Har Khadijah ta isa bakin titi kuka take bata damu da mutanen dake kallonta ba, ta ma rasa inda xata bi gashi ko sisi bata da shi, all this while Sudais na cikin motarsa yyi parking motarsa ya dinga bin ta da kallo har ta d'an yi nisa, ya jinginar da kansa da kujera ya lumshe ido yana kiran Allah a xuciyarsa, he is just confuse, a hankali ya ci gaba ya fara driving motar har ya iso dai dai inda take ya tsaya ya wani hade rai cikin tsawa yace "Ina kika san xaki tafi yanxu?" Ta juyo a tsorace tana kallonsa ta tsaya bata ce komai ba, yace "Shigo mu je" fuska daure yyi maganan, A sanyaye ta xaga ta bude motar tana kallonsa ta shiga, bai ko kalleta ba ya ja motar, har ya isa gidansa bai ce mata komai ba, ita ko tayi nisa cikin tunanin da take ya bude motar ya fita ta bi sa da ido, Juyowa yyi ganin bata fito ba Yace "Should I bring u down?" girgixa kai tayi ta fito ya kulle motar ya nufi entrance din gidan ta bi bayansa, kana ganin yanda yake tafiya kasan a gajiye yake, xaune ta gansa parlor ya jinginar da kansa jikin kujera bayan ya xauna ya lumshe ido, a hankali ta xauna kasa ta takure waje daya sbda sanyin parlon, bude ido yyi bayan wani lokaci ya kalleta, suna hada ido ya dauke kai, khadijah dai sai kallonsa take, yanda ya tsura ma ac dake aiki a parlon ido yasa xaka gane tunani yake, a hankali khadijah tace "Xan yi wanka..." sai a snn ya juya ya kalleta, a takaice yace "In kai ki bayin kenan?" Ta girgixa masa kai, yace "Toh tashi ki tafi" mikewa tayi ta wuce dakin da ya saukar da ita, wanka tayi ta fito ta shirya ta sa Hijab, yana nan yanda ta bar sa, har ta iso kusa da shi kuma bai sani ba, duk jikinta yyi sanyi ta durkusa nan kusa da shi cikin sanyin murya tace "I knw I am a burden, u don't knw where to start from, and u don't want to send me away cos you've got a good heart... You look so responsible to keep me in ur home, you have parent and elders that won't take it likely.... I don't want to be d beginning of ur problems, sbda haka nake rokon ka don Allah ka taimakeni ka kai ni gidan marayu kamar yanda na roka a baya, I will cope there in sha Allah, I will take care of the motherless there, but I want u to do me the favour of coming to see me, even if it's just once in a year plss, I want to feel I have somebody in this world, don Allah kar ka mance ni bani da kowa" tana kai wa nan hawayen dake makale idonta ya sakko, kallonta kawai sudais yake, can ya runtse ido ya bude ya mike ya fice parlorn, hade kai tayi da gwiwowinta tana kuka a hankali tana me tausayin rayuwarta, sai bayan kusan minti talatin sudais ya dawo parlorn, duk da ta ji shigowarsa bata dago kanta ba, muryarsa taji yace "tashi ki shiga daki kiyi kukan da kyau" ba musu ta tashi ta wuce cikin dakin, tayi kukan kamar yanda yace mata har ta gaji ta kwanta ta takure waje daya, bude kofar dakin yyi ya shigo, ta daga kai tana kallon sa har ya iso inda take yana tsaye yace "Good, am hoping all the tears you where planning to shed while in this house kin yi su yau kin gama, cos I am nt gonna tolerate that, clear? Better ki barni in ji da daya" Mikewa xaune tayi ta gyada masa kai tana share guntun hawayen idonta, yace "Me xa ki ci?" Ta girgixa kai tace "Bana jin yunwa" ganin kallonta yake a hankali tace "Toh xan ci apple" yace "Not apple, I mean food" ta d'an yi shiru, can ta dago tana kallonsa a hankali tace "Wainar flawa" wani kallo yake mata yace "Meye shi?" Taace "Da flour, albasa, tarugu, maggi, gishiri and man gyada ake yin sa, Anty Kyauta tayi mana a can gidan" da mamaki yace "A ina xan samo maki shi?" Tayi shiru bata ce komai ba, ya fi minti biyar a tsaye, can ya tabe baki ya fiddo wayarsa a aljihu yayi dialing number ya kai kunne, ba a dau lkci ba ya amsa sallaman da aka yi masa yace "Rabi'ah am on my way now, pls ina son ki min...." Juya ido yyi kamar me son tuno sunan abun, can ya cire wayar a kunne da sauri ya jefa ma khadijah wani kallo yace "Meye sunan ma?" A hankali tace "Wainar flawa" ya mayar da wayar kunne yace "Wainar flawa" Khadijah na jin yarinyar na dariya ya tabe baki ya katse wayarsa ya mayar aljihu ya fice a dakin. Khadijah na nan yanda ya bar ta ya dawo dakin, yana kallonta yace "ermm, ohk let me say Amira, you see xan je gida yanxu, but baxan dade ba xan kawo maki abincin, xa ki iya tsayawa ke kadai ai koh?" Ta gyada masa kai yace "Good, I will be right back now" kashe ac din dakin yyi ya kunna mata kayan kallo daga haka ya nufi kofa khadijah tace "Allah ya tsare" juyowa yyi ya kalleta yace "Amin" daga haka ya fita ya kulle mata kofar. Kwanciya tayi duk da sonta da kallo ta rufe idonta. Tun da sudais ya shiga gidansu yyi parking gabansa ke faduwa ya bude motar a hankali ya fita ya wuce cikin gidan, jin ana soye soye a kitchen ya karasa kitchen din, Rabi'ah ce tsaye tana soya wani abu da bai taba gani ba yace "What's this" wara ido tayi ganinsa tace "Sannu da xuwa yaya, wainar da kace mana" yace "Dama kamar kwai yake?" Ta gyada masa kai tana yar dariya ya tabe baki yace "Mami fa?" Tace "Tana bedroom da su Anty Maryam" bai ce komai ba ya haura sama yyi sallama kofar dakin maminsa, Kanwar mami da kanninsa biyu dake Dakin ne suka amsa masa ya shiga ciki, kallon uban kayan dake jibge a kasa ta ko ina a dakin, ga boxes masu tsada dake ajiye su ma, dukawa yyi ya gaida mami ta amsa da fara'a tana masa tambayar ya hanya, yace "Alhmdllh" sannan ya gaida Anty Maryam ta amsa da murmushi tace "Welcome barrister" sai a sannan ya amsa gaisuwar kanninsa ya mike ya koma can karshen gado ya xauna, Mami tace "Ka ga sai yau Maryam ta karbo sauran akwatunan xa a xuba kayan ciki yanxu" a hankali yace "Ohk" Mami tace "ka gama gyaran da kace a can gidan naka" ya gyada kai yace "Eh Mami" Mami tace "Toh maa sha Allah" Yana ta xaune har suka gama jera gaba daya kayayyakin a akwatunan, kanninsa su Humairah suka fita dakin ya rage daga shi sai Mami da kanwarta, Mami tace "Lkci na ta tafiya sudais yaushe ka ga ya kamata a kai kayan" tasowa yyi a hankali ya dawo kasan carpet ya xauna kansa a kasa murya can kasa yace "Mami..." Mami dake ta kallonsa kamar yanda Anty Maryam ma ke kallonsa tace "Ya aka yi sudais?" Kasa dago kansa yyi yace "Mami ina son a dakatar da kai kayan nan yanxu ne...." Mami dake masa kallon mamaki tace "Ko saboda me Aliyu?" Ya girgixa kai yace "Mami a dai dakata kawai" Anty Maryam tace "Ko Jiddahr ta yi maka wani laifin ne sudais?" Shiru yyi bai ce komai ba, Mami tace "Toh ni dai abinda xan ce maka a nan shine idan dai kasan ba shiririta bane, ba wani concrete laifi bane ka ajiye wannan shashancin da kake fadi aside, idan kuma kaga laifi ne babba to shkkn" Anty Maryam tace "Ka fada mana me tayi, wani laifin ka kama ta da shi Sudais, Kar mu xama kananun mutane" ya girgixa kai a hankali yace "A bar xancen kawai mumy" Mami tace "Toh Allah rufa asiri" yace "Ameen" mikewa yyi yace "Xan fita in dawo yanxu Mami" daga haka ya nufi kofa Mami ta bi sa da ido har ya fita, Anty Maryam tace "Kar ki tilastata masa don Allah Mami tun da kika ga haka ba karamin laifin ya kamata da shi ba, kin dai san halin sudais da xurfin ciki ko xaki shekara kina tambaya ba fada xai yi ba" Mami dai bata ce komai ba. Sudais na fita ya shiga kitchen ya tarar Rabi'ah ta gama wainar ta xuba masa a warmer, ya bude warmer din yana ta kallon abincin kafin ya tabe baki ya dauka ya fito parlor, da mamaki tace "Yaya ba a nan xaka ci ba?" Yace "Ehh ni da frnds dina xa mu ci, sai na dawo" daga haka ya fita gidan ya hau motarsa ya wuce. Sai da Sudais yyi azahar a masallacin layin gidansa sannan ya shiga gidan misalin karfe daya da rabi, jin an bude kofa Khadijah dake bacci ta bude ido da sauri, karasowa yyi yana kallonta ya ajiye warmer din hannunsa yace "Tashi ga abincin" ta xauna ya bude mata warmer din, ba don tsare ta da yyi ba da daya ma baxata cinye ba amma haka ya dinga forcing dinta har ta cinye biyu, sai dai duk she was restless don amai kawai ta dinga ji, ya hade rai sosai yace "Look idan ki ka yi aman nn I will nt bother my self about ur food again am telling you" hawaye cike idonta tace "Kayi hakuri wllh ba ni bace" ya xauna gefen gadon yace "Toh nayi, amma ki daure kar ki yi.... Just try" ta gyada kai ta koma xata kwanta ya ce "Toh ai hakan xai sa ki yi aman" dagowa tayi da sauri ta xauna, toshe baki tayi tana girgixa kai, ya wani hade rai kamar bai taba dariya ba yana kallonta, a hankali tace "Wllh amai xan yi kayi hakuri" daga haka ta mike ya fixgota har sai da ta kusa fadawa kansa, yace "Am serious baxa ki yi ba" bai rufe baki ba ta kwarara masa aman gaba daya a jikinsa da bedsheet, wani kallo ya dinga mata yana yamutse fuska, can ya runtse ido har ta gama aman, Khadijah ta kasa kallonsa sae sauke numfashi take, wani tsaki da bata taba jin irinsa ba ya ja a fusace ya mike ya shige toilet, hawaye ya dinga sakko mata a sanyaye ta hade kai da gado, bayan kusan minti goma ya fito, ita dai tana nn yanda take, taji ya dafa ta ta dago da sauri, singlet da 3qtre ne jikinsa, ya sauke idonsa yace "kije kiyi wanka na sa maki ruwa" ta girgixa masa kai tace "Baxan iya ba ynxu" yace "No ki daure" daga hka ya sa ta tashi ta wuce bayin, Tana fitowa taga har ya shimfida wani bedsheet din ya cire na da, ta kwanta tana rawan sanyi, ya shiga bayi da xanin gadon, bai fito ba sai da ya wanke da shirt dinsa ya fita dakin. Daga wannan rana Khadijah ta fara laulayi me tsanani kamar baxa ta yi ba, tausayinta Sudais yake har ransa, duk ta rame ba kadan ba ga yawan complain din ciwon kirji da take, idan aka ga yanda sudais ya damu sai a rantse ya taba sanin Khadijah, hakan bai hanasa trying best dinsa gun ganin Maminsa bata d'ago komai a rashin dawowa gida da baya yi da wuri da fitan da yake yi da sassafe ba, yawanci duk khadijah ke cinye masa time dinsa, ya kai ya kawo sai ya fi kwana biyu bai karbi case ba tunda he is always by her side kwana ne kadai bai yi gidan nasa, karfe sha daya idan tayi bacci yake barin gidan ana idar da sllhn asuba kuma kafin ya shiga gida sai ya taho gidansa dubata yaga ya ta tashi, Dr Yusuf ke xuwa bata medication kusan kullum da safe da yamma tun daga allura xuwa drugs duk da biyansa Sudais yake, A haka har Khadijah ta cika sati biyu ciff a gidan. Da safe misalin karfe sha daya Sudais yaje can clinic gun Yusuf, bayan sun gaisa Yusuf ya tambayesa jikin khadijah, ya shafa kai yace "Toh ga ta can dai, am just tired Yusuf, wai why not baxa ka taimaka ka cire mata cikin nan ba frnd, am talking to you about this for the 3rd time don Allah ka cire mata ko nawa ka bukata xan baka, plss Yusuf" Yusuf ya girgixa kai yace "My reply will always be the same, I don't abort pregnancies and I will not, nace ka kai ta wani asibitin ni dai baxan yi ba ka ki ganewa" Sudais ya marairaice yace "Nasan baka cire ciki amma ita wannan case dinta daban ne, she was raped... beside she is too young da ciki dubi fa yarinya ce karama, gashi sai wahala take sha ko don haka ka tausaya mata mana Yusuf" Yusuf dake rubuce rubucensa yace "Ae sai kuma ka yi Barrister" Sudais ya d'an hade rai yace "Haba Dr, ya kke son marainiyar tayi da yaron da xata haifa yanxu, ta ina xata fara rainonsa don ni dai ba dauwama xata yi tare da ni ba na har abada, har ynxu ina tunanin taimakon da xan bata ta tafi ta inganta rayuwarta but nt when she is this sick everyday, dubi fa jiddah gani take kamar na yaudareta ne, but ba hka bane idan aka yi auren ina xan sa ta, kasan it won't make sense ina da gida in kama haya, dole Mami xata so sanin dalili, infact she will be suspicious, Yusuf don girman Allah ka rufa min asiri ka cire mata jaraban nn ta kama gabanta plsss" Yusuf ya tabe baki yace "xa ma ka gama dadin bakin ka" jin Sudais yyi shiru yana kallonsa ya ajiye pen din hannunsa yace "Sae in har in rubuta maka kaje can pharmacy ka siya nasan baxa ka rasa iya allura ba, duk sai kayi mata da kanka" ban da hararansa babu abinda Sudais yake, Yusuf yace "yes, or you buy her just drugs shkkn amma ni dai ba da hannu na ba" Sudais ya dake trying hard to hide his anger yace "Rubuta min" Takarda Yusuf ya jawo yyi rubuce rubucensa ya mika masa Sudais ya fixge ya nufi kofa Yusuf ya bi sa da kallo yana murmushi, Gida ya nufa bayan ya je garage din mota amso sakon Mami da ta aikesa tun safe, Xaune ya same Mami parlor, tun da ya shigo take kallonsa ganin ramar da yyi har ya karaso ya xauna kasa kusa da ita yace "Ina yini Mami" tace "Lafiya lau, sannu da xuwa" ajiye mata ledan hannunsa yyi yace "Ga sakon Mami" Bata ce komai ba ganin haka ya daga kai yana kallonta, tace "Aliyu ni ban fa gane nufin ka ba kayan akwatunan da kasa nayi jere da shi a daki ka hana a kai, toh Abbanku ya sa in xaunar da kai ka sanar da ni ko fasa auren kayi, wannan ai iskanci ne da kokarin mayar da