NAFEESAT 1-END

NAFEESAT Page 11 to 20

Still Murmushi tayi idanun ta akan titi, sau da dama tana mamakin yanda Baffa yake nuna mata kulawa fiye da tunanin ta, kuma yake yin duk abinda take so yake barin duk abinda ba ta so, tasan cewa yayan nata me ƙaunar ta ne tun tana ƙarama don ba ya son ɓacin ranta.

       Yana yin parcking a haraban asibitin ya fito ya zo ya buɗe mata yana nuna mata hanya da hannu, cike da murmushi a face ɗin sa yace, “Yauwa Gimbiya fito an kawo”.

Sunan da ya kira ta dashi ya saka tayi dariya tana kallon sa cike da farin ciki, zuro ƙafafun ta waje tayi ta fito, sannan ya rufe suka jera sukayi ciki.

               ⚫⚫⚫

“I told you to come in at 08:00am o’clock. Me ya tsayar da ke?” Doc. Said yayi maganar yana juyawa cikin kujeran sa

Fari tayi da idanun ta sannan tace, “kai ma ban da abun ka ya Docta; kasan ba a raba mu da ɗan shafe-shafe na kwalliya, kuma ka ga 08:00am yayi wuri da yawa”.

Murmushi ya saki yana sakar mata wani shu’umin kallo

“Uhmm Sulaima kenan! That’s why I love you more sabida wannan kwalliyan naki, ko kaɗan baki wasa da jikin ki wajen kin ga kin fito kin burge kowa, wasu kuwa ko a jikin su be dame su ba”. Yaƙarishe maganar da taɓe bakin sa

Dariya tayi tana sake lanƙwashe murya tace, “Ya Dacta kenan! Ni fa nasan da wacce kake yi, kuma kasan zan iya zuwa in faɗa mata”.

Waro ido yayi yana dariya yace, “rufa min asiri don Allah karki haɗa ni da ita kin san halin ta, but yaushe Ni zaki bani dama ne wai? Na gaji da wannan kwane-kwanen da kike min”.

Sulaima tace, “Ya Dacta Ni fa gaskiya ba na tunanin zan iya harka da kai, ko ka manta kai Mijin Yayata ce? Haba dai ka sauya tunani mana Ni gaskiya bazan iya ba”. Taƙarike maganar a shagwaɓe

Lumshe idanu yayi yana sake kallon ta cike da tsananin sha’awar ta, sai da ya ɗago daga jikin kujeran ya ɗaura hannayen sa kan Deks ɗin sa sannan yace, “Sulaima kin san ni; na sanki, why kike son haramta min kan ki? karki manta fa ba wai na ce miki auren ki zan yi ba bare ki kawo wani zancen Ƴar uwan ki, Ni dai don Allah ki bani dama mu more rayuwan mu tare kin san bazan iya haƙura dake ba, kinga matsayin ki daban matsayin ƴar uwanki daban a waje na”.

Murmushi tayi tana girgiza kanta cike da yauƙi tace, “ya Dacta let’s change our talk, muyi abinda ya kawo ni ka ga ina da inda zan je”.

Doc. Said yace, “to shikenan tunda kin fi son haka, amma ki sani ba wai na bar maganar bane kenan, yanzu ya aka yi kika bar ciki ya shiga jikin ki?”

“Hmm tsautsayi mana, wlh nayi mamaki da naje Hospital aka gwada Ni wai ciki ne dani, kuma duk wani matakan tsaron da na saba yi nayi but abun kamar almara”.

Ɗage kafaɗa yayi yace, “any way muje ki hau gadon in duba ki mu gani, don Nima Ina da aiki yanzu a gaba na”.

Tashi tayi tana cire gyalen jikin ta ta nufi wajen gadon, shima ya tashi ya bi bayan ta.

             ⚫⚫⚫

    Zuwan ta Office ta tarar da patients ɗin ta suna jiran ta, yau bata zo akan lokaci ba hakan yasaka har suka rigata zuwa tunda ƙarfe 10:00am zata soma duba su, yanzu gashi har goma saura

Tana shiga ta saka rigan aikin ta sannan ta zauna taba su umarnin shigowa ɗaya bayan ɗaya tana duba su, tayi wajen awanni biyu tana faman duba su sannan ta gama ta tashi ta shiga Toilet tayi uzurin ta ta fito, wasu files ta ɗauka ta fita ta nufi rooms ɗin patients ɗin ta masu jinya

Tana shiga da gadon farko ta fara, taƙarisa da fara’an ta tana gaishe da matar dake jinyar wata burduwan yarinya, bayan sun gaisa cikin faram-faram sannan Ɗahira tace, “Mama har yanzu bata farka bane?”

