handkerchief d’in gabansa ya mik’a Mata ta Y’ar k’ofar gilas d’in data raba tsakaninsu, ta kar6a yayinda idonsu ya shiga cikin Na juna, cikin fad’uwar gaba tai saurin janye nata tana jawo numfashi dak’yar, wani k’amshi mai dad’i yadaki hancinta lokacin datakai handkerchief d’in kusada fuskarta, idanu ta lumshe ahankali ta furta “Masha ALLAH”. saida ta goge fuskarta fes dukda hawayen nacigaba da zubowa kafin ta mik’a masa. Kansa ya girgiza mata yana d’auke kansa, a kan la66anta ta furta “Jazakallahu khairan”, ya amsa da “Amin” shima a saman la66ansa, dan yana kallonta ta gefen idonsa.
Anfara Mata tambayoyin daduk suka kamata, harma acikin wasu littatafan daban, cikin amincin ALLAH tana bada amsa yanda ya kamata. Duk sanda Sheikh Aliyu zaima Jiddah tambaya sai idonsu yashiga na juna, saidai kowanne yay saurin janyewa.
Dad’i sosai yacika wakilan Nageria irinsu Malam Abdul-ra’uff da manyan malamai, Sarkin Musulmai da sauransu, saboda jin yanda Jiddah ke amsa komai daki-daki, kurakuran da ake samu daga gareta k’alilanne wad’anda ba’a rasaba.
Bayan an gama da Jiddah aka cigaba da kiran d’alibai.
Saida kowa yayi sannan aka tashi saikuma an tantance wad’anda suka tsallake.
★★★★
Washe Gari Jiddah tasamu nasarar shiga cikin k’asashe bakwai wad’anda suka tsallake, a ranarma Jiddah tasha kuka wajen yin nata.
Washe gari again nanma aka kuma fafatawa da k’asashe uku da suka tsallake, ciki harda Jiddah mai wakiltar Najeriya.
Randa akai Na k’arshe ba k’aramar cika wajen yayiba, dan harda Sarkin Saudia da wasu manya-manyan mutane da duniyar Musulinci ke ji dasu, wad’anda mukeji sunayensu a bakunan malamanmu da litatafai Na Addini da suka riskemu.
A yau kam bak’aramin rud’u Jiddah ta shigaba, saboda tambayoyi su Aliyu ke zak’ulo musu masu wahala da tsunduma kwakwalwa cikin dogon nazari. Kasancewar an Fara da wuri kuma kasashe Uku ne kawai suka fafata sai aka gama da wuri, Nageria ita kad’aice takai wannan mataki a yankin Africa.
Bayan kammalawar su Jiddah manyan malamai suka koma bayan fage domin tantancewa, yayinda a wajen taro aka cigaba da gudanar da lectures masu ratsa jikkuna da duniya gaba d’aya.
Ba’a samu nutsuwar sanar da sakamako ba sai bayan salar zuhur.
Kowa dai kunnensa a bud’e yake da fatan k’asarsa tazo Na farko.
Wajen yay tsit an zubama Manyan wajen idanu dake Magana k’asa-k’asa.
An Kira *Azra Asen* Mai wakiltar k’asar *Turkiyya* wadda itace tazo Na uku.
Gaba d’aya wajen yad’auki kabbara, Azra ta fita inda ake buk’atar ganinta, bayan jinjina da yaba Mata da addu’ar fatan alkairi agareta aka bata k’yautar data samu da k’yautar Nasarar datasamoma k’asarta.
Gaban Jiddah nata fad’uwa da wasiwasin ta farkoce ita kota biyu….
Tunanintane ya katse lokacin da ake shelanta kiran sunan *Arwa Saiyyad* Mai wakiltar k’asar Saudiyya, wadda itace ta biyu. Itama dai tasamu k’aututtukan dasukafi Na Azra tareda fatan alkairi, inda y’an saudia sukai murna, dukda sunyi burin zuwa Na d’aya suma.
Jikin Jiddah duk yay sanyi, azatonta ko ancire sunantane, sai tajiyo Ana kwala kiran sunan *Jiddah Zakari Yaro* *Najeriya* sosai jikinta yahau rawa, saida taimakon Ummusulaim dasuka zama k’awaye ta iya mik’ewa, tafiya take tamkar zata fad’i saboda sassarfa da idanun mutane, ga lalurarta ta tsoron kasancewa muhali d’aya da maza, danma Ubangiji ya sauk’ak’a lamarin..
