NOOR AL HAYAT 21-30

✨ *NOOR-AL-HAYAT* ✨
Bude motar Sudais yyi ya fita yana kallonta yace “Come down” a hankali ta fito gabanta na faduwa, ya nufi gate din gidan ta bi bayansa kamar me tausayin kasa, da farko Usman mai gadi ya tsaya tambayarsa wanda yake nema amma ganin khadijah ya fito da sauri yana kallonta da mamaki yace “Khadijah?” Ta kirkiri murmushi ta gaishesa, tuni Sudais ya shiga gidan, Khadijah ta bi bayansa Usman yace “Duk kika daga ma kowa hankali ana ta neman ki har station Hajiya ta kai report, to Alhmdllh tunda Allah ya bayyana ki, Alhmdllh” ita dai Khadijah bata ce komai ba ta kalli parking space xuciyarta na bugawa ta ga ba motar Aliyu da na Mumy, Sudais ya danna bell din entrance na gidan a hankali, sau uku yana danna bell din kafin a bude kofar, Anty khadijah ce tsaye bakin kofar kana ganinta kasan bacci take, idanuwanta suka bude sosai ganin khadijah dake gefen Sudais a tsaye tsoro dauke fuskarta, Sudais da yana ganin ta yyi guessing ita ce Anty khadijah ganin kallon da take ma khadijah yace “Assalamu alaikum” hade rai Anty khadijah tayi tace “Wa’alaikumus salam” daga haka ta kalli khadijah tace “Lafiya? Daga ina? Wa ku ke nema?” Sudais yace “Aliyu muke nema” daga haka ya shiga parlorn, Khadijah ta kasa shiga saboda tsoro, Wani kallo Sudais yyi mata yace “Come in” a hankali ta daga kafa ta bi gefen Anty khadijah ta shiga cikin parlorn ita ma, tuni Sudais ya isa kan kujera ya xauna, Anty khadijah dake kallonsa da mamaki tace “Malam nan din fa gidan matan aure ne ka shigo, lafiya? wa kake nema?” Yace “Shi yasa nayi sallama kuma kika amsa min kafin in shigo hajiya” Anty khadijah tace “Me kuma ya hada ku da Aliyu ku ke neman sa?” Sudais yace “Xai fi kyau idan ma bai nan ki yi hakuri ki kira mana shi ya dawo, and mahaifiyarsa hope tana nan?” Anty khadijah tayi mitsi mitsi da ido cike da masifa tace “Nima uwarsa ce ae halak malak, sannan Aliyu bai ma kasar gaba daya idan xaka fadi abinda ke tafe da kai malam ka fada don bacci nake ka taso ni…” Shiru Sudais yyi na d’an lkci kafin ya nuna mata khadijah yace “Kin san wannan yarinyar koh?” Ta kalli khadijah ta kara tsuke fuska tamau tace “Kwarai kuwa, yar aikin da muka dauka kwanaki kenan ta lalata mana xumunci ta shisshige ma d’a na, ta raba ni da shi ina ji ina ganin bana iya cewa komai, wannan shari’ar kuma sai a lahira don duk da barin ta gidan har yau abubuwan da ta cakuda bai gyaru ba, Allah ya isa tsakaninmu da ita” Kuka Khadijah ta fara yi a hankali ta durkusa inda take tsaye, Sudais ya ciro handkerchief dinsa ya share fuskarsa yana kallon khadijah yace “Dena wannan kukan xa kiyi ki bude baki da kanki kiyi mata bayani yanxu” Anty khadijah ta dawo tsakiyar parlorn da sauri tana xaro ido tace “Bayanin me?” Khadijah ta dinga goge hawayen da ya ki tsaya mata, kare mata kallo Anty khadijah ta shiga yi, can ta fashe da dariya irin na mugunta lkci daya kuma ta tsayar da dariyar tana ma Sudais wani matsiyacin kallo tace “Xuwa kayi da ita tace mana tana dauke da ciki?” Sudais yace “Alhmdllh fine, unfortunately kin ma san halin d’an naki kenan” Khadijah ta hade kai da gwiwa tana kuka a raunane, Anty khadijah ta fashe da wani shegen dariya kamar bokanniya tayi mai isarta tayi shiru sannan ta nuna masa kofa fuskarta kamar bata taba dariya ba idonta yyi mitsi mitsi tace “Tun muna mu uku a nan bamu fi haka ba ku tashi ku fice mana a gida” a tsawace ta kare maganar, sudais ya tabe baki yace “Tsawar ki ko ihun ki fa baxae razana ni ba malama… Don haka hold it xai maki amfani gaba a wani wajen” Anty khadijah na huci tace “Xan nuna maka a nan ma yana da amfani, har wannan karuwar xata xo ta makala ma d’ana cikin shegen da tayi a wani wajen