Mama tace, “ta farka jiya da daddare, kuma Dacta ɗin da kika ce zata zo ta duba ta ita ta duba ta, ga ma takardan da tace, “in baki”. Ta miƙo mata takardan

Ita kuma ta’amsa tana dubawa, sai da ta gama dubawa sannan ta kalli Maman tace, “Mama to ya jikin nata tana samun sauƙi ko?”

“Ai alhmadulillah Dacta ba kamar jiya da safe ba, ta samu sauƙi sosai”.

Gyaɗa kai Ɗahira tayi tana rubutu cikin wani file, sai da ta gama ta matso kusa da yarinyan ta soma duba ta sannan ta ɗago tana kallon Maman tace, “Mama insha Allahu komi zai zo da sauƙi, idan ta farka sai ta soma amfani da ruwa me ɗumi ana mata tsarki, daga yau sai a soma mata amfani dashi ko yaushe insha Allahu komi zai zama normal”.

“To Dacta mun gode ƙwarai Allah ya saka da alheri”.

Murmushi Ɗahira tayi tace, “ameen Mama Babu komi ai, Allah Ubangiji ya bata lafiya”.

Mama ta’amsa da “ameen” tana sake mata godiya

Daga nan Ɗahira gadon gaba ta wuce, itama Yarinya ce budurwa, wata shirgegiyar mata take jinyar ta, sai dai yarinyan bata kai wancan shekaru ba don baza ta fi 13yrs ba

Bayan sun gaisa da matar ta tambaye ta jikin yarinyan

Matar cike da sanyin murya kamar za tayi kuka tace, “Doctor babu sauƙi wlh yarinyan nan tana shan wahala sosai, tun jiya farkawar ta biyu, kuma duk idan ta farka a firgice take tashi tai ta ihu tana surutai”.

Ɗahira da take bin yarinyan da kallo cike da tsananin tausayin ta ta juyo tana kallon Matar tace, “Mama ki kwantar da hankalin ki insha Allahu zan yi iya bakin ƙoƙari na wajen na ga ta samu lafiya, Allah zai saka mata duk wanda yayi mata wannan abun”.

Share hawayen ta matar tayi tace, “ameen Dactor na gode ƙwarai”.

Daga nan Ɗahira duba yarinyan ta soma yi, ta jima tana duba ta kafin ta saka mata ruwa tayi mata allura ta cikin ruwan sannan tayi mata sallama ta wuce

Sauran gadon ta nufa ta duba su su ma, sannan taje wasu Rooms ɗin, sai da ta gama ta koma Office ɗin ta.

           Tana shiga taga Baffa zaune yana kallon ta yana sakar mata murmushi

Itama murmushin tayi masa ta shigo ta nufi wajen zaman ta ta zauna, cikin muryan ta na yanga take cewa, “Yaya na yaushe ka shigo?”

“I Come in right now, what’s your job?”

“Alhmadulillah. How’s yours?”

Murmushi yayi yana shafa suman kansa yace, “uhmm sai godiyar Allah my Sister amma babu daɗi”.

Dariya Ɗahira tayi tana kallon sa tace, “kai kenan Yaya, kai da ka jima tsawon shekaru kana aiki kake faɗan haka ina ga Ni da jiya na soma? wlh Yaya da wahala sosai aikin nan duk na gaji”. Taƙarike maganar ta tana lanƙwashewa ajikin kujeran

Baffa dariya yayi yace, “oh my dear sister ke dai kawai ki ce ke raguwa ce, amma daga fara aiki kice kin soma gajiya?”.

Murmusawa kawai tayi tana ɗan lumshe idanuwan nata don tasan halin yayan nata tsokana yake ji, ita kuma ta gaji ko maganar ma  daƙyar take amsa masa

Baffa da ya tsare ta da idanun sa yana sakin murmushi me ƙara masa kyau yace, “sis Naga da alamun kin gaji tashi muje muci abinci”.

Shiru tayi tana ɗan tunani

Hakan ya saka Baffa yace, “Do you have a job?”

Girgiza masa kanta tayi tana miƙewa ta zare rigan aikin tace, “No let’s go”.

Tashi yayi shima cike da jindaɗi suka fito suka jera har wajen lifter, shiga suka yi yakai su downstairs, mota suka shiga suka bar cikin asibitin, babu nisa da Resturant ɗin da suka je.

_More Comments more post_????????‍♀️????????‍♀️????????‍♀️????????‍♀️

[5/23, 9:05 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????

             *FAMILY DOCTORS*

                         ????

????????????????????????????????????????

????????????????????????????

  *NAFEESAT RETURN*

????????????????????????????

*MALLAKAR:*

                 _NAFISAT ISMA’IL LAWAL_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*????????‍

Previous page 1 2 3 4 5 6Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button