mu kananun mutane da kake, idan ma da matsala ne ai sai ka yi mana bayani, babu mai maka dole tun da kai ka kawo yarinyar nan kana so ba wani ya kawo maka ita ba, yanxu ni ka gaya min ma'anar cewa da kayi kar a kai kayan a dakata" Sudais da har xufa ya fara keto masa ya shafa kai da kyar yace "Mami ba wai na fasa bane, kawai dai akwai matsala... ina son a min alfarmar ce masu su d'aga ko xuwa sabon shekara da xa mu shiga, idan kuma sun ga baxa su iya dagawa ba to gaskiya na hakura, Allah bata wanda ya fi alkhairi a kai na" Mami dake masa wani kallo tace "A daga a kan wani dalili?" Ya kasa dago kai yace "Kiyi hakuri Mami ayi min yanda nace pls, I just want to figure out the problem, Mami kin fa san aure ba don kwana daya ko 'yan watanni ake yin sa ba na har abada ne, Mami I don't want to make marriage mistake in my life don ni bani da burin xama da mace fiye da daya so I want to have the best marriage, ku taimaka ku ce masu a daga har lkcn, idan sun ga yyi masu tsayi to na hakura gaskiya I don't want to cheat my self" Mami tace "Toh shi kenan, Allah sa mu dace, xan yi ma Abban naku bayani" Sudais ya dan yi murmushi a hankali yace "Nagode Mamina, xan je in dawo yanxu" Mami na kallonsa da kyau tace "Wllh ban gane fitar nan da kake kamar me talla ba kwanan nan sudais, da sassafe ka fice baka dawowa sai kusan sha daya, what's wrong with you?" Ya dago yana kallonta a hankali yace "Mami wani case ne ya shige min duhu, so ina bincike ne shi yasa kika ga haka" kallonsa kawai take can ta tabe baki tace "Though I knw when you are saying the truth and when u are lying, and duk da nasan karya kake coz I saw it in ur eyes, ni kam sai dai ince Allah tayi jagora, ya kuma yaye maka abinda ke damun ka, wnn ramar kuma da kayi, kayi kkrin ganin cire ko ma ke damun ka plss, it's better you pray to ur God" Sudais ya dauke kansa daga kallonta da yake ya mike a hankali yace "Toh nagode Mami sai na dawo" tace "Allah ya tsare" daga haka ya fita. Pharmacy ya tsaya ya siya magungunan da Yusuf yyi masa prescribing sannan ya siya fruits kafin ya wuce gidansa, har wani faduwa gabansa ya shiga yi bayan yyi parking cos bai son xuwa ya ga khadijah in pain, ya dai dake ya shiga gidan, kwance ya sameta kamar ko da yaushe a daki idonta a rufe, yawanci duk haka yake xuwa ya sameta kuma ba bacci take ba, yana tsaye a hankali yace "Amira" ta bude idanuwanta a hankali tana kallonsa, yace "Ya jikin" kai ta gyada masa ya durkusa yana bude ledan apples da banana da ya siyo mata yace "Ga Apple nan" ta girgixa kai da sauri tace "Anjima" yace "Toh kin yi sllh?" Gyada masa kai tayi, ya d'an yi shiru sai kuma ya mike yace "Toh tashi ga magani na kawo maki ki sha, you feel more better idan kin sha" kamar xata yi kuka tace "Xan yi amai ni nafi son allura" kallonta ya tsaya yi, can yace "Baxa ki yi ba kawai guda uku ne fa" daga haka ya fiddo magungunan a leda sai kuma ya fita xuwa ya debo mata ruwa, har ya dawo tana kwance ya d'an hade rai yace "Toh tashi mana" mikewa tayi da kyar ya bude maganin gudu uku kamar yanda yace ya bata a hannu ya mika mata ruwa a cup, ta karba tana bata fuska xata yi kuka, ya daure fuska yace "Ki sha Ki ban cup yanxun nan" wayarsa ne ya fara ring ya ciro a aljihu tana ganin haka ta watsa maganin a bayanta tayi saurin kai ruwan baki tana sha dai dai lkcn da ya maido dubansa kanta, da sauri yace "Kin sha?" Ta mika masa cup din tana yamutse fuska, ajiyar xuciya ya sauke a hankali, kokarin amai ta shiga yi da sauri yace "Noooo, don't ko in bata maki rai" ta koma baya a hankali kar ya xagayo ya ga maganin ta jingina da gado yace "Good girl" daga haka ya fita ya kira Yusuf dake kiransa, da sauri ta kwashe magungunan ta watsar a bayan gado tana turo baki, Sudais ya hade rai bayan ya kai wayar kunne yace "Ya aka yi?" Yusuf yace "Ya ta sha?" Sudais yace "It's nt ur concern" dariya Yusuf yyi yace "In dai ka tabbatar ta sha don't leave her alone kar ka kashe yar mutane nan da few hours xata samu miscarriage din in dai magungunan da na rubuta ka siya ka bata" Sudais yace "Ohk" daga haka ya katse wayar ya xauna parlor. Haka Sudais yyi ta xama gidan har magrib amma shiru kke ji, ya duba ta yyi sau ashirin kafin magrib amma banda bacci bbu abinda take hankli kwance, yana fitowa masallaci ya kira Yusuf yace "Kai ni da ina ta xaune gidan har yanxu shiru" Yusuf yace "Bata sha ba toh" Sudais yace "Ya xaka ce haka, a gabana fa ta sha ni ma na bata maganin da ruwa" Yusuf yyi shiru jin haka, sudais yyi tsaki ya katse wayar. har washegari shiru kake ji bbu alamar miscarriage gashi Yusuf yace kar ya kara bata wani, duk ran sudais ya baci, da yammacin washegari Yusuf ya xo gidan, Magungunan ya dauka yana ta kallonsu kamar yanda Sudais ke hararansa shi kuma, can ya balli wasu ya mika ma sudais yace "Bata ta sha" Khadijah dake kwance tana kallonsu kamar xata yi kuka tace "Ni maganin wani iri yake min bana so plss" Sudais ya daure fuska yace "Karba my friend" mikewa tayi hawaye ya cika idonta ta amshi maganin ya mika mata ruwa, daga shi har Yusuf suka kafeta da ido, ta daga gefen Hijab din jikinta tana share hawayen idonta hakan ya bata daman sakin maganin gaba daya a Hijab din cikin dubara sai kuma tayi saurin dage kafarta kamar xata daura kanta bisa kneel dinta, har lkcn kuma hannunta na dunkule kamar tana rike da drugs din, Yusuf yace "Baxa ki sha ba?" Bude baki tayi ta yi kamar ta watsa su ciki sannan tayi saurin xuba ruwa bakin ta tana yamutse fuska har da kokarin amai, da sauri Sudais yace "Don't try that" ta hade kai da gwiwa suna ta tsaye suna kallonta har ta dago a hankali, Yusuf ya juya ya fita sudais ya bi bayansa, Yusuf yace "Toh sai kayi xaman gadi" daga haka ya bar gidan, Sudais na ta xaune har dare amma shiru, mamaki ya dinga yi anya ba yaudararsa Yusuf yyi ba, a fusace yaje har gida ya samesa don jin me yasa yyi masa haka, Yusuf dake dakinsa kwance yace "Toh ka kai ma wani likitan takardar maganin ka tambayesa na menene, I think that's all I can tell you" Bayan kwana biyu sudais ya sake komawa Yusuf office da rana, da damuwa yace "Dr ko xaka canxa wani method din ne, wllh I don't have rest of mind, am afraid kar Mami ta san abinda nake yi, gashi in few weeks time xan je UK, to ya xan yi da yar mutane?" Yusuf yayi dariya yace "Tunda taimakonta kake son yi ka tafi da ita mana" Yusuf ya watsa masa kallo yace "Ko matata ce ke wannan laulayin ina xa ni da ita balle wannan" Yusuf yace "In baka shawara Barrister?" Sudais yyi shiru yana kallonsa, Yusuf ya mike tsaye yace "Wllh ka kyale mata cikinta tunda ka ga haka, Allah kadai yasan me xata haifa, there is power in the baby, banda haka ban ga dalilin da xai sa ta sha drugs din nan har sau biyu ba amma shiru ake ji, just let her pls and idan son samu ne ka taho da ita clinic ko gobe da safe ayi mata scan cos this is almost a miracle" kasa cewa komai Sudais yyi can ya juya ya fita. Washegari kamar yarda Yusuf yace haka Sudais ya sa khadijah ta shirya suka je asibiti don a mata scan, gaba daya jikinsa yyi mugun sanyi bayan result ya fito, shi kadai da Yusuf ne a office din Yusuf din, ita kuma tana reception, Yusuf yace "You see, da haka xaka sa ayi wasting bayin Allahn da basu san komai ba, 2 souls barrister" Sudais bai iya yace komai ba. A hakan dai Sudais ya ci gaba da ba Khadijah kulawa yanda ya kamata, bai rage ta da komai ba a gidan sa, damuwarsa daya yanda ta ki kwantar da hankali har lkcn ga yawan koke koke, idan ya sa ta gaba ta fadi me ke sa ta kuka sai ta ce masa ita bata da kowa yanxu, hakan nasa jikinsa yyi sanyi, sannan hakan ke kara masa kwarin gwiwan ci gaba da taimaka mata, ganin saura yan kwanaki ya fita kasar ya sa ya shiga tunanin wanda xai bar ta da a gidan, idea ne ya xo masa yasa aka nema masa wata dattijuwar da xa su xauna tare da Khadijah a gidan nasa, hakan aka yi bayan matar da baxata haura shekaru hamsin ba ta amince duk wata xai dinga bata dubu arba'in. A yau Khadijah na daki xaune kasan carpet tana shan kunun da dattijuwar da ta dama mata, dattijuwar matar da a ranan tayi kwana uku a gidan duk tunaninta Khadijah matar Sudais ce, su biyu ne dakin Sudais yayi sallama bakin kofa, ta mike da sauri ta iso kofa ta bude tana cewa "Sannu da xuwa yallabai" Gaisheta yyi ta amsa cike da jin dadin yanda yake girmamata sannan ta fita, Sudais ya karasa cikin dakin yana kallon khadijah, wani mugun haske tayi da kyau sai kyalli take, lips dinta yyi pink colour, dauke kai yyi ya isa gefen gado ya xauna, a hankali tace "Ina yini?" Yace "Lafiya lau, ya jiki?" Tace "Da sauki" shiru yyi na wasu yan mintuna kafin yace "Am traveling Amira" ta dago tana kallonsa, ya gyada kai yace "Yeah, gobe xan tafi" sauke idonta kasa tayi, lkci daya hawaye ya kawo idonta cikin sanyin murya tace "Tafiya xaka yi ba bar ni" ya tsura mata ido kafin yyi murmushi yace "Aiki xan tafi yi can, in sha Allah xan dawo when am done" ta kallesa hawayen idonta ya sakko tace "Toh yaushe ne xaka gama" ya wara Manyan idonsa yace "Nima ban sani ba, but da na gama xan dawo ai" kai kawai ta gyada masa amma kana ganinta kasan jikinta yyi sanyi, murmushi ya sake yi yace "Ba ga mama ba xata dinga kula da ke xan bar mata kudi ta dinga siya maki duk abinda kike so, just promise me baxa ki dinga damuwa ba that's all" murya can kasa tace "I promise, amma yaushe xaka dawo?" Dariya ta basa ganin ta yi tambayar daxu yace "Duk sanda kika samu lafiya kika fara cin abinci sosai sannan bakya damuwa xan dawo" xaro ido tayi tana kallonsa, yace "Yes" murmushi tayi ta sunkuyar da kanta, sae ranan ya fara ganin murmushinta ya dinga kallonta ganin xata dago kanta yyi saurin dauke kai, tana wasa da dogayen yatsun ta tace "Toh naji" yace "Yauwa ko ke fa" wayarsa daya ya Ciro ya mika mata yace "Xan dinga kiran ki in sha Allah" karba tayi a hankali tace "Toh" yace "to tashi ki raka ni" Ba musu ta mike shi ma ya tashi ya nufi kofa sannan ta bi bayansa, a parlor ya tsaya yyi sallama da Dattijuwar ya kuma sanar da ita xai yi tafiya ta dinga masa addu'ar Allah ya tsare yace "Ameen Ngd mama, don Allah ki dinga sa mata ido bata son cin abinci" tace "In sha Allah kar ka samu damuwa" Dubu hamsin ya ba matar ta dinga siya ma khadijah duk abinda ta bukata, ya kuma sanar da ita komai babu gidan Dr Yusuf xai kawo masu, daga haka ya juya yana kallon khadijah dake ta kokarin ganin bata yi kuka ba yace "Toh mu je" har bakin mota ta rakasa kanta a kasa ya kara mata sallama ta kasa daurewa ta fara kuka, duk jikinsa yyi sanyi, a hankali yace "Look Amira ba dadewa xan yi xan dawo ba, ki daina kuka pls" kai ta gyada masa cikin sanyin murya tace "Toh Allah ya tsare hanya" daga haka ta juya ta koma cikin gida ya bi ta da ido. Kamar kar Sudais ya bar kasar Khadijah ta fara samun lafiya sosai dattijuwar me kirki komai take so shi take mata kafin wani lkci duk babu ramar da tayi sai cikinta da ya fara fitowa, kullum a rana sudais xai kirata kusan sau biyar just to check if she is fine, idan bai kirata ba kuwa ta dinga damuwa kenan, a haka har watanni suka shude. 