saboda ita matsiyaciya ce” Sudais yace “Toh abu mai sauki sai mu je asibiti a ga kwanakin cikin nawa, idan yyi dai dai da kwankin da ya koreta ta bar gidan to nasa ne in sha Allah” Anty khadijah tayi shiru jin abinda sudais yace, auuuu wato Aliyun ne ma ya koreta ashe, ita dai ta dawo kauyen da taje bayan kwana biyu da tafiyarta taji wai ba a ga khadijah ba ko sama ko kasa har station an kai report, Ranta yyi mugun baci a lkcn don bata so Khadijah ta tafi haka nan bata walakanta ta ba kmr yanda ta yi alkawari, me yasa xata tafi bata gama cika burin ta a kan ta ba har hawaye sai da tayi sbda bakin cikin kudin mota da kudin magani da tayi asara, suree a lkcn tayi mugun mamakin yanda Aliyu bai wani damu can ba kamar yanda mahaifiyarsa da baby suka damu amma ita bata taba kawo cewar shi ne ma ya koreta ba, Muryar Sudais ya dawo da Anty khadijah “Hajiya kin yi shiru daga nayi xancen asibiti” abinda ya fada kenan yana kallonta, ta yi masa wani shegen kallo tace “Ji gantalalle, to tunanin da nake daban malam, kuma asibitin ya ci kaza kazan sa baxa a je ba, idan ma cikin Aliyu take dauke da, idan ma ba nasa ba… bbu wanda ya isa ya shigo mana da shege cikin xuri’ar mu, I can swear with the Qur’an fasikanci ba halin Aliyu bane idan ma yyi Ita ta koya masa don kullum dakin sa take yini, wa ya sani ma ko har kwana tana yi can, yayata ba mai xama bace don yanxu xancen da nake ma bata kasar, kullum nice ke tare da su, wai hanata shige ma Aliyu da nake har shi ya janyo min bakin jini gun ta, ta janyo d’a na ya daina ganina da gashi a gidan, yanxu tun muna magana irin ta mutane ba mu dawo na mahaukata ba ku tashi ku fice min a gida kar ku ga d other side of me, ku fita nace” a tsawace ta kare maganar, Sudais dake ta kallonta yyi murmushi yace “Toh cikin nasa dake jikinta tayi ya da shi kenan?” a takaice Anty khadijah tace “Ta xubar, don kaf xuri’ar mu ba shege kuma baxa a fara a kan d’a na ba, idan kuma taga xata iya sai ta raini cikin ta haifa ma kanta ajalinta….” Khadijah dai banda kuka babu abinda take, Sudais ya mike yace “Good, I made her brought me here for just 2 reasons, na farko… is to find out how sincere she is, and na karshe… Is just to let you and ur son knw d pains u are about putting the innocent orphan coz ni dai nasan definitely baxa ku taba accepting cikin ba, kun rabata da warce take da ita a duniya, kun goga mata bakin fenti da ba lallai ya gogu ba har karshen rayuwarta, amma Hajiya ina son ku sani, kamar yanda marainiyar nan tayi bankwana da farin ciki to wallahil azeem kuma hakan ne xai same ku a a xuri’ar ku barin shi Aliyun, He will know no peace da hakkin marainiya a kansa, who knows tunda tace likita ne shi signs na pregnancy din ya gani ya koreta, in sha Allahu sai kun yi da kun sanin abinda ku ka aikata ma yarinyar nan” yana kai wa nan ya karasa gabanta ya ciro ID card a gaban rigarsa ya nuna mata yace “Barrister Aliyu Umar, or just sudais.. we might meet some other time in sha Allah…. Or probably not” ya fadi hakan yana gesturing da hannunsa, khadijah da gabanta yayi mugun faduwa ta dago da sauri tana kallonsa wasu hawayen masu xafi na xubo mata, wani dariya Anty khadijah tayi tana tafe hannu tace “Are you threatening us?” Ya girgixa kai yana murmushi yace “Noo, not at all, kilan idan kika gaya masa aika aikan da yyi xai iya biyota, here is my complimentary card…” Ya ajiye card din gefen kujera, dauka tayi ta yayyage ta xubar nan kasa a gabansa tana huci tana kallonsa, yayi murmushi ya kalli khadijah yace “Tashi mu je” khadijah ta mike a hankali ta bi bayan sudais da har ya isa kofa, tana goge hawayen ta har ta iso gun motarsa, shi ya bude mata motar ta shiga ya rufe ya xaga