Dak’yar ta iya k’arasawa garesu. Doguwar Addu’a da jinjina ga Jiddah da iyayenta da malamanta da k’asarta sosai akayi, kafin a damk’a Mata k’autar nasararta dakuma k’yaututtuka da malamai daban-daban wad’an suka fito a k’asashe daban-daban, da manyan attajiran da suka halarci wannan gagarumar Mubabaqa. Kuka kawai Jiddah ta sakamusu harda sheshsheka, inda mutane dayawa suke tayata musamman ma mu y’an Najeriya damuke cikin farinciki.
Aliyu dake murmushi yasaka handkerchief ya d’auke hawayen da suka cika masa idanu, hakama Uncle yahya, su malam mustafa malam Abdul-ra’uff, Sarkin musulmai da sauran malamai dasuka halarci taron y’an Nigeriya duk suna tare da tsantsar farinciki, Aunty Siyama jitake tamkar k’anwarta ciki d’aya, dad’i dukya lullu6eta.
Abubuwa sunciga da gudana kafin taro ya tashi lafiya, masu murna nayi masu kuka nayi.
A ranar su Jiddah suka baro birnin Riyadh zuwa Makkah.
Kowa saiji yake da Jiddah, sai nan-nan su malam Abdul-ra’uff sukeyo da Jiddah, yayinda dad’i ya cikata, gata ga Sarkin musulmai da manyan malamai Na k’asarta da takejin labarinsu kojin wa’azinsu a redio ko TV.
Saidai abinda yabata mamaki bataga malam Aliyu ba tun barowarsu Riyadh, dan badashi suka taho Makkah ba, batadai tambayi kowaba tayi shiru da bakinta, amma haka kawai taji tana kwad’ayin ganinsa kodan tamasa godiyar Handky daya bata ranar, dan dataji d’an Najeriya ne kuma d’an mutumin da zuciyarta take kauna da girmamawa sai dad’i ya kamata, ashema tana sauraren tafseer nasa sosai batasan shi baneba sai yanzu.
Uncle yahya kam fad’a muku irin farin cikin daya tsinci kansa ai 6ata lokacine ma.
Labari kuwa yakai Najeriya tuni, sai hotunan Jiddah ke yawo a jaridu da televisions.
Lokacin da zance yakai kunnen su Umma ai kuka kawai ta sanya Na dad’i, tuni labari yagama zagaye dangi, kowa burinsa Jiddah tadawo ya k’ara ganinta. (Saikace sun manta fuskarta????), sundake sai sayen jarida suke suk’ara ganinta, su Zarah ma har Umma suka sayomawa, aiko tasaka k’asan gado ta 6oye bayan sungama Karantawa, wai zata adana tarihi????????. Zumud’in dawowar Jiddah garesu dukya cikasu.
Lokacin da aka nuna Jiddah a labarai Abba da Hajia Hindu suka gani Hajia Hindu rud’ewa tayi, shikansa Abba yau saiyaji wani iri, yarinyarsace a tsakkiyar manyan mutàne da duniyar musulinci ke ji dasu, duk surutan da Hajia Hindu kemasa baibi takantaba yatashi yashige d’akinsa saboda wani jiri dayakeji yana Neman kwasarsa.
hakance takuma kasancewa a gidan Alhaji Garba, dan gaddama suka kwaso suka dire akan ba Jiddah data zauna a gidan baceba, yayinda Ashir keta rantsuwa da ALLAH itace. Alhaji garba yace bai yardaba saiya bincika.
Yayinda wancan cakwakiyar ke faruwa a Najeriya Su Jiddah suna can suna gudar da Umrah a Makkah, tareda zagayen guraren tarihi domin k’arin ilimi, yayin da daga baya kuma suka tattarasukak nufi Birnin Madina.
Kwanansu bakwai a Madina Gari Mai tarin Ni’ima da dad’in zama, Wanda duk muminin daya shiga baya fatan yaga ya fita, kuka dai Jiddah ta shashi yayinda taganta gaban kabarin MANZON ALLAH (S.A.W) da ahalin gidansa.
Ranar jinta take wata iri daban tamkar ba itaba.
Duk inda yakamata suje wajen tarihi malam Abdul-ra’uff shine jagoransu, itadai Jiddah tana k’ara mamaki Ina Aliyu ya shiga?.
Gaba d’aya kwanakin su Jiddah ashirin Cif da tafiya suka juyo k’asarsu ta haihuwa Najeriya cikeda farin cikin d’umbin nasaarorin da suka k’unso………….✍????
*_Barkanmu da Juma’a sweet sister’s????????????????????_*
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*????????????