5 months later. Yau tun da Khadijah ta tashi take ta murna ta rasa dalili, har hirarta ya fi na ko wani rana yawa har da dariyarta wanda da wuya ka ga tayi dariya, Dattijuwar mama suwaiba da take kira da Anty har ta lura da hakan tace "Wannan murnar yayi yawa khadijah ko dai mai gidan ne xai dawo yau" Khadijah dake hada fruits salad xata sha ta daga kai tana kallon mama suwaiba tayi shiru don kuwa gaskiya ne jiya da daddare da suka yi waya da Sudais yace mata yau xai dawo, murmushi tayi ta sunkuyar da kanta ta ci gaba da abinda take a hankali, mama suwaiba tace "Toh gwara a tashi a san me xa a girka masa, ki fadi duk abinda kika San yafi so sai in shirya in tafi kasuwa yanxu" Khadijah tayi shiru don har lkcn bata san komai game da Sudais ba balle ta san abinda ya fi so da wanda bai so, hakan yasa jikinta yyi sanyi sosai. A cikin watanni biyar din nan khadijah ta warware jikinta yyi kwari, babu abinda bata ci har da wanda bata ci a da can, wato wake, taliya kai har da tuwo da miyar kuka, wani kyau na musamman tayi don hatta fatar jikinta har wani glittering yake yayi taushi, yanxu kam cikinta ya fito sosai don sai ayi tunanin at anytime xata iya haihuwa don da kyar take yin komai nan ko watannin cikin bakwai, tausayi take ba mama suwaiba ganin yarinya ce sosai wa ya sani ko xata iya haihuwa da kanta ma, hakan yasa in dai ta fita cefane ko siyo wani abun bata rabo da dawowa da magunguna irin na gargajiya da tasan mai ciki na bukata, duk ranakun alhamis kuma tare da mama suwaiba suke xuwa can clinic dinsu Yusuf domin Antenatal a bisa umarnin sudais, damuwar Khadijah daya a lkcn ummarta don ko cikin dake jikinta baya damunta ta kuma rasa dalili, gaba daya tayi kokarin ganin ta mance ta taba rayuwa gidansu Aliyu, amma duk sanda cikinta yayi motsi sai ta tuna shi Aliyun, duk wannan difficulties na rayuwa da ta shiga ko sau daya bata taba jin haushin Aliyu ba kuma har ranta take jin ta yafe masa a lkcn... ko don tana tare da yarinta har sannan ne oho. Khadijah ta kasa hakuri ganin har yamma bata ga sudais ba alhalin yace mata in sha Allah yau yana Nigerian duk jikinta yayi sanyi ta tafi daki ta kwanta, Mama suwaiba kuma ta ki hakura tana ta girke girke a kitchen ita kadai. Sudais na sauka taxin da ya kawo sa har kofar gida ya shiga gidan yana rike da daya daga travelling bag dinsa guda uku da mai taxin ya dire masa a bakin gate, kai kana ganinsa kasan daga turai yake don wani fresh na musamman yyi da haske sai dai ya rame sai idanuwa da hancinsa da suka fito, sosai ya rage bak'in gashin kansa, yyi murmushi ya na amsa gaisuwar da mai gadi ke masa da fara'a yana masa sannu da dawowa sannan yace "Ka shigo min da sauran kayana bilyamin" tun a bakin kofa kanninsa suka rungumesa ko wacce na murnar dawowarsa bayan kusan watanni biyar, Mami dake parlor da Anty Maryam ma sai murmushi suke, lkci daya murmushin Sudais yyi fading ganin Jiddah da yayi xaune parlorn, ya karaso a sanyaye ya duka kasa ya gaida mami ta amsa tana murmushi tace "Sannu da xuwa Aliyu ya hanya?" Yace "Alhmdllh Mami, fatan mun same ku lafiya?" Tace "Alhmdllh" gaisawa suka yi da Anty Maryam sannan ya kalli jiddah yana kirkiran murmushi ta sunkuyar da kai tace "Sannu da xuwa ya hanya?" Yace "Alhmdllh mun same ku lafiya?" Tace "Sure" Rabi'ah da Humairah suka dau bags dinsa xa su kai daki yace "Noo don't worry sisters wancan kadai xaku dauka ku bar wa ennan, xan d'an fita yanxu" da mamaki Mami tace "Ka fita kaje ina daga dawowa, idan ma fitan xaka yi ina xaka da jaka kuma?" Ya sunkuyar da kai yace "Sakon wani abokina ne xan kai gidansu Mami" Mami tace "Ohk, to amma sai ka huta ka ci abinci koh?" D'an shiru yyi sai kuma yace "Mami baxan dade ba xan dawo yanxu" daga haka yasa kanninsa suka dau jakunkunan suka kai masa bakin motarsa sanin ko baya nan ana amfani da motar, ya mike yace "Toh sai na dawo Mami" tace "Toh don Allah kar ka jima ka dawo ka ci abinci ka huta" yace "In sha Allah" yana barin gidan bayan ya hau titi ya dau wayarsa ya shiga kiran khadijah, Khadijah dake kwance har lkcn a daki ta mike da sauri kamar jira take jin ring din wayar ta jawo ganin Sudais ne ta daga ta kai kunne, daga daya bangaren yyi sallama yace "Amira" turo baki tayi tace "Uhn" yace "How are you" a hankali tace "Fine baka dawo ba kuma" d'an murmushi yyi yace "I postponed the trip xuwa next month in sha Allah" wani irin faduwa gabanta yyi da har sai da ta ji a kirjinta da ya mata sauki kwana biyu sbda magungunan da Yusuf ke bata, hawaye ne ya shiga sakkowa idonta, yace "Hello are you there?" Kasa amsawa tayi ya dinga hello ta katse wayar ta hade kai da gado ta fara rera kuka, sake kiranta yyi ta ki dauka har ya katse ya kara kira, sai a snn ta dauka ta kai kunne taki cewa komai, murya can kasa yace "Amira" ta fashe masa da kuka a hankali, wara ido yyi hade da murmushi yace "Har da kuka kuma?" Ta ki cewa komai, murya can kasa yace "Cry no more, tunda kina son ganina kawai fito gate ki tsaya ni kuma xan taso daga UK yanxu, har kofar gida jirgin xai ajiye ni" mikewa tayi xaune da sauri tace "Don Allah ka bari, ka dawo pls?" yace "Da gaske fa just wait me outside xa ki ganni yanxun nan" katse wayar tayi ta tashi da sauri ta dau Hijab har Kasa ta sa sannan ta fita dakin, Ganin xata fita waje Mama suwaiba da fitowarta kitchen kenan tace "Ya iso halan" Khadijah bata iya ta ce komai ba ta kirkiri murmushi ta fita, a hankali take tafiyar har ta isa gate ta tsaya gabanta na bugawa, tsaye ta ga motarsa bakin gate din suna hada ido ya bude motar ya fito yana murmushi, tsabar farin ciki ta kasa cewa komai amma kana ganin ta kasan she is just happy, ita dai tasan yau da ace mace ce Sudais da ta tafi da gudu ta rungumesa, ya wara mata ido ganin kallon da take masa yace "Toh ko dai in koma tunda kallona xa ki tsaya yi" tahowa tayi ta tsaya gabansa ta sunkuyar da kai tana murmushi, murmushin yayi shi ma murya can kasa yace "How are you Amira" ta kasa dago kai cikin sanyin murya tace "Am fyn, sannu da dawowa" yace "Sannu, ya babies dinmu" dagowa tayi ta kallesa da sauri sai kuma ta juya masa baya, dariya yayi yana kallonta, tayi murmushi tana jan hannunta, yace "Toh mu shiga" tafiya ta fara yi ya bi bayanta bayan ya rufe motar har suka shigo parlor. Xaunawa yayi parlorn suna gaisawa da mama suwaiba dake tayi masa sannu da xuwa, khadijah ma ta xauna kasan parlorn tana kallonsa ko kiftawa bbu, mama suwaiba ta koma kitchen ya maida dubansa kan Khadijah, sauke idonta tayi kasa da sauri, yace "Are you now happy" murmushi tayi tana gyada kai a hankali shi ma yyi murmushin yana kallonta, Kirar ta Mama Suwaiba tayi ta mike ta nufi kitchen ya bi ta da ido, Mama suwaiba tace "Toh ke haka ake yi, sai ki je bayi ki hada masa ruwan wanka, idan kuma abinci xai fara ci sai ki kai masa daki" murmushi khadijah tayi bata ce komai ba, mama suwaiba tace "Toh kin yi shiru kuma" a hankali khadijah tace "Toh bari in tambayesa" daga haka ta juya ta koma parlor, Wayarsa yake dannawa ta duka gefensa ya kalleta yace "Xauna kujera mana, you are stressing ur self and the babies" sauke idonta tayi kasa tace "Dama Anty ce ta ce in tambayeka ko xaka ci abinci a kai maka daki" shiru yyi na wani lkci kafin yace "She is thinking something different, and Mamina ta min abinci a can gida but... Ohk toh kai abincin daki" Tashi Khadijah tayi ta koma kitchen ta karbi abincin da Mama suwaiba ta hada a tray ta wuce can bedroom da shi, Sudais ya mike ya bi bayanta, karban abincin yyi a hannunta ya ajiye kan rug sannan ya xauna yace "Ke kin ci abincin" tace "Na ci daxu" yace "Daxu daban, yanxu daban, so xauna mu ci" dafa gado tayi xata xauna a kasa yace "No ki xauna saman gado" xaunawa tayi gefen gado ya debi abincin a plate ya sa spoon sannan ya mika mata ta amsa a hankali tace "Nagode" ya debi kadan a wani plate din dai dai nan wayarsa yyi ring dubawa yyi da sauri ya ga Mami ce, ya d'an bude ido sannan ya daga, daga daya bangaren Mami tace "Wai daga dawowa ina ka tafi haka Aliyu? Are you even okay" a hankali yace "Gani nan tahowa Mami am sorry" katse wayarta tayi, ya ajiye wayar yana kallon abincin, samun kansa yyi da Kasa cin abincin, ya rufe yace "Amira xan je gida Mami na jirana idan kin cinye wannan sai ki kara da nawa" Bata ce komai ba sai wasa da cokalin hannunta take, ya mike yace "Kilan xan xo gobe da safe, take care of ur self" daga haka ya juya ya fita, hawaye ne ya cika idonta ta rasa dalili abincin duk ya fita ranta ta kasa ci ta ajiye tana goge hawayen dake xubo mata, Sudais na fita ya tuna bai shiga da kayan da ya taho mata da su daga UK ba, ganin xai kara bata lkci kawai yyi deciding ya bar sa a motar sai gobe idan ya xo. Ko da ya koma gida kawai yana cin abincin da Mami tayi masa ne amma gaba daya hankalinsa na kan Khadijah don bai san ko ta ci abincin da ya debar mata ko bata ci ba, Mami dake xaune ta sa shi gaba da jira har ya gama cin abincin sannan tace "Kun yi waya da jiddah xaka dawo yau ne?" Girgixa kai yyi duk da faduwar da gabansa yyi a hankali yace "Aa mun ma kwana biyu ba mu yi magana ba, fushi take ai da ni" Mami tace "Toh wasa wasa gashi har watanni kusan shidda da kace a daga biki yyi, yanxu kuma ya ake ci" kasa kallonta yayi ya fara kame kamen rufe warmers din abinci, strictly tace "Magana nake ma ka Aliyu" da kyar ya dago ya kalleta yace "Toh Mami a sa bikin nan da wata daya xuwa biyu in sha Allah" wani kallo ta watsa masa tace "Me sati biyu ko uku yayi da har sai an kai wata biyu kuma?" Ya shafa kai yace "Dai dai wannan lkcn xan koma UK kuma xan jima sosai kafin in dawo kinga kawai ana bikin a lkcn sai mu tafi tare da ita" Mami tace "Allah ya kai mu, xan ma Abbanku bayani" yace "Nagode Mami" daga haka ya mike yace mata xai kwanta ya wuce bedroom dinsa. Yana shiga dakinsa khadijah ya kira, tana dagawa yace "Kin gama cin abincin?" Turo baki tayi tace "Na koshi" yace "Baki ci ba kenan?" Shiru tayi bata ce komai ba, yace "Me kike yanxu?" Tace "Na kwanta" yace "Tashi ki je ki dau abincin ki ci idan ba haka ba baxa ki ganni gidan nan ba for plenty days" tashi tayi xaune da sauri tace "Ni ban ce baxan ci ba" yace "Toh je ki ci" ta mike da kyar tace "Toh" yace "Idan kin gama ki kirani" gyada masa kai tayi kamar yana ganinta ya katse wayar. Sosai ta ci abincin ta hada har da wanda ya dibar ma kansa, tana gama ci ta dau wayar ta kirasa, sai da ya kusa katsewa ya daga, jin muryarsa tace "Bacci kake" a hankali yace "Yea, kin gama cin abincin?" Tace "ehh na cinye" yace "Good Mami" murmushi tayi tace "Toh kayi baccin, byee" murmushin shi ma yyi ya katse wayar. Xuwan Yusuf gidansu da daddare ne saving grace dinsa don da shi da fita kuma sai gobe, bayan Yusuf ya gaisa da Mami suka tafi dakin Sudais yana tambayar sa ko yayi ciwo a UK ne don ya rame sosai, bayan kusan minti talatin Yusuf yace xai tafi suka fito tare da sudais da yace ma Mami xai rakasa, sai da suka shiga mota Yusuf yace "Kaje ka duba mai cikin ka?" Sudais ya hade rai yace "Mai cikina kuma" dariya Yusuf yyi yace "Toh ai kusan baka da banbanci da uban yaran, kai ma uba kake a gare su kama fi sa xama masu uba kan ubansu" tsaki Sudais yyi bai ce komai ba, Yusuf yace "But don Allah Sudais da yau ko watarana xaka ga uban unborn babies din nan me xaka masa?" Sudais yyi wani murmushi da kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "I won't even look at him twice yaran da xata haifa sun ishesa" Yusuf yace "What if ya xo wataran yayi claiming yaran fa?" Wani kallo Sudais yyi masa baki bude, can yyi wani dariya yace "Wllh wllh I will sue him, sai na sa yyi shekaru da dama a gidan yari" Yusuf dake driving ya wara ido yace "Tohhh, kenan yaran ka ne ba nasa ba" Yusuf na dariya ya kare maganar, Sudais yyi banxa da shi, Yusuf yace "Toh why not bayan ta haihu ka aureta kawai Sudais" juyawa Sudais yyi yana kallonsa da wani expression, can ya dake yace "Ko saboda me?" Yusuf yyi murmushi yace "Saboda ka ji dadin ci gaba da kula da ita da yaran da xata Haifa kwanan nan, kasan a yanxu kai ne ubanta kai ne uwarta, i mean kai ne gatan ta, don haka sai ka ci gaba da xama gatan nata har karshen rayuwarta, nan da shekaru biyu kai ma ta haifa maka naka yan biyun ba na wani ba" Girgixa kai Sudais yyi bayan ya dauke idonsa daga kallon da yyi ta ma Yusuf yace "I didn't blame you Dr, why?? Because am very sure kafin ka xo gidanmu yanxu daga club din da ka saba xuwa kake, and definitely idan ka je club dole sai ka sha ruwan can na sani, soo no offense, u are drunk...." Dariya kawai Yusuf yake yace "Kai kuma tun bayan haduwarka da marainiyar nan ka daina xuwa can koh? Thank God we where both drunkards before" Sudais da yyi mugun hade rai yace "Drop me here my frnd" Yusuf yyi parking yace "Ji dan iska kamar wani driver din sa wai drop me here my frnd" Bude motar Sudais yyi ya fice ya juya yana masa wani kallo, da yatsarsa yyi masa xagin turawa yayi wucewarsa, dariya kawai Yusuf yake ya ja motarsa ya wuce gida, Da kafa Sudais ya karasa gidansa, Mama suwaiba kadai ce parlor tana cin abinci TV a kunne, tana ganinsa ta mike da sauri tana masa sannu da xuwa yace "A'a yi xaman ki mama" Mama suwaiba ta koma ta xauna tace "Toh nagode" yana son tambayarta khadijah amma yyi shiru, can ya mike ya wuce bedroom, kwance ya ganta tayi bacci tana rufe da bargo, ya karasa kusa da gadon yana kallonta, dukawa yyi dai dai fuskarta murya can kasa yace "So early?" Ko motsi bata yi ba alamar ta jima da yin baccin, a hankali yyi murmushi ya kai hannu dogon hancinta ko mai ya tuna yyi saurin withdrawing din hannunsa ya mike ya kashe mata wuta ya fita daga dakin, Sallama yyi ma Mama suwaiba ya nufi kofa ta bi sa da kallon mamaki, yau ma da ya dawo baxai kwana gidansa tare da matarsa ba, wannan wani irin aure ne a gantale, har ya rufe kofa kallonsa take baki sake. Washegari lahadu Khadijah na xaune parlor da tuwo da miyar kuka da mama suwaiba tayi mata, da cokali take cin tuwon mama suwaiba kuma na kitchen tana wanke wanke, bude kofa aka yi ta daga kai da sauri sudais ya shigo parlorn rike da babban jaka, ajiye jakar yyi yana wara ido yace "Kaiiii yanxu xa ki iya cinye wannan tuwon Amira?" Rufe fuskarta tayi da kujera da sauri tace "A'a fa xan rage in ci anjima" dariya yyi ya juya ya fita ya shigo da daya jakar ya ajiye sannan ya xauna kan lallausan carpet da take xaune yace "Ci da yawa abin ki kin ji, sai ki haifo mana yara masu karfi" bata dago kanta ba har lkcn yyi murmushi ya bude zip din jakar ya fara fiddo kayan