ya shiga maxaunin driver, har suka hau titi bai ce komai ba ta hade kai da gwiwa tana rera kuka ko xata ji saukin tukukin da xuciyarta ke mata, A bakin hanya sudais yyi parking ganin masallaci ya fita don yin sllh da bottle water ya dawo motar, bayan ya sha ruwan ya ci gaba da driving dinsa, ya hade rai yace “Will you stop those tears and start thinking of how to face reality” ba shiri tayi shiru tana shessheka ya ci gaba da tukin sa. Dab da isha suka shigo kano, direct ya nufi hotel bayan yyi parking yace “Gobe da safe xa mu je gidan Step mum dinki” a tsorace take kallonsa, ya bude motar ya fita yace “Ki fito” daga haka ya wuce reception, daki biyu ya amsar masu, ya siya masu abinci a nan reception din sannan suka wuce sama, yana tsaye daga bakin kofar dakin da ya bude mata ta shiga na hotel din yace “Make sure you try and pray, ki daure ki ci abinci kiyi wanka sannan ki kwanta” spare ki ya cire yace “Don’t leave the key jikin kofar” daga haka ya juya ya shiga nasa dakin, wanka kawai yyi, yyi sallah abincin ma bai iya ya ci da yawa ba ya kira mami, bayan sun gaisa ta tambayesa ya hanya, yace “Alhmdllh mami gobe xan dawo in sha Allah” tace “Toh maa sha Allah, in ji anyi nasara” yace “In sha Allah mami” tace “Toh Alhmdllh” a hankali yace “Am very tired mami xan kwanta” tace “Toh Allah huta gajiya” yace “Ameen” daga haka ya kwanta nan da nan bacci me nauyi ya daukesa, bai farka ba sai karfe uku, mikewa yyi xaune da sauri ya dau shirt dinsa ya sa ya dau spare key dinta da ya cire ya fita dakin ya nufi nata, saka makullin yyi ciki yana addu’ar Allah yasa ta cire makulli jikin kofar, yana murdawa ya bude ya tura kofar dakin, xaune ya ganta ta jinginar da kanta jikin gado, ya karasa da sauri ya durkusa gabanta yace “Kin samu kin ci abincin kuwa Amira?” Shiru yyi yana kallonta ganin yanda idonta ya kumbura, ya sauke idonsa kan ledan abincin da ya ajiye mata jiya da daddare, bude ledan yyi yaga bata taba abincin ba, ya wani hade rai yace “What’s wrong with you, tun dare kike kuka har yanxu?” Ta girgixa masa kai da sauri muryarta na rawa ta nuna masa kirjinta tace “Yana min ciwo” sauke ajiyar xuciya yyi murya can kasa yace “Kin yi wankan?” Ta girgixa masa kai, yace “Sallah fah?” Nan ma girgixa masa kai tayi, mikewa yyi ya shiga bathroom da ke dakin ya hada mata ruwan wanka ya fito yace “Tashi ki je ki yi wanka, you will feel more better” a hankali ta tashi ta wuce bathroom din, yana ta xaune har ta fito da kayan ta da Hijab ta kwanta kan gado ta dukunkune waje daya, ya mike ya rufa mata bargo, ba a dau lkci ba ya ga alamar bacci ya dauketa, tashi yyi ya kashe wutan dakin ya nufi kofa ya fita ya rufe. Da asuba bayan sudais ya idar da sllh ya koma dakinta yaga har lkcn bacci take ya koma dakinsa shi ma ya kwanta. Da safe ya fita hotel din don nema mata kunu, wani almajiri da ya gani kan hanya ya ba kudin ya tafi gun masu siyar da kosai ya siyo masa kunu, yana ta jiransa gaban wani store har yaron ya dawo da kunun a cikin leda, karba yyi yyi masa godiya ya bar masa canjin dari takwas din don na Dari biyu yaron ya siya, ya mike ya amshi ruwa bakin store din da yake ya dawo kan bench ya xauna ya bude bottle water din ya sha kadan ya xubda sauran sannan ya juye kunun ledan a ciki ya mike ya koma hotel din, tashinta yyi daga baccin da take ganin tun jiya bbu abinda ta ci, ta tafi bayi ta kuskure bakinta kamar yanda ya ce mata, da alwala ta fito yana ta xaune yana jiran ta gama sallah, duk ta galabaita kafin ta idar, ya dawo kusa da ita ya mika mata bottle din kunun bayan ya bude yace “Gashi ki sha ko ba yawa kin ji” kai ta gyada masa ta karba ta kai baki a hankali har wani rawa hannunta yake, kusan rabi