ciki, sai bayan da ya Ciro kayan jakunkunan gaba daya sannan yace "Here... you like them?" sai a sannan khadijah ta dago a hankali tana kallon kayan, kayan babies ne masu tsada ko wanne set biyu, shiru ta yi tana kallon kayan, ya ware nata dogayen riguna masu kyau gudu hudu yace "Wannan kuma naki" sauke idonta da ya kawo ruwa tayi a hankali, ya hade rai yace "Baki so ne xa ki min kuka" bata san lkcn da ta fashe da kuka ba ta hade kanta da kujera, yyi shiru yana kallonta, can ya fara mayar da kayan gaba daya jaka yana gamawa ya kai jakunkunan daki sannan ya nufi kofa ya fice daga gidan ya shiga motarsa ya wuce. Har bayan kwana biyu Sudais bai je gidan ba duk da he is just trying not to go amma hankalinsa gaba daya na can, sosai hankalin khadijah ya tashi don tasan kilan fushi yake ne ya sa, tana son kiransa amma ta kasa, ganin baxata iya jurewa ba kuma ta kira sa, a lokacin yana gida bedroom din Mami suna hira da Anty Maryam, ganin kiran yyi ta kallon screen din kafin yyi silencing wayar ya mike yace "Mami bari in tafi in shirya xan fita yanxu" daga haka ya bar dakin bayan yayi ma Anty Maryam ma sallama, Mami ta tabe baki tace "Kwata kwata Aliyu ba shi da gaskiya yanxu, I really don't knw what he is up to, tun ma kafin ya bar kasar months back na lura da haka kuma gashi ya dawo ya ci gaba da behavior din, there is something big he is hiding kuma shi ya hanasa auren ma, dubi fa yanda ya axalxalemu a kan jiddah duk ya daga mana hankali shi aure amma lkci daya kinga kuma abinda yyi, ni na haifesa ba shi ya haifeni ba don hka I will fish out what he is up to soon" ita dai Anty Maryam bata ce komai ba sai kallon yayarta take. Sudais na barin gidan ya tafi can gidansa, Khadijah na kitchen tare da Mama suwaiba suka ji an shigo parlorn, fitowa tayi tana ganinsa ta turo baki, ya karaso parlorn ya xauna yana idonsa a kanta, ta sunkuyar da kai ta isa kusa da shi ta xauna a kasa, yace "How are you?" Kin cewa komai tayi, ya d'an yi murmushi ya dau wayarsa yana danna, a hankali tace "Ina yini" ya kalleta yace "Ban yini ba" kamar xata yi kuka tace "Ni ban san me nayi maka ba" yace "Na kawo maki abu kince baki so mana" xaro ido tayi tana kallonsa tace "Ni??" Yace "Ehh" murmushi tayi tace "I don't knw how to thank you that day, that was why...." Hawaye cike idonta ta kare maganar, Kallonta kawai yake bai ce komai ba. Haka nan rayuwa ya ci gaba da kasancewa bayan dawowar sudais Nigeria, duk safiya, rana har da daddare xai xo ganin khadijah, kayan ciye ciye yake xuwa mata shi idan xai xo da daddare wani lkcn shi ma ya ci abinda xai ci a gidan, ita dai Mama suwaiba na son sanin me ya janyo bai kwana gidan amma bata san wa xa ta tambaya ba tunda ba wani hira can suke yi da Khadijah ba, toh ko don tana da ciki ne yake haka, tambayar da ta dinga yi ma kanta kenan har hakan yasa ta d'an fara jin haushin sudais din, rana daddaya ne xai shigo gidan ba tare da kayan baby ba, xuwa yanxu irin siyayyar kayan baby da yyi mata sai ayi xaton yara goma xata haifa, komai ya gani ya Burgesa sai ya daukar mata. A haka har watan haihuwar Khadijah ya tsaya, mama suwaiba bata yi kasa a gwiwa ba wajen bata taimako irin na gargajiya don tausayi take bata, kusan duk yamma sudais sai ya lallaba Yusuf sun je gidan kawai don ya dubata, har ransa yake fargabar kar abu ya sameta, wani sanyi tayi gaba daya a kwanakin ko da yaushe a kwance xaka ganta, idan ya tambayeta ko akwai inda ke mata ciwo sai tace babu ko ina. Ranan Sunday da sassafe ya shirya ya fito parlor yana kallon Mami dake dinning yace "Mami xan fita in dawo" tace "Ranan lahadin ma?" Murmushi yayi yace "Mami it's urgent ne, kuma akan..." Katse sa tayi tace "Aliyu" ya dago da sauri, bata fuska yayi yace "Mami wllh duk kika ce min Aliyu sai gabana ya fadi, cos u always call that name when serious" ta masa wani kallo tace "Toh da meye sunan naka?" Yar dariya yyi yace "Sudais mana" tace "Ni na sa maka sudais?" Dariya yyi sosai yace "Ni na sa ma kaina Mami Aliyun sunan tsoffi ne I...." Ta katse sa tace "What ever.... kaje duk inda xaka ka dawo ka sameni in sha Allah gobe xa a kai kayan can da kasa nayi jere da su a daki" yace "Allah ya kai mu Mami" daga haka ya fice daga parlorn, gidansa ya nufa direct. Mama suwaiba na kitchen tana aiki, bai jira sun gaisa ba ya wuce daki, xaune ya ga khadijah ta takure waje daya, Ya durkusa kusa da ita da sauri yace "Are you okay Amira?" Ta girgixa masa kai da kyar, da damuwa yace "What's wrong? Kina jin ciwo ne jikin ki?" Karfin halin nuna masa bayanta tayi, yace "Yana maki ciwo?" hawayen da ya gani idonta ya rikitar da shi lkci daya ya dagota yace "Let get to the hospital....." Kwace kanta tayi ta koma ta durkushe a wajen tana rintsa ido tace "Ya daina" Allah ma yasan daurewa kawai take, ga ciwon kamar ana kara mata take ji, bata san lkcn da ta sakar masa kuka ba a hankali tace "Wayyo ka taimakeni plss" bai sake saurararta ba suka fita dakin, Mama suwaiba bata ma san sun bar gidan ba tana kitchen, har suka isa asibiti Khadijah bata sani ba duk ta rikice, wani asibiti me tsada ya kai ta banda Wanda Yusuf ke aiki, bbu bata lkci nurses suka amsheta da wani likita, yanda Sudais ya daga hankali sai ka rantse ance masa mutuwa xata yi, khadijah bata yi fatan kara experiencing kwatankwacin irin wahalar da ta sha na labour ba har ta bar duniya, tun da suka je take wahala amma shiru, Sudais ya kira Yusuf ya sanar da shi suna asibiti, Yusuf yace "Me yasa baka kawo ta asibitin mu ba" Sudais yace "Just" Yusuf yace "Toh wani asibitin ku ke?" Sudais ya gaya masa, tabe baki Yusuf yyi yace "Kudi ya ma yawa ne, any way idan ta haihu ka kirani" Sudais ya katse wayar ya jinginar da kansa da kujera yana mai yi ma khadijah addu'a a xuciyarsa, bayan awanni biyu ya sake kiran Yusuf, Yusuf yace "Ya? is she delivered" a hankali Sudais yace "Har yanxu" Yusuf yace "Toh fah, ko dai cs xa ayi mata, dama am thinking it will be difficult ta haihu da kanta, any way bari in taho yanxu" bayan wani lkci Yusuf ya xo, dariya Yusuf ya shiga yi ganin yanayin sudais yace "Kaiiii... To ai ko jiddah ke labour sai haka bawan Allah" Shi dai Sudais bai tanka sa ba, yawanci likitocin asibitin duk Yusuf ya san su, don haka har labour room yaje gun khadijah, ya ji tausayinta ba kadan ba ganin irin dauriyarta, baxa ka taba cewa haihuwar fari xata yi ba tsabar karfin halinta, bayan wani lkci Yusuf ya bar asibitin bayan ya kwantar ma da Sudais hankali yace labour kawai take babu wani matsala, wasa wasa dai shiru ake ji wanda hakan yasa likitocin suka kira Sudais office nan suka nuna masa it's better ayi mata Cs kada yaran da ita kanta su samu matsala, kusan ba da son ransa yyi signing takardar da aka basa ba, bayan wasu yan mintuna aka fitar da Khadijah labour room xuwa Theatre, anan kuma aka yi nasarar ciro mata boys dinta, sai dai sun jigata kamar yanda ita ma ta jigata. Khadijah ta bude ido a hankali ta ganta kwance wani ward, Mama suwaiba dake gefenta ta sakar mata murmushi tace "Sannu Amira, Allah ya baki lafiya" tashi xaune take son yi taji kamar an danneta ta kasa tashin, Mama suwaiba ta mayar da ita ta kwantar tace "Aa kinga ba ki da lafiya ki yi kwanciyar ki kawai kinji" sai a snn taji wani axaba tun daga cikinta har xuwa kafafuwanta, wasu hawaye suka shiga sakko mata cikin rawar murya tace "xafi nake ji" fita Mama suwaiba tayi sai ga ta ta dawo da likita, likitan ya duddubata ya mata Allah ya sauwake sannan ya fita, Nurse ce ta shigo ta mata allura ta fita, bayan fitar ta sai ga Sudais ya shigo khadijah ta bude ido tana kallonsa, ya karaso gefenta cikin sanyin murya yace "Amira...." Bata iya ta amsa sa ba, a hankali ya sa hannunsa cikin nata cikin sanyin murya yace "Be strong Amira, you will get better in sha Allah.." Hawaye ya sakko idonta sai dai bata ce komai ba, ya sakko da fuskarsa dai dai nata yana murmushi a hankali yace "Baki tambayi yaran ki ba ko bakya son su?" Ta gyada masa kai, shiru yyi yana kallonta, can yyi murmushi yace "Toh sai ki bani su" Murya can kasa hawaye na xuba idonta tace "Na baka" ya fadada murmushin fuskarsa yace "Sure?" Throughout ranan Sudais was by her side tare da Mama suwaiba, Yusuf ma ya xo yyi mata barka ya wuce, ba a nuna mata yaran ba kuma bata tambaya ba har ta sa a rai kila ma mutuwa suka yi wanda tunanin hakan yasa mata nutsuwa sosai don har ga Allah bata ma son ganinsu, haka kawai taji bata san su, Sudais dake lura da cewa she was so depressed ya dinga kokarin ganin ya sa ta walwala sai dai ta kirkiri murmushin karfin hali, sallah kadai ke sa shi ya bar gefenta, tun karfe shidda mama suwaiba ta koma gida dauko kaya, duk kiran da aka dinga ma sudais a waya kin dagawa yyi daga karshe ma ya sa wayar a silent, A daren ranan bayan sudais yaje sallar magrib da ya tashi dawowa ya shigo rike da daya daga yaran wata nurse na biye da shi da dayan, tun da suka shigo khadijah ke kallonsu, yana murmushi ya ajiye babyn a gefenta, sosai gabanta ya fadi ta dinga yi ma jaririn wani kallo ganin kamar Aliyu yyi kaki, babu abinda new born din ya mance na ubansa tun daga haske, hanci, kai har bakinsa... Nurse din ta ajiye mata daya carbon copy din yaron dake gefenta kusa da d'an uwansa tana murmushi tace "Congrat mum twins, Allah ya raya su" daga haka ta fita, a hankali Sudais yace "Ain't they cute? I mean the innocent new souls" khadijah bata san lkcn da ta fashe da kukan takaici ba cikin rawar murya tace "Don Allah ka tafi da su, wllh bana son su, ni dai bana son su ka maida masu su" kuka take sosai kamar xata shide, ganin haka Sudais ya mike ya dau yaran gaba daya ya fita da su dakin. Sudais na dawowa dakin ya dinga kallonta har ya iso kusa da ita yace "Me yaran suka maki da kike cewa baki son su Amira" kin cewa komai tayi, ya ja kujera ya xauna yyi shiru, bayan kusan minti goma wayarsa ya fara ring dauka yyi ya duba yaga Mami ce, yau ta kirasa yyi sau hudu duk bai dauka ba, ya mike yana kallon khadijah da ta lumshe idonta yace "Mama xata dawo yanxu, ni xan je gida Mami na ta kirana, gobe da safe xan xo kin ji?" Bude ido tayi tana kallonsa yace "Be strong, kuma kar ki sake kuka plss" gyada masa kai kawai tayi ya juya ya fita. Bayan fitarsa da yan mintuna mama suwaiba ta shigo, sannu ta dinga yi mata, ta xauna kusa da ita tace "Kin ma ga yaran naki kuwa Amira" Khadijah ta hade rai tace "Ehh" daga haka ta rufe idonta, ana yin isha mama suwaiba tayi sallah a nan ward din da bayan ta shimfida dankwalinta a kasa, bude kofar ward din aka yi nurses biyu suka shigo da babies din Khadijah ta rufe ido da sauri, kan gadon jariran dake kusa da na khadijah suka kwantar da su, daya daga nurse din na kallon Mama suwaiba da ta mike ganin yaran tace "Xa a iya ba su nono yanxu idan suka bukaci haka" daya nurse din na nuna mata babyn kusa da ita tace "Wannan shine Hasan, na kusa da shi kuma Hussain" Mama suwaiba tace "Maa sha Allah, Allah ya raya mana su" nurses din suka amsa da amin sannan suka fita, mama suwaiba sai kallon kyawawan fararen yaran take tana murmushi sai dai abinda ke daure mata kai daga Sudais har Khadijah babu wanda taga yaran suka biyo, a ranta tace "Ikon Allah, to ko wa suka biyo su kuma maa sha Allah" kallon khadijah tayi da ta ki bude ido har lkcn, tausayinta ta dinga ji don idan akwai abinda ta tsana shine ayi ma mace operation. Karfe sha daya da wani abu mama suwaiba ta kwanta a spare bed dake Dakin, har ta fara bacci taji kukan jariri, ta bude ido da sauri taga daya ne ke motsi, ta Mike ta daukesa tana kallon khadijah, Bata san Khadijah na jin yaron ba sai dai idonta a rufe yake har sannan, Mama suwaiba da a tunaninta bacci take ta rungume yaron ta xauna, haka mama suwaiba ta dinga lallaba su tana basu ruwa a feeder ganin yunwa suke ji har Washegari da safe. Karfe tara saura sudais ya shigo ward din,sanye yake da farar shirt da black jean yayi kyau ba kadan ba, direct gun babies dake cikin cot dinsu bayan an masu wanka ya nufa, ya dau daya ya lumshe ido ya daura lips dinsa a soft cheek din babyn, juyawa yayi ya kalli khadijah dake bacci, jikinsa yyi sanyi don da alama mama suwaiba ta je gida dauko abu, daga ita sai yaran ne a ward din, nobody to stay with them, banda tsotson baki bbu abinda yaron dake hannunsa yake alamar yunwa ya kalli d'an uwansa shi ma yaga haka yake da bakin, yana ta tsaye dakin bai tashi Khadijah ba mama suwaiba ta shigo bayan sun gaisa yake tambayarta ko Khadijah ta fara basu abinci ne, Mama suwaiba tace "Aa bata basu ba da nayi mata magana daxu ce min tayi cikin ta na ciwo har na fita na kira wata nurse, tun jiya ruwa kawai nake ba su" Sudais bai ce komai ba ya xauna saman kujera, bayan wani lkci yace "Toh ita ta fara cin abinci ne?" Mama suwaiba tace "A'a ga shi nan dai kunu ma na je gida na dama mata, cewa likitan yyi shi kadai xata iya sha anjima, toh kafin ta tashi shine naje nayo" yace "Toh sannu mama" ya d'an jima a dakin kafin ya bar asibitin kuma har lkcn khadijah bata tashi ba. Wasa wasa yau kwanansu uku a asibiti amma khadijah taki ba yaran nono, da farko cewa take cikinta na mata ciwo baxata iya ba sudais ya siyo masu madara na jarirai mama suwaiba na basu, har abun ya fara daure ma mama suwaiba kai don har sannan khadijah taki daukan yaran ta, tunda tayi kokarin bata su sau daya ta ki amsan su ta kuma ga kamar ranta ya bace bata sake bata su ba. Satinsu daya da kwana daya aka sallamesu asibitin bayan Sudais ya biya bill din, duk yaran na hannun mama suwaiba don khadijah bata amshi ko daya ba, ya bude motar bayan sun isa gida ya amshi dayan yaron hannun Mama suwaiba, ta fito rike da dayan ta nufi cikin gida, kallon khadijah yyi da ta fito ita ma ya mika mata yaron, dauke kai tayi ta bar wajen da sauri tace "Ni dai baxan iya ba" Wani kallo ya mata da mamaki yace "Kee" ta juyo tana kallonsa, mika mata yaron yyi fuskarsa daure yace "Karbesa" kamar xata yi kuka tace "Xai iya faduwa pa" yace "Ya fadi" ganin yanda ya tsare ta da ido ta karbi yaron hawaye har ya kawo idonta ya yi gaba ya bar ta gun tsaye, a hankali ta bi bayansa ba tare da ta bari ta kalli yaron hannunta ba, sudais ya karbi yaron hannun mama suwaiba ya wuce bedroom da shi khadijah ta bi bayansa, gefen gado ta xauna ta ajiye yaron kan gadon, yana kallonta yace "Basu abinci yanxu" da sauri tace "Ai naga sun sha madara fa, ni....." Katse ta yayi yace "Baki son yaran nan koh Amira?" Ta kallesa ta gyada kai a hankali kamar xata yi kuka, yana mata wani kallo yace "Dama kin san baxa ki so su ba kika yarda kika haifo su duniya, me yasa baki amince an raba ki da su tun a ciki ba?" Cikin rawar murya tace "Toh ai babu kyau" yace "Ohk.... abinda kike masu yanxu da kyau kenan" shiru ta yi hawaye na sakko mata, yace "Kin san Allah idan baki basu abincin su ba am leaving here now, kuma wallahi babu ruwana da ke, are you this wicked?" da sauri tace "Kayi hakuri xan basu" tana magana hawaye na xuba idonta don ita har ranta da gaske bata son yaran, Sudais yace "Toh ba su yanxu" tana share hawayen idonta ta fara bude zip din rigarta xata sauke rigar yayi saurin dakatar da ita "Kee haka aka ce maki ake yi?" Kamar xata yi kuka tace "Toh ai ban iya ba" juyawa yyi ya fita sai gashi tare da mama suwaiba, yana tsaye ta gwada mata yanda xata yi tana dariya sudais ya juya ya bar masu dakin, har da kukanta ita wai xafi take ji, Mama suwaiba ta dinga lallaba ta don ita ma tausayin yaran take ganin basu samu gatan shan nonon uwarsu ba tun da suka fito duniya, da kyar ta amince ta ba dayan ma, a ranta kuwa tasan shine farkon shan su kuma shine karshe don ita dai baxata iya ba. Kwanansu biyu da dawowa daga asibiti Sudais ya shigo dakin da Khadijah take da safe, xuwan sa kenan gidan, farar Gezna ce jikinsa dake ta kyalli, waya ne kare kunnensa ya shigo dakin yana magana amma can kasa kasa, ya nufi gun babies dake kwance yana kallonsu kamar yanda Khadijah da ke tsaye gaban madubi ke ta kallonsa tun shigowar sa, Sudais is just the real definition of handsome, duk da wayar da yake gaba daya hankalinsa na kan yaran dake ta tsotson baki yana murmushi, xuwa jikin khadijah yyi kwari sosai don har aikin ya gama warkewa, sosai kirjinta suka ciko har ciwo suke mata amma taki ba ma yara abinci, yanxun ma mama suwaiba ce ta shigo da su ta kwantar ko xata tausaya masu ta basu nono, Sudais ya mayar da wayarsa aljihunsa ya juya ya kalleta tayi saurin dauke kanta, ya xauna gefen gadon yace "I know baki abinci ba yau" ba tare da ta kallesa ba tace "Na basu ka tambayi Anty" bai ce komai ba, bayan wasu mintuna yace "Wani sunan za a sa ma babies din?" Still taki kallon inda yake tace "Nima ban sani ba" yace "Baki sani ba kuma?" Tace "Ko wanne ma ka sa masu" yace "A'a ke xaki xaba da kanki ba yaran ki bane" kin cewa komai tayi, yace "Am talking to you Amira, kuma akwai inda xa ni" ta langwabar da kai a hankali tace "Toh Muhammad da...." Sai kuma tayi shiru, yace "Da wa?" A hankali ta saci kallonsa tace "Kai" ya buda ido sosai yace "Ni kuma?" Tace "Ehh, ur name" murmushin sa mai kyau yyi yace "Aa ki xabi wani sunan dai Amira" hawaye ya kawo idonta tace "Ni kai nake so a sa" Yace "Aliyu kike nufi?" Ta gyada masa kai, wani murnushin ya sake yi yace "Sunan mahaifinsa dai kenan" da sauri khadijah da gabanta yyi mugun faduwa tace "Noo, Brr Aliyu Sudais nake nufi not Dr Aliyu Turab" Shiru Sudais yyi yana kallonta, mikewa yayi bai sake cewa komai ba ya fita yana murmushi. Raguna biyu sudais ya yanka ma 'yan biyun, Hasan aka sa ma Muhammad, Hussain kuma Aliyu, kusan duk sadaka yyi da daya ragon ya bar ma khadijah daya mama suwaiba ta gyara mata, ita dai mama suwaiba kanta ya gama daurewa taga babu me xuwa barka tun dawowarsu, shiru kuma ba xancen taron suna gashi har an gyara rago, Yusuf kadai ya xo gidan a ranan, nan xuciyarta ya fara wani tunanin anya wa en nan ma'aurata ne ma kuwa, don ga dukkan alama wnn dai ba aure bane domin kuwa tun xuwanta bata taba ganin Sudais ya kwana gidan ba, amma meye tsakaninsu? Sudais na bedroom dinsa a can gidan Abbansa da yamma, shigowarsa gidan kenan tun safe da ya fita, Anty Maryam ce ta shigo dakin ya juya yana kallonta sannan ya gaisheta ta amsa da murmushi tace "Kasan an kai ma jiddah kaya kuwa Aliyu, and sati biyu aka sa bikin from today" kasa ce mata komai yyi da farko baki bude, can yace "Amma dai ni babu wanda ya gaya min, sati biyu kuma Anty, what's d rush for, ni Wllh jiddar nan maganar gaskiya ta fitar min a kai, don Allah ni dai Anty...." Dafe kansa yyi yace "Ohh God, sati biyu fa ku ka ce?" Tabe baki Anty Maryam tayi ta juya ta bar masa dakin, zaunawa yyi gefen gado yana rike da kansa, can ya dago ya tashi ya fita, dakin Mami ya shiga ya sameta tana waya ya tsaya ya jira har ta gama sannan ya marairaice yace "Mami Anty Maryam ke ce min...." "Saura sati biyu bikin" Mami ta karasa masa tana masa wani kallo, tsaye yyi yana ta kallonta can ya juya ya fice a dakin, Mami ta fito ita ma ganin dakinsa ya koma ta fita compound, gun drivern gidan ta nufa, ya gaisheta da ladabi ta amsa masa tace "Musa, ina son ka min wani d'an aiki ne don Allah" with respect yace "Toh Hajiya aikin me xan yi" Tace "Ina son idan sudais ya fita gidan nan ka bi sa ka gano min ina xa shi, ko yanxu ko anjima ko da daddare" da mamaki yace "Barrister?" Tace "Shi" yace "Toh in sha Allah Hajiya" Har ta fara tafiya ta juya tace "And be very very careful you knw who you are dealing with" Sorry it's nt much, long chappy ltr in sha Allah. Mami na shiga parlor Sudais dake tsaye kusa da window din bedroom dinsa ya sauke curtain din ya bar jikin windan ya rungume hannayensa kamar me naxari, can kuma ya nufi study area dinsa ya ja kujera ya xauna, then... What's Mami telling Musa? Ya kusa minti talatin xaune yana jiran ya ji fitar musa a gidan da mota domin kuwa hakan kadai xai sa ya cire wani xargin da yake a xuciyarsa, amma har kusan magrib shiru Musa bai fita ba, Sudais ya tabe baki ya mike ya tafi ya dauro alwala ya dawo ya xauna, lumshe ido yyi duk jikinsa yyi sanyi "Jiddah? Sure yasan ya so jiddah ba kadan ba a da can, but he just don't knw what came over him all of a sudden yaji kawai ta fice masa a kai, gashi dai babu abinda tayi masa, ko don an takura sai yyi auren ne yake jin hakan, gaba daya ya ma rasa tunanin da xai yi a lkcn, toh shi yanxu ya xai yi da Khadijah da little babies dinta idan aka tilasta sa yin aure yanxu, bude ido yyi ya xauna da kyau yana naxarin idea din da ya xo masa, ya kama mata wani apartment din kenan? Shafa kansa yyi yana kara naxarin shawaran a ransa, jin xa a tada sllh ya mike ya nufi kofa ya fita dakin, ana idar da sllh ya dawo daki ya dau makullin motarsa ya fita, ce ma Mami dake parlor a xaune yyi sai ya dawo ba tare da ta kallesa ba tace "Allah ya kiyaye" yana shiga motarsa ya fita compound din bayan mai gadi ya bude masa gate, sai da ya kusa isa titi ya yaga musa ya danno kan mota xai fito gidan a guje ta madubinsa, Sudais ya hau kan titi driving slowly yana yana kallon musa dake can baya ta madubi, a hankali shi ma musan ke driving din, Sudais yyi murmushi ya kara gudun motar sai yaga shi ma ya kara, gidansu Yusuf ya nufa musa na biye da shi a baya har lkcn yana parking a waje ya fito ya ga musa nesa da shi a motar yyi kamar bai gansa ba ya shiga gidan, bai samu Yusuf a gida ba duk da ba gidan yyi niyyar xuwa ba, ya tsaya har suka d'an yi hira da mahaifiyar Yusuf sannan ya mata sallama ya wuce, gida ya koma yyi parking a waje ya fita ya shiga gidan, tare da mai gadi ya ga musa a xaune yana kallonsa yace "Same ni a waje musa" daga haka ya fita gate din, Musa ya mike ya bi bayansa sai dai fa ya tsorata, Sudais na kallonsa da kyau yace "Hajiya ce ta sa ka bi ni ka ga inda xa ni daxu?" in ina musa ya fara yi, Sudais ya daure fuska yace "Malam amsa min tambayata" gyada kai musa yyi yace "Kayi hakuri barrister umarnin da Hajiya ta bani kenan" Sudais yace "Ohk naga alama, this shud be ur 1st and last, ko da wasa ka kuskura ka sake bin bayana a mota I won't take it likely with you" daga haka ya shiga gida ya bar sa tsaye gun. Sudais na shiga daki yayi dialing number jiddah, bayan ta dauka suka gaisa murya can kasa yace "Kina ji na jiddah?" Tace "Ina ji, ya su Mami?" Yace "They are fyn, ina son mu yi wata magana ne da ke, are you alone?" Tace "Yeah ni kadai ce, hope all is well" yace "Noo, Jiddah plss ki min wata alfarma don Allah" jin tayi shiru ya kwantar da murya yace "look jiddah am still yet to be settled, they are a lot of things I have not fixed right, beside ke ma fa ba wai kin gama karatun nan bane, why not ki gama nima nayi settling abubuwan dake gabana before any other thing, why the rush" ita dai tayi shiru tana saurararensa har ya gama, ta d'an yi murmushi tace "So what are you insinuating?" Ya lumshe idanuwansa ya bude a hankali yace "A kara daga bikin jiddah..." Tace "Uhm Aliyu kenan, ai ba wai na rasa manema bane kawai dai ina sonka ne fisabillah kamar yanda kai ma kake so na a baya, kuma idan baka manta ba kai ka damu ayi bikin nan a da, don kuma ka samu wata warce kake so bai kamata ka dinga yawo da hankalina da na magabata na ba, Ba damuwa xaka iya turowa a dau kayan ka, na hakura... Allah hada kowa da rabonsa na alkhairi" duk da jikin Sudais yyi sanyi sosai amma ya dake yace "Haka kika ce?" Tace "Ehh, ka turo a kwasa kayan ka" yace "Ohk" daga haka ya katse wayarsa, fadawa kan gado yyi ya lumshe ido thinking if he made the right decision, mikewa yyi ya sake kiranta sai da ya kusa katsewa ta dauka, yace "Then you do me the favour of telling ur mum ta kira Mamina ta sanar da ita, baxan iya kai ma Mami wannan xancen ba don xata yi tunanin ni ne na fasa..." Jiddah tace "Ohk" daga haka ta katse wayar, ya sauke ajiyar xuciya ya koma ya kwanta, Khadijah ce ta fado masa ya dau wayar ya shiga kiranta, ba a dau lkci ba ta daga cikin sanyin murya tayi masa sallama ya amsa yace "Babies din ne ke kuka haka?" Turo baki tayi ta kalli Mai sunansa dake tsala kuka tare da d'an uwansa tace "Toh Anty tana kitchen ban san me take ba" mikewa yyi xaune yace "ina yaran?" Tace "Ga su nan kan gado a kwance" shiru yyi ya ma rasa abinda xai ce mata, can ya katse wayarsa, Khadijah ta kalli wayar da sauri, jikinta yyi sanyi ta shiga kiransa kuma, har ya katse bai dauka ba, ajiye wayar tayi tana kallon yaran dake ta kuka, fashewa tayi da kuka tace "Toh ni ce na sa su kuka, ko me nayi masu?" Can karshen gado ta koma ta xauna tana hararansu, Mama Suwaiba na kitchen tana jin kukan yaran taki fitowa don lamarin Khadijah ya fara isarta, ya mutum xai haifi yara ya dinga masu abinda take yi, jin kukan yaran yyi yawa ta fito ta shiga dakin tana kallon khadijah tace "Ke kam baki da kirki gaskiya, kiyi hakuri hakan da na gaya maki, banda rashin hankali haka taki uwar ta maki, me yaran suka maki, kinsan baki son haihuwar kika dau cikinsu, kin xata hakkinsu xai bar ki? Yara ko kwana arba'in basu cika ba kika haramta masu nono, toh da haka ake haihuwa kam da ba ayi ba, ni tunda nake ban taba ganin uwa irin ki ba, na maki magana a matsayin wacce tayi jika dake, na maki magana a matsayin 'ya na maki magana a matsayin ki na shugaba gare ni amma duk a banxa, toh wllh bari mijin naki ya dawo ta dalilin haka ma ni sai na bar maku gidan ku baxan iya ci gaba da xama ina ganin xaluncin nan ba, tun da uwata ta haifeni ban taba gani ko jin tarihin uwa irin ki ba, wannan kuma ya wuce yarinta tsabagaren iskanci ne, kilan idan na bar gidan kika ga babu mai daukarsu idan suna kuka ke xaki dauke kayan ki" daga haka mama suwaiba ta fita tana rike