ta sha kunun ta ajiye ta jinginar da kanta da gado, yace “Ki daure ki kara kadan” ta girgixa kai da sauri tace “A’a xan yi amai idan na sha kuma” rufewa yyi yace “Toh ki kwanta kafin in yi wanka xa mu je can gidan step mum dinki” shiru ta yi ta bi sa da kallo har ya fita dakin, da yake ba ya rabo da spare clothes a motarsa can ya tafi ya dauko kayansa yana gama wanka ya canxa. Ko da ya dawo dakin idon Khadijah a lumshe yake duk da ba bacci take ba, tausayin kanta kawai take don bata san wani irin rayuwa xata fara yanxu ba kuma, ita da ba kowa gareta ba a duniyar, muryarsa da taji ya sa ta bude ido da sauri don bata ji shigowar sa ba, ta mike xaune yace “Let go, it’s almost nine yanxu” tashi tayi ta sauka daga kan gadon, ya dau ledan abincin jiya da bata ci ba ya fita tana biye da shi a baya, nan reception ya bada makullan dakin ya nufi wajen hotel din xuwa Parking lot, ya bude mata front seat ta shiga sannan ya xaga ya shiga maxaunin driver, sai da ya hau kan titi yace “Ina ne gidan step mum din naki yake?” Kamar xata yi kuka tace “Wllh tsoro nake ji kuma tace kar in kashe mata aure, I don’t want to be the cause of that” yana kallon titin gabansa yace “Kar ki damu you will remain inside the car, while we talk” kai ta gyada masa a hankali hawayen dake makale idonta ya sakko, yace “Clean those tears now” da sauri ta goge idonta, tana ta nuna masa hanyar gidan bayan sun shigo anguwar, ganin sun kusa a hankali tace “Plss ka tsaya da motar a nan kaga gidan can” ya tsayar da motar ya na kallon gidan da take nuna masa, kashe motar yyi yace “Ya sunan step mum din ki?” Tace “Hajiya Amina” bude side dinsa yayi ya fita, ta bi sa da kallo ganin yanda yake tafiya har ya isa kofar gidan ya tsaya, wani yaro ne ya fito gidan dake kusa da gidan ya kirasa, yaron ya taho sudais ya duka yana kallon yaron yace “Big boy… shiga gidan nan kace ana sallama da Hajiya Amina” yaron yace “Toh” sannan ya shige gidan da sauri, ba a dau lkci ba sai ga Shafah da Hasana sun fito ko wacce daga mai riga a kai a matsayin mayafi sai mai wando, Sudais ya dinga kallonsu daga sama har Kasa, Shafa dake ta kallon sudais tace “Sannu da xuwa bawan Allah” yace “Ina kwanan ku” a tare suka amsa masa, ya shafa lallausan gashin kansa da ke kara masa kyau yace “Dama Hajiya Amina nake son gani” a tare suka hade rai Hasana tace “Yar uwar ka ce?” Ya girgixa kai tace “Halan kudi xaka karba gunta? Toh Allah sa dai ba yawa, don kuwa Amina xamanta ya xo karshe gidan nan tun shekaranjiya don kuwa Alhaji ya saketa, yanxu haka ko tsinkenta babu a gidan” Kallonsu Sudais yake a sanyaye, Hasana tace “Atoh, ban da mugunta ki tura yar mutane karuwanci don ba ke kika haifeta ba yarinya marainiya bata da kowa duniyar nan banda Allah, dama an ce idan mutum xai gina ramin mugunta yyi ta yar karama…. To ita kam da xurfi tayi sa gashi ta afka ciki” Sudais da ko kadan bai san ma abinda suke cewa ba yyi karfin halin cewa “Toh don Allah kun san garinsu?” Shafah tace “Halan kudin da yawa, matar da har gorin cin bashi take mana ashe a boye take nata” Hasana tace “Mun dai ji kishin kishin a gari ta siyar da duk kayan dakin nata wai xata koma kasarsu, ka san 6are ce ba yar Nigeria ba” Sudais yace “Ina ne kasar ta su?” Shafah tace “Wai ko Ethiopia ko morocco ko Sudan oho dai… amma nan Africa ne, mu dai Allah ya raba mijinmu da alakakai” juyawa sudais yyi ransa a dagule ya nufi motarsa yana shiga ya hade kai da steering yana tunanin ta ina xai fara, ya xai yi da yarinyar nan da kowa ke kira da marainiya, khadijah da ke ta kuka tun bayan fitarsa cikin rawar murya tace “Ummata na fushi da ni har yanxu koh?” Dago kansa yyi yana kallonta da idanuwansa da suka sauya kala.