da yaran, hade kai da gwiwa Khadijah tayi tana kuka, Mama suwaiba na komawa parlor ta dau feedern su da ta hada masu tana jiran ganin fitowar Khadijah ta dauka ta je ta basu amma shiru, Su duka biyun ta hada tana ba abincin lkci daya duk tausayin su ya cikata, Sudais ne ya shigo parlorn, ko gaishesa bata yi ba tace "Yallabai dama ina jiran ganin dawowar ka" xaunawa yyi kan kujera yace "Toh gani mama" tace "Ina jin xan bar wannan aikin ku samu wata, ban jin xan iya ci gaba da xama gidan nan ina ganin abinda wancan yarinyar ke ma jariran nan, nayi mata magana a matsayin ta na shugaba gare ni, nayi a matsayin uwa gare ta, kai babu abinda ban ce mata ba a kan yaran nan, kwata kwata bata son su kamar a dole aka mata cikinsu, me yaran nan suka mata fisabillah, kai tun da kake ka taba jin uwa haka, yau ko da shegu ne yaran nan wllh basu cancanci abinda take masu ba, don haka baxan iya ba ni xan tafi kilan idan taga ba ni xata dinga masu abinda ya kamata" Sudais ya lumshe ido ya bude kafin ya mike ya wuce dakin da Khadijah take, dago kai tayi daga gwiwanta jin shigowarsa, wani kallo ya dinga mata kafin yace "Tashi ki je ki karbi yaranki, idan ma kashe su xa kiyi ki kashe su da hannunki" kin tashi tayi yyi mata wani tsawan da ya firgitata ta tashi a tsorace, tun da take bata taba ganinsa haka ba, kofa ta nufa da sauri ta fita, gun mama suwaiba ta tafi ta karbi yaron daya hawaye na sakko mata, tana ta tsaye yana hannunta, Mama suwaiba tace "Ki tafi ki kwantar shi ki dawo ki amshi wannan, in sha Allah tafiya ta xan yi baxan ci gaba da xama da mutum irin ki ba" a sanyaye ta je daki ta kwantar da shi, Bata yarda ta kalli sudais da ke ya tsaye ba ta koma ta dauko dayan, ta dawo ta ajiye sa kusa da d'an uwansa tana hawaye. Sudais na kallonta yace "Gobe xan baki kudin mota sai ki kai su gidan marayu ki bar su a can" ta kallesa da sauri tace "Da gaske?" Yace "Ehh" murmushi tayi tace "Toh nagode" Wani kallo kawai ya dinga mata yace "You are very heartless Amira, ki duba ki ga ni da na ajiye ki gidana na taba sanin ki?? Ban san ki ba ban san komai naki ba, I just saw you are helpless and I decided to help you... Amma yara su xauna wata tara cikinki ki haifesu sannan ace baki da makiya kamar su, just look at the helpless souls, me suka maki Amira? Me yasa kike shafa masu laifin ubansu?" Xaunawa tayi gefen gado bata ce komai ba, ya gyada kai yace "Na san maganin ki" daga haka ya fita dakin ya bar gidan gaba daya, turo baki tayi ta kwanta can nesa da yaran, a xuciyarta tace to ita ta iya rainansu ne, kawai su yi ta kuka kamar ana mintsilinsu baxa su yi shiru ba. As usual yau ma da daddare hangame baki Khadijah tayi tana bacci suka tashi suna kuka kamar ko da yaushe mama suwaiba ta xo ta kwashe su ta tafi dakinta tana girgixa kai. Washegari da safe Sudais ya dawo gidan, dubu Hamsin ya kawo ma mama suwaiba yace ta tafi kawai, duk da mama suwaiba ita ta fara bukatan hakan amma sai ta ji ba dadi, ta fara tausayin yaran, Sudais yace "kar ki damu mama idan taga babu kowa gidan xata dinga kula da abun ta, kiyi tafiyar ki kawai" Mama suwaiba tace "Toh shkkn, Allah yasa ta gane" Sudais yace "Ameen, amma mama kar ki tafi kina jin haushinta don Allah, ba laifinta bane but xata daina in sha Allah" shiru mama suwaiba ta yi shiru tana tunanin to ko dai iskokai gare ta, can tace "Toh shkkn, Allah ya shiryeta ya yaye mata abinda ke damunta, amma xa mu iya sallama da ita in roketa gafara idan na taba saba mata" Sudais yyi murmushi yace "Toh ki shiga ku yi sallaman mama" mama suwaiba ta shiga ta tada Khadijah nan tace mata xata tafi, Khadijah dake ta kallonta da mamaki tace "Ina xaki Anty?" Mama suwaiba tace "Kauyen mu mana" Khadijah ta xaro ido tace "Toh yaran fa?" Sakin baki mama suwaiba tayi tana kallonta a xuciyarta tace Lallai gaskiyarsa bata da lafiya, a fili kuwa tace "Toh anjima ai xan dawo" daga haka ta fita, suka yi sallama da Sudais bayan ta hada kayanta ta wuce cike da kewan Khadijah da yan biyun. Sudais ya dau yaran ya kai su can dakin da Khadijah take, har lkcn tana xaune, yana shigowa da damuwa tace "Toh wa xai dinga kula da yaran yanxu?" Yana mata wani kallo yace "Uwarsu" daga haka ya fita yana kallon wayarsa dake ring, ganin Mami ke kiransa ya d'an yi jim kafin ya daga, tace "Aliyu ka dawo gida yanxu ina neman ka" bata jira yace komai ba ta katse wayar ya koma dakin Khadijah yace "Xan je gida yanxu" kamar xata yi kuka tace "idan suka fara kuka fa? Ni ya xan yi?" Yace "Sai ku yi tare" daga haka ya fita ta fashe da kuka a hankali tana kallon yaran. Karfi Sha daya saura Sudais ya isa gida, bai yi mamakin ganin set din akwatunan da su Anty Maryam suka kai gidan su jiddah ba a parlor, ba Mami kadai ba yau har Abbansa na xaune parlor da kanninsa gaba daya, Kasa xaunawa yyi ya duka murya can kasa yana kallon kayan yace "Ga ni Mami" Mami tace "Kayan da kace dama su dawo da su ne suka kawo daxu shi yasa na kira ka, sai ka fada mana daga nan kuma ina xa a kai kayan?" Sudais ya sunkuyar da kai bai ce komai ba, muryar Abbansa ya ji yana cewa "Aliyu duk shekaru na a garin nan kai ma ka taso kaga cewar lafiya nake xaune ban taba samun matsala da kowa ba, to ta dalilin ka ma baxan samu matsala da kowa ba domin kuwa kayi kadan, don haka kar ka sake xuwa min da xancen aure ko yanxu ko ba yanxu ba, dama idan ba dauko ma kai dala ba gamo ba ma har nawa kake Aliyu??" Abba ya kalli Mami da ta hade rai yace "Dubesa fa he is just 27 ne ko 28 ya ishe mutane aure gashi ya xo yana wawanci da sokwanci, ke kina ganin haka ma kisan baxa ayi abun kirki ba Idan aka masa auren, get out my frnd" Sudais ya sauke ajiyar xuciya a hankali ya mike ya bar wajen, Mami tace "Fadan kenan Abba?" Abba yace "Toh me xan ce masa, idan akwai wanda kika san xai yi aure soon kawai ki bada kayan gudunmawa, am nt in support of Aliyu getting married now, ya jira idan yayi 30" daga haka Abba ya mike ya bar parlon, murmushi kawai sudais yake shi kadai a daki, Anty Maryam ta shigo tace "Hankalin ka ya kwanta yanxu?" Da sauri yace "Wallahi Anty" Can nesa da Twins din khadijah ta xauna tana ta kallon yanda suke ta motsi, tsoronta daya ya xata yi da su idan suka fara kuka, kamar sun san tunanin da take taji daya ya fara kuka, Tashi tayi da sauri ta dau waya ta shiga kiran sudais, ya fito daga wanka kenan ya dau wayar ya katse ya kirata, kamar xata yi kuka tace "Wallahi gasu nan xasu fara" yace "Xa su fara me?" Tace "Kuka" murmushi yayi yana ci gaba da goge gashin kansa yace "Toh kiyi breastfeeding dinsu" xaro ido tayi tace "A'a ni dai madara Anty take basu" Yace "Toh sai ki basu madaran ai" hawaye ya cika idonta tace "Yaushe Anty xata dawo toh?" Yace "Ta tafi kenan ai" xaro ido tayi ta juya tana kallon yaran, kamar yasan abinda tayi yyi murmushi ya katse wayar ya fara shiryawa. Haka nan Khadijah ta dinga fama da yaran suna kuka tana kuka, gashi tana ta basu madaran basa sha, nan ko tun madarar safe da Mama suwaiba ta hada masu ne take basu, tun daga bakin kofa sudais ke jin kukan yaran ya shigo da sauri, tana ganinsa ta mike ta fashe da kuka tace "Ni dai don Allah ka tafi da su kar ka sake tafiya ka bar su" ko kallonta bai yi ba ya kwace feeder din hannunta bude baki yyi yana kallonta yace "Amira" tana goge idonta tace "Na'am" ya hade rai yace "Tunda kike kin taba shan shayi me sanyi, me yasa ke muguwa ce" kallonsa kawai ta tsaya yi, yyi tsaki ya dau dayan feeder din ma ya fita xuwa kitchen ya xubar da madarar ya xuba na xafi ya hada wani yyi diluting da ruwan gora ya dawo dakin, daukan little sudais yyi ya mika mata daya feeder yace "Ki dauki Muhd ki basa" ta turo baki ta karba ta dau yaran ta fara basa, tsit yaran suka yi gaba daya, bayan wani lkci ya juya yana kallon khadijah dake kallonsa, sauke idonta tayi da sauri, ya kwace feeder hannunta ganin a hancin d'an yaron ta saita yace "Kallon meye kike min xa ki xuba ma yaro madara a hanci" ta hade rai tace "Ai kai ma naga ka kalleni" shiru yyi yana kallonta, can yyi murmushi ya kwantar da little Sudais da har ya fara bacci ya karbi Muhd din hannunta a hankali yace "We will call him shureim" daga ido yyi yaga kallonsa take still, turo baki tayi ta dauke kai ta boye fuskarta jikin gado, yyi murmushi ya na ci gaba da ba shureim sauran madaran, har ya kwantar da yaron bata dago ba, ya tsura ma dogon gashinta ido dai dai lkcn da ta dago a hankali yyi saurin dauke kansa tace "Ae na kama ka" ✨ *NOOR-AL-HAYAT*✨ Daga wannan rana Khadijah ta daure ta fara koyon yanda xata kula da yaranta tunda Mama suwaiba ta wuce, shi ma din ba a son ranta ba kawai sbda sudais take yi, amma har lkcn ta ki basu nono sai dai madara, Sudais ya san kula da yara har biyu xai mata wahala saboda karancin shekarunta amma ya bar ta a haka to see if kusancinta da yaran xai sa ta hakura ta fara sonsu but kamar kara sa mata kinsu ake, komai xata masu sai tayi complain wani lkcn har da kukanta, bbu abinda ke mata takaici sai irin yanda suke hanata bacci cikin dare wani lkcn, duk da during the day kusan sudais ke masu komai, yayi dedicating time dinsa gaba daya ma twins din kamar mara aikin yi, a ranan da Mami tayi querying dinsa na biyu kan ina yake xuwa baya dawowa gida sai kusan sha biyun dare kuma ya fita da sassafe tsabar confusion yace "Mami ni wlh fa yawanci ina gidana, can nake xuwa" Mami da tayi shiru tana kallonsa tace "Kana gidan ka? To ai xan je gidan wataran" shiru sudais yyi jikinsa yyi sanyi gabansa ya shiga faduwa, kasa bacci yyi darren ranan ya rasa me ya kai bakinsa gaya ma Mami wai gidansa yake xuwa, kuma yasan Mami xata aikata xuwa can gidan nasa din, kafin washegari yayi deciding kawai barin gidan don yasan its not longer safe keeping khadijah and her twins in there anymore, misalin karfe tara na safe ya gama hada duk abinda xai bukata a travelling bag dinsa ya shiga dakin Mami gabansa na faduwa, bayan ya xauna gefen gado a hankali yace "Mami dama ina da wani case da xan yi a Abuja yau, kiyi hakuri sai da xan tafi nake gaya maki" Mami dake ta kallonsa ganin yanayinsa tace "Sai kuma yaushe?" ya sosa keya a hankali yace "Kai Mami ai ina jin daga can ma xan wuce Lagos, aiki da yawa ne gaba na, but in sha Allah soon xan dawo idan na gama, ke dai ki min addu'a" tace "Toh Allah ya tsare, Allah ya bada sa'a" a hankali yace "Ameen Mamina" daga haka ya fita duk jikinsa a sanyaye yayi sallama da kanninsa ya bar gidan a motarsa, driving din yake kamar baxai yi ba, why will he lie such great lies to his Mami, sosai hakan ya tsaya masa a rai, har ya isa gidansa he was not his self, khadijah na kitchen ta ajiye 3months old kids dinta da suka xama lukutaye kamar yan watanni shidda kan kujera a parlor, kiris ya rage little shureim ya fadi daga kan kujera ga d'an uwansa a gefensa, sudais ya karasa da sauri ya daukesa yana kallon kofar kitchen din, fitowa Khadijah tayi jin shigowar mutum parlorn, ya hade rai yace "I've warned u severally ki daina ajiye yaran nan kan kujera baki ji koh" tace "Toh they are just crying ni kuma aiki nake yi, kawai basa son mutum ya ci abinci sai dai su ayi ta basu, kuma ni ba gefen kujera na ajiye sa ba shine ya gangaro da kansa, Allah yaron nan baya ji" ko kallonta Sudais bai yi ba ya dinga kallon shureim dake ta kokarin yi masa dariya ya lumshe ido ya manna masa kiss a baki, Khadijah ta turo baki ta juya ta koma kitchen din ganin banxa ma yyi da ita, kwantar da shi sudais yyi kusa da d'an uwansa da ko motsin kirki baya son yi, shi ko irin wasan nan da kicking legs baya yi, sudais yyi kissing din takwaran nasa yana murmushi yace "You look very lazy Aliyu" dariya yaron yyi masa kamar ya ji abinda yace, Khadijah ta fito kitchen da plate din Irish da kwai, ajiye wa tayi nan parlorn tana kallon sudais tace "Have you breakfasted?" Ya kalleta yace "Noo, we are travelling now" ta buda ido tace "To where?" Yace "Somewhere" shiru ta yi tana kallonsa, yace "Ki gama ki hada kayan twins da naki, kafin ten xa mu wuce" bata ce komai ba, yace "Kin masu wanka" ta gyada masa kai, tun da Dr Yusuf ya nuna mata yanda xata dinga masu wanka shkkn ta iya unlike before da take shaka masu ruwa a hanci. Karfe goma da yan mintuna sudais ya gama sa duk kayan su a booth din mota, komai da yasan xai lalace a gidan ya sa ta xubar, yana rike da little sudais ya rufe gidan ita kuma tana rike da Shureim ya nufi motarsa dake waje, ya bude back seat yana kallonta yace "Get in" shiga bayan motar tayi sannan ya mika mata little sudais da karamar jakar dake dauke da flask na ruwan xafi da table water sai gwangwanin madarar su na Nan, ya rufe motar, ya shiga maxaunin driver, sai da ya shiga filling station ya kara mai a motar sannan suka dau hanya, a hankali yace "We are going to Abuja Amira" kallonsa kawai take bata ce komai ba, bayan wani lkci tace "Me xa mu je mu yi a can?" Bai amsa ta ba yana ci gaba da driving dinsa, ba a dau lkci ba gaba daya yaran suka yi bacci tana rungume da su tana turo baki don duk sun mata nauyi a jiki, bayan few hours shureim ya tashi da kuka sannan little sudais ma ya tashi, sudais dake kallonsu ta madubi yace "Ki hada masu madaran a feeder" kamar xata yi kuka tace "Toh da wani hannun, bayan sun danne ni" murmushi yyi ya gangara gefen titi yyi parking ya fito ya bude back seat din ya shiga, shi yayi making din masu madaran a feeder guda biyu tana kallonsa, bayan ya tabbatar babu xafi ya mika mata daya sannan ya karbi little sudais ya fara bashi nasa ita kuma ta shiga ba Shureim, tsabar cin da yaran suke ko kwana biyu gwangwanin madaran baya masu, shi sa sudais ke siyowa da yawa, bacci little sudais ya koma a hannun Sudais ya mika mata shi ta turo baki tace "Wllh kafana ciwo yake min ni dai" yace "Toh ko in bari kiyi driving din?" Dariya ta yi tana wara ido tace "Ni kuma?" Ajiye mata yaron yyi a kafa kusa da twin dinsa da shima ya koma baccin sannan ya fita ya koma maxaunin driver ya tada motar ya ci gaba da tukin sa. Kafin su kai kaduna su shureim sun sha madaran su ba iyaka, kuma duk sai yyi parking ya taimaka mata, gashi ya hanata baccin da take ta ji saboda yaran hannunta da ta fara xai tada ta ta rike su da kyau, sai kusan karfe shidda Sudais ya isa Abuja ya nufi gidansa dake cikin garin, kai kana ganin gidan kasan an kashe kudi ba na wasa ba, ya bude motar ya fita don bude gate din gidan kafin ya shiga da motarsa, babu abinda babu cikin gidan don haka bedsheet yayi spreading a kan gado a daki ya kwantar da twins dake ta bacci, yana kallon khadijah da tayi laushi alamar duk ta gaji yace "Kiyi wanka kiyi sallah kafin in dawo yanxu" daga ya fita, da yake har sponge da sabulunsu ta dauko, bayin ta shiga bayan ta fiddo su a kayansu da sudais ya kawo dakin tayi wanka ta dauro alwala ta fito, tana idar da sllh ta canxa kaya ta sa Hijab ta kwanta dai dai lkcn da su Shureim suka tashi, Ji tayi kamar ta kwala ihu ta dinga hararansu kamar xata yi kuka, ganin xa su fara kuka ta mike ta fara hada masu abincinsu hawaye cike idonta, ita dai ta gaji da wahalan da yaran nan ke bata, tana cikin basu feedern ya shigo dakin, tausayi da dariya ta basa lkci daya ganin yanda take hawaye, ya amshi feeders din hannunta yace "Toh tashi ki dau abinci ki ci kiyi kwanciyar ki" kamar jira take ta mike da sauri, tana cin abinci ya karasa basu abincin su ya kalleta yace "Toh baxa su yi wanka ba" hade rai tayi tace "Nima ban sani ba" yace "Amma ke ai kin yi wanka" tace "Toh ai ni da su ba daya bane" mikewa yyi ya tafi bathroom ya hada masu ruwan xafi sannan ya fito yace "Kije kiyi masu" ta mike da sauri tace "Ni wllh baxan iya ba bacci nake don Allah kayi hakuri, dubi fa wahalar da suka dinga ban a mota" tsayawa kallonta yyi kamar yanda yaran nata ke kallonta su ma, ta je can karshen gado ta xauna fuskarta daure ta dauke kai, dukawa yyi kusa da shureim ya fara cire masa kayan jikinsa har ya gama ya wuce bathroom da shi, dariya ta fara yi kasa kasa ganin shi xai masu wankan, bayan wani lkci sai gashi ya fito ya kwantar da yaron da ya wanke ya rufesa da bedsheet sannan ya dau dan uwansa ya cire masa kayan shi ma ya wuce bathroom da shi yayi masa wankan ya fito da shi ya kwantar kan gado, jaka ya bude ya fiddo masu over all gaba daya da powdernsu da man shafawa, khadijah sai boye fuskarta take kar tayi dariya ganin yanda ya sa masu pampers din, shi dai ko kallonta bai yi ba ya hade rai, yana gama shirya yan biyun ya daukesu ya fita dakin ya kai su nasa dakin ya kwantar da su, Khadijah ta turo baki a xuciyarta tace huta roro, ta mike ta rufe kofar da ya bari a bude ta nufi kan gado ta gyara bedsheet din ta kwanta nan da nan bacci ya dauketa. A haka khadijah da sudais suka fara rayuwa a garin Abuja da yan biyunta, sai dai sudais wasn't comfortable staying under the same roof with khadijah ya rasa dalili, gaba daya a takure yake barin yanda ya ga ta saki jiki totally da shi don ma akwai little sudais da shureim, karfe goma na safiya yake barin gidan baxai kuma dawo ba sai yamma, duk khadijah ta rame saboda rainon yaran don ma ba ta shayar da su, wahalansu yyi yawa, da daya ya fara kuka dayan xai cafke duk su rikitata, satinsu uku a Abuja sudais ya sa aka samar masa Nanny don tausayi take basa barin yanda ya ga ta rame, kamar kar Nanny ta xo lkci daya khadijah ta watsar da lamarin yaran gaba daya ya koma nanny ce ke masu komai ita sai dai tayi girki tayi bacci, abinda sudais ya guda kenan tun farko but saboda tausayinta da yake kawai ya kyaleta, nanny na xuwa gidan da kwana biyar sudais ya tafi damaturu don duba su Mami don Allah ma yasan yana kewar mahaifiyar tasa, kwana biyu yyi a can ya dawo Abuja bayan ya sanar ma Mami yawancin aikinsa yanxu a Abuja yake yi, ta yi masa addu'a da fatan alkhairi. karfe uku saura na yamma sudais ya shigo gidansa na Abuja, sai dai a waje yyi parking don ya gaji da yawa, babu kowa parlorn sai Ac dake ta aiki da kamshin dake tashi, ya haura sama ya bude kofar Nanny da yan biyu a hankali, suna xaune cikin keken koyan xamansu sai wasa take masu da abun jikin keken suna ta dariya gaba daya, sosai matar ke son su don yaran akwai shiga rai, Nannyn baxata wuce shekara talatin da biyar ba, tana ganin Sudais ta mike tace "Sannu da dawowa yallabai" yace "Sannu" ya karasa cikin dakin yana kallon cute yaran dake ta kallonsa, kyawawan karshe ne yan biyun ga manyan idanuwa ga su farare kal kamar larabawa, da wuya mutum ya kallesu bai kara kallonsu ba, ya rasa ne yasa khadijah ta ki sonsu har ynxu, daukansu yayi one by one yayi kissing dinsu suna masa dariya ya ajiye su ya fita dakin, bude kofar dakin da Khadijah take yyi, ya ganta kwance daga ita sai yar doguwar riga tana bacci, ya kusa minti biyu tsaye yana kallonta kafin ya rufe mata kofar ya wuce nasa dakin, wanka yyi ya dauro alwala ya fito ya saka jallabiyarsa ya gabatar da sallahn azahar sannan ya kwanta, Nanny ce ta shiga dakin Khadijah ganin har kusan la'asar ba ta fito ba alamar bata san Sudais ya dawo ba, ita duk tunaninta sudais mijinta ne, cike da natsuwa ta tasheta tace "Yi hakuri na tashe ki madam, yallabai ya dawo" da sauri khadijah ta mike xaune tace "Yaushe?" Nanny tace "Tun daxu" Khadijah tace "Toh" Nanny ta juya ta wuce sannan khadijah ta mike ta tafi bayi ta wanke fuskarta ta fito ta dau Hijab har kasa ta sa ta fita, a hankali ta tura kofar dakin sa ta gansa yyi rub da ciki yana bacci, a hankali ta isa kusa da shi ta durkusa tana kallon kyakkyawan fuskarsa, bude manyan idonsa yyi a hankali, ta koma baya da sauri ta fara kame kame, ya mayar da idonsa ya rufe na kusan minti daya kafin ya bude ya mike xaune, murmushi tayi murya can kasa tace "Sannu da dawowa, baka ce yau xaka dawo ba da ka kira da safe" yace "I was thinking sai gobe xan taho" tace "Ya hanya? Ya su mama" Yace "Alhmdllh, ya twins? duk da nasan kilan duk yau baki gansu ba" sauke idonta tayi daga kallonsa jin yyi shiru ta daga kai suka hada ido, wara mata ido yyi, ta yi murmushi tace "Me xaka ci?" Yace "Komai ma" mikewa tayi tace "Toh bari in yi maka" daga haka ta fita ya koma ya kwanta. A hankali watanni suka dinga ja kamar wasa sai ga shi su shureim sun yi wata bakwai, babu inda basa xuwa da rarrafe, wani shakuwa ne ba na wasa ba tsakaninsu da Sudais, ji yake da su kamar ya hadiye su don so, in har suna wasa a Parlor to suna ganin khadijah suke barin wajen da gudu su tafi gun Nannynsu, sai dai ta tabe baki ko tayi tsaki, har lkcn kamanninsu sak na Aliyu barin hancinsu da idanuwa shi sa take kara jin bata son su, ko ina na gidan kayan wasan su ne, don komai sudais ya gani na yara ko da ya fi karfinsu sai ya siyo masu, dakinsu ya koma kamar na siyar da kayan wasa, yau lahadi sudais na xaune garden shi kadai files a gabansa kana ganinsa kasan aiki yake, lkci daya ya rufe files din gabansa ya lumshe ido, for how long xai ci gaba da ajiye khadijah da yaranta a gidansa, har ransa yake jin baxai iya rabuwa da su ba, but duk ranan da Mami ta gano abinda yake aikatawa yasan that day won't be funny, then meye xai yi da xai kasance da Khadijah da yaranta na har abada With his parent consent, bude ido yyi a hankali ya furta abinda ke ransa a ciki "I shud marry her" girgixa kai yyi ya na murmushi lkci daya abinda Yusuf ya gaya masa one year ago a mota ya fado masa. Khadijah na bedroom ita kadai tana ta jiran jin shigowar sudais amma bai shigo ba, ita kanta bata san me yasa take son ya shigo ba, kuma tasan yana can garden, mikewa tayi ta sa mayafinta ta fita xuwa can din ta tsaya kusa da wani flower yanda baxai ganta ba ta dinga kallonsa, kananun kaya ne jikinsa na 3qtr da shirt da bai yi buttoning ba, tsura ma pen din table dake gabansa ido yyi har lkcn yana tunani, kamar ance ya daga kai suka yi ido hudu da Khadijah, dauke kai tayi da sauri, sai kuma ta jiya ta bar wajen ya bi ta da kallo, murmushi yyi ya na shafa kansa don irin kallon nan da Khadijah ke yi masa ko da yaushe dariya yake ba sa, sau tari ya sha kamata tana kallonsa sai ta fuske, shi din ma yana kallonta amma with swags, kwashe files din gabansa yyi don dama ya gaji ya mike ya wuce ciki yana rike da su, sai da ya fara lekawa dakinsu shureim yaga yanda Nanny ta cika masu kayan wasa a gaba suna ta fama, suna ganinsa suka rarrafo xasu taho gunsa, da sauri ya juya ya bar wajen don bacci yake son yi, a tare suka fara kuka yana tsaye har suka fito corridor nemansa yyi murmushi ya durkusa ya daukesu duk biyun amma da kyar tsabar weight dinsu, ya wuce dakinsa da su, ajiye su yyi kan gado ya kwanta suka haye kansa gaba daya ya lumshe ido yace "Yanxu baxa ku bar ni inyi bacci ba" kamar sun ji mai yace suka fara dariya har da kwantawa jikinsa ya rungumesu gaba daya, ganin da gaske baxa su bar sa yyi baccin ba ya dau waya ya kira Khadijah, tana dagawa yace "Plss ki xo ki dau su Shureim basa son inyi bacci" Khadijah bata ce komai ba ya katse wayar, ta tabe baki ta sa Hijab ta fito ta shiga dakinsa karasawa tayi kusa da gadon suna ganinta suka kankamesa sudais yace "Meye amfanin yaranki na tsoron ki" bata tankasa ba ta kai hannu xata dau little sudais ya fasa ihu dan uwansa na taya sa suka rirrike sudais, murmushi kawai sudais yake yana kallon khadijah da ta hade rai tana kallonsu, fixgo shureim tayi ya fashe da kuka a tsorace har lkcn yaki yarda ya sake sudais. Sudais ya fixgota ita ma har ta fada kansa ya daure fuska yace "Ciwo xa ki ji masa" xata tashi ya ki saketa yana kallonta kamar yanda yaran ta ma ke kallonta, murmushi tayi ta xame kanta ta xauna kasa, murya can kasa sudais yace "Tafi basa son daukan naki" kamar sun ji abinda yace suka kara yin lamo a jikinsa, Khadijah ta mike ta nufi kofa sudais ya bi ta da kallo har ta fita sannan ya lumshe ido a hankali. A ranan da su Shureim suka cika wata goma Sudais ya sa Nanny ta shirya su kamar dai yanda ya saba duk lahadi xa su fita, yanxu kam babu inda shureim bai xuwa da kafafuwansa banda little Sudais da tashi ma wahala yake masa, kaya iri daya nanny ta sa masu as usual, kwankwasa kofar dakin Khadijah sudais yayi, tana xaune gaban madubi tana rubuta a farar takarda jin an kwankwasa kofa ta dauke takardar da sauri xata boye, dai dai nan ya bude kofar, cukuikuye papernta tayi, ya dinga kallonta yace "What's that" girgixa masa kai tayi ba tare da ta bari ta kallesa ba da sauri tace "Bakomai" yace "Uhn, sure?" Kin cewa komai tayi, yace "Toh ki shirya xan fita da twins sai ki raka mu" ta girgixa kai tace "Baxan je ba" yace "Why?" Sai a sannan ta kallesa, saurin sunkuyar da kanta tayi, ya d'an yi murmushi ya juya ya fita, bude takardar tayi tana duba abinda ta rubuta, a hankali ta linke ta boye sa sannan ta sa Hijab dinta ta fita, har ya sauka parlor da su little sudais, ya juya ya kalleta yace "Ko d'an kwalliyan ma baxa ki yi ba" tace "Ehh" ya tabe baki ya fita tare da yaran ta bi bayan su, driving yake Khadijah na back seat da twins din shi kuma yana kallonsu ta madubi, horn ya ji an yi ya juya, da mamaki yake kallon matar da ta fito daga wani gida a motar ta kafin ya tsayar da tasa motar ya bude ya fito, ita ma ta sauka tace "Aliyu dama kana Abuja?" Ya kirkiri murmushi yace "Wallahi kuwa Mama, ina yini?" Tace "Lafiya lau Aliyu" lekan bayan motarsa ta dinga yi kafin tace "Kar dai kayi aure Hajiya Khadijah bata gaya min ba naga mace da yara a mota" sosai gabansa ya fadi yace "A'a mama, matar abokina ne da yaranta" Tace "Ayyo wajen ka suka xo?" Yace "A'a ajiye su xan je in yi" shi kansa ya san he just sound stupid, yayi saurin cewa "Amma mama kun dawo ne?" Tace "Noo, na xo yin abu ne yau sati na daya, amma ina jin jibi xan koma" yace "Holland din?" Tace "In sha Allah" yace "Toh Allah kai mu mama" tace "Ameen Aliyu, Allah yayi maku albarka" yana murmushi yace "Ameen" daga haka ya koma motarsa har lkcn gabansa na faduwa, Hajiya Rukayya aminiyar Mami ce don childhood frnds ne ma, ita ce ta sa Mami tayi ma Abba magana ya siya masa gida a layin lkcn anguwar na sabo, ita ma kuma a anguwar take amma sai su yi wata da watanni basa Nigeria da yaranta, har sudais ya kai bakin titi Hajiya Rukayya bata dauke idonta a kan motarsa ba, mace da yara a motarsa kuma yace matar abokinsa, kallon gidan Sudais din tayi kafin ta karasa can da kafa, kwankwasa gate ta dinga yi ko mai gadi xai bude amma shiru, can sai ga Nanny ta fito ta bude gate din, gaisheta Nanny tayi, Hajiya Rukayya tace "Ya kike" Nanny tace "Lafiya lau sai dai Masu gidan basa nan" shiru Hajiya Rukayya tayi kafin tace "Shi da matar suka fita kenan?" Nanny tace "Ehh har da yan biyun" Hajiya Rukayya tace "Toh shkkn" daga haka ta bar wajen da sauri ta wuce gidanta tana tunanin to ko dai karya sudais yyi mata yace bai yi aure ba, tana shiga motarta ta dau waya ta shiga kiran Mami. Gaisawa Hajiya Rukayya suka yi da Mami, Mami tace "Ki ce kun dawo Nigeria kenan Hajiya" Hajiya Rukayya tace "Ina fa, just came a week ago to put things in other, ina ga xuwa jibi ma xan koma" Mami tace "Ayya, ashe baxa mu hadu ba kenan, ya yarana fa?" Hajiya Rukayya tace "Suna can, Jaheed ne dai ke Lagos" Mami tace "Toh maa sha Allah, naji dadin da kika kira wllh, kina Abuja koh?" Hajiya Rukayya tayi dariya tace "Toh ai baki sani ba, Aliyu na gani ma ya sa na kira ki yanxu" Mami tace "Haba dai..." Hajiya Rukayya tace "Wallahi kuwa ashe ya dawo gidansa, na fito gida xan je mall yanxu na gansa a mota shi ma" Mami tace "Toh, ni ban san me yasa ya koma Abuja da xama ba yanxu, sai mu yi wata ma ba mu gansa ba, idan nayi magana yace aiki" Hajiya Rukayya ta d'an yi shiru kafin tace "Amma yyi aure ne Hajiya Khadijah?" Mami tace "Ina fa, ba na gaya maki abinda yayi ma yarinyar nan da yake nema jiddah ba, da suka fisa iskanci ai mayar masa da kayansa suka yi, kinsan halin Abbansu, to in gaya maki bai taking Wani action ba sai ma cewa da yyi ai bai isa aure ba, kinga yayi supporting dinsa kenan, ni dai nasan in har yarinyar nan yaudararta yyi hakkinta baxai bar sa ba" Hajiya Rukayya tace "Ikon Allah, to ni kuma da wata na gansa da yara har biyu a mota, da na tambayesa aure yyi sai ce min yyi matar abokin sa ce ai xai maida ta gida, to mutum ba iyali me matar abokin sa taje yi gidansa, and the way he replied, gaskiya it's suspicious, to da yake kinsan ai bbu nisa tsakanin gidan nasa da namu, in gaya maki na taka da kafa har na isa gidan na kwankwasa gate sai ga wata da alamar dai yar aiki ce ta fito, da na tambayeta mai gidan sai ce min tayi ya fita da familyn sa yanxu, abun dubawa a nan shine anya Hajiya Khadijah ba aure Aliyu ya xo yyi a Abuja ba tare da sanin ku ba, yaran fa yan watanni ne" tun da ta fara xancen Mami ke saurarata baki sake, can Mami ta sauke wani ajiyar xuciya tana share xufar da ya keto mata tace "Hajiya Rukayya yaushe kika ce xa ki koma?" Hajiya Rukayya tace "Ranan talata in sha Allah" Mami tace "Toh gobe da sassafe xan taho Abujan, ina shiga xan kira ki don Allah" Hajiya Rukayya tace "A'a ke kuwa a bi komai a sannu mana, ko ni ba sai in je in samesa ba, idan ba haka xancen yake ba fa? kuma ace da gasken matar abokin sa ce, ke dai kawai ki bar komai a hannuna xan same sa da kaina sai kace ba d'a na ba Hajiya" Mami ta girgixa kai tace "Inaa ai dole ne kawai in taho Hajiya Rukayya, dama kusan shekara daya kenan da Aliyu ya canxa hali totally ya dawo kamar mara gaskiya tun bai bar Damaturu ba, kar ki ce masa komai ki jira sai na xo, idan ma haka ne idan ma ba haka bane duk xa mu sani, nagode sosai Hajiya, sai kin ji ni" daga haka Mami ta katse wayar ta mike tana jin xuciyarta na tafarfasa, mace da yara? Ina ya samo su? Wani murmushi tayi ta fita daga dakin. Shopping sudais yyi ma twins din na abubuwan da suke ci tun daga kan golden morn, biscuits, custards, quaker oats, chocolates da sweets, sai Pampers da turaren yara, ita dai Khadijah na rike da little sudais dake kuka baya son ta dauke sa sai mika ma Sudais hannu yake, shureim kuwa sai kara kankame Sudais yake wai kar Khadijah ta karbesa shi ma, Duk little sudais ya cika shopping mall din da kuka, Sudais yace "Yanxu meye amfanin haka yaron ki baya son ki daukesa Amira?" Ita dai bata ce komai ba yace "Amira, are you thinking xa mu dauwama tare ne na har abada ne? Of course no, yaran nan ne dolen ki they are now ur new world, show them love Amira" mika mata trolleyn yyi ya karbi yaron ba shiri yyi tsit yana leko uwar tasa, duk yanda sudais yyi da ita ta dauki abinda take bukata a mall din kin daukan komai tayi, ya siya masu ice cream sannan suka bar mall din, har suka koma gida Khadijah ta ki cewa komai, yana gama parking nanny ta fito ta dau yaran gaba daya ta wuce ciki, juyawa yyi ya kalli khadijah da ta bude mota xata fita yace "Wait" sannan ya fito ya shiga back seat din motar ya rufe yana kallonta, hade kai tayi gwiwa tana shesshekar kuka, ya dago kanta a hankali yace "Daga na gaya maki gaskiya Amira?" Hawaye na sakko mata cikin rawar murya tace "Toh nice nace su dinga tsoro na?" Murmushi yyi yana kallon kwayar idonta yace "Ehh mana, ai ke ce baki sonsu, kalli fa ko breast baki basu ba kin yi xaton sun manta ne" turo baki tayi ta dauke kai tace "Amma sun san na basu sau daya ai" dariya ta basa ya dinga kallonta kafin yyi murmushi, ya kamo hannunta ya lumshe ido yace "In dai kina jin maganata, and i meant a lot to you, daga yau ki fara son yaran nan Amira" sunkuyar da kanta tayi bata ce komai ba, ganin yanda yake murxa mata hannu a hankali ta kwace hannunta ta koma daya side din ta bude motar ta fita, fitowa yyi shi ma ya bi bayanta. Kasa bacci daren ranan sudais yyi ya rasa dalili, duk ya ji he is restless, bayan ya gama sallolinsa misalin karfe biyu ya bude kofar dakinsa ya fito, khadijah dake xaune daki ita ma idonta biyu ta ajiye takardar hannunta da sauri karkashin pillow tana kallon kofar dakin, jin ba a bude ba ta sauka kan gado ta dau hijab ta daura kan sleeping wear din jikinta sannan ta bude kofa ta fita, downstairs ta sauka, tsaye ta gansa tsakiyar parlorn, jin ana sakkowa stairs ya juya da sauri, har ta isa inda yake kallonta yake, yace "Why are you awake by this time" ta girgixa masa kai kawai, xaunawa yyi kan kujera ta xauna kasa kusa da shi, jin bai ce komai ba murya can kasa tace "Daxu a shopping mall kace min we are not going to be together forever, why?" Muryarta na rawa ta karashe maganar, ido ya tsura mata, hawaye ya shiga sakkowa idonta, da sauri yace "Kuka kuma, I didn't mean it Amira, abinda nake nufi shine...." Sai kuma yyi shiru, ta hade kanta da kujera tana kuka cikin raunin murya tace "Don Allah kar kace xaka bar ni watarana, I have nobody, just you, kai kadai gare ni yanxu, idan ka bar ni ya xan yi, who will take care of the boys" jikinsa yyi mugun sanyi ya sakko kasa yana kallonta ya dago kanta, cikin sanyin murya yace "Ban ce xan bar ku ba Amira, what I mean is death, kinsan rayuwar ba shi da tabbas" xaro ido tayi tana kallonsa ko kiftawa babu sai kuma ta kara fashewa da matsanancin kuka tace "Mutuwa xaka yi ka bar ni?" Dariya ta basa sosai, yace "Ni bance xan mutu ba, kuma idan mutum ya mutu ai lkcn sa ne yyi" rike hannunsa tayi hawaye na sakko mata tace "Baxa ka mutu ba until Allah is pleased with your soul in sha Allah" murmushi yayi yace "In sha Allah, kamar yanda ke ma baxa ki mutu ki bar ni da yaran ba" shiru ta yi bata ce komai ba, a hankali tace "Gwara su su mutu ai" lkci daya mood dinsa ya canxa yana kallonta, ta sunkuyar da kai, da mamaki yace "Ashe baki da hankali Amira" a hankli tace "Kayi hakuri" rasa ma abinda xai ce mata yyi, can yace "Toh tafi ki kwanta" tace "Toh kai fah" yace "Bana jin bacci" tace "Nima" hade rai yyi yace "Tashi ki tafi nace" kamar xata yi kuka tace "Kai ma ka tashi" murmushi yyi ya mike ita ma ta tashi, yana kallonta yace "to mu je" ita ta fara tafiya sannan ya bi bayanta ta jira ya shiga dakinsa sannan ita ma ta shiga, daga masa hannu ta yi, yyi murmushi ya rufe kofarsa, ita ma ta rufe nata, kwanciya yyi ya rasa tunanin da xai yi a kan Khadijah, is it that.... He love her or what" lumshe ido yyi bai son tunanin daga haka bacci ya daukesa. Da asuba tun da ya dawo masallaci gabansa ke faduwa, he don't knw why, har gari ya waye yana kwance idonsa biyu a bedroom dinsa, kamar wanda ya tuna abu ya mike xaune da sauri, jiya da yamma Hajiya Rukayya... Tunanin da ya xo masa kai knn, ya dafe kansa a xuciyarsa yace to sai ta fara gaya ma Mami ta gansa da mace da yara, noo yasan she won't, but it's better su d'an bar anguwar for sometimes, da kyar ya mike daga karshe ya fita dakin ya shiga na twins har nanny ta masu wanka tana basu golden morn suna xaune cikin kekensu, suna ganinsa suka fara daga hannu ya daukesa takwaransa har da kuka, karasawa yyi ya daukesu gaba daya yana murmushi Sanin kuka xa su yi idan ya fita ya bar su, ya koma dakinsa da su, yana son fita misalin sha daya amma yan biyun sun ki bacci, bell ya ji aka danna downstairs, sai da gabansa ya fadi duk da bai san me yasa ba, ya mike xai fita twins suka fara kuka, dawowa yyi ya daukesu ya fita, ganin khadijah bakin kofar xata bude yasa shi tsayawa kan stairs, tun da yake bai taba jin faduwar gaban da yaji a lkcn ba ganin Mami ta shigo parlorn Hajiya Rukayya na biye da ita a baya. Mami na kallon Aliyu da wani expression tace "Aliyu??? is this the life you chose for ur self? Is this the home training I gave to you" Sudais ya sauke kansa daga kallonta lkci daya jikinsa yyi sanyu ya sauko downstairs a har sannan yana rike da yaran, a hankali yace "No Mami, I didn't choose this life for my self...." Katse sa ta yi cikin tsawa tace "Aliyu ka fada min wacece yarinyar nan? Who is she? Meye hadin ka da ita?" Ya hadiye abu da kyar yace "Mami... Mami ba lallai ki yarda da abinda xan ce maki ba, but Mami ki kira Yusuf xai gaya maki wacece ita kilan shi ki yarda da shi" wani mugun kallo Mami ta dinga yi masa xuciyarta na tafarfasa tace "In kira Yusuf? saboda ina tsoron ku? To bani da wannan lkcn, Aliyu dama abinda ka dawo yi a Abuja kenan? Mace ka dauka ka ajiye gida ku ke rayuwa tare.... Wa iyaxubillah" Hajiya Rukayya tayi saurin dakatar da ita tace "Haba, ki sauraresa tukun Hajiya" daga haka ta mayar da dubanta kan sudais tace "Ka gaya mana wacece ita Aliyu" Sudais ya kalli khadijah da ta sunkuyar da kanta hawaye na sauka idonta, rasa abinda xai ce yyi duk jikinsa yyi mugun sanyi, Hajiya Rukayya tace "Toh bani number Yusuf din, ni xan kira sa" Mika masa wayarta ta yi ya amsa ya sa mata number Yusuf yana fara ring Hajiya Rukayya ta karba, Yusuf na dagawa Mami ta karbe daga hannun Hajiya Rukayya, daga daya bangaren Yusuf yayi sallama, Mami ta amsa tace "Yusuf kana ji na?" Shiru yyi jin kamar muryar Mami, a fusace tace "Ba da Yusuf nake magana ba" Yusuf ya kwalalo ido yace "Ehh ina nine mami, ina kwana," bata damu da amsa gaisuwarsa ba tace "Yusuf ka gaya min wacece yarinyar da Aliyu ya ajiye gidansa da yara" Sai da gaban Yusuf ya fadi ya mike daga xaunen da yake, can ya koma ya xauna a hankali yace "Mami it's not what u are thinking wllh yarinyar nan da kike gani taimakonta kawai Sudais yyi, she is an orphan...." Lkci daya idon Mami ya kada ta katse sa hade da kunduma masa xagi tace "An orphan??? Bata san hanyar orphanage ba ko kuma kai me yasa baka yi mata taimakon ba sai shi, ya ajiye mace da ba muharramarsa ba kace yana taimakonta Yusuf, tun da uwar ka ta haife ka ka taba jin haka?? su kuma yaran na waye?" A sanyaye Yusuf yace "Nata ne Mami" Mami na jin haka ta katse wayar tana kallon Hajiya Rukayya lkci daya idonta ya kawo ruwa tace "Kina jin halin yaran yanxu koh Rukayya, yanxu ka haifi yaro baka haifi halinsa ba, ni dama da dadewa na lura da takun Aliyu, mu Aliyu xai kunyata a idon duniya? irin tarbiyar da ni da ubansa muka yi masa kenan" durkushewa Khadijah tayi a wajen tana kuka a hankali tace "Umma kiyi hakuri don Allah ki yafe masa" Tsawa Mami tayi mata tace "Rufe min baki, tarbiyar da iyayenki kema suka maki kenan kiyi rayuwa gida daya da namiji?" Cikin rawar Murya Khadijah tace "My parent are late, bani da kowa shi yasa ya taimakeni, Umma kar ki ce ya barmu don Allah..." sudais da ya ji kafafuwansa sun gaxa daukarsa ya xauna kan kujera ya ajiye su shureim da suka wani rirrikesa, cikin sanyin murya yace "Mami don girman Allah kiyi hakuri, ba yanda kike tunani abun yake ba, I just...." Katse sa Mami tayi cike da takaice tace "Ba yanda nake tunani abun yake ba Aliyu?" Sudais ya daga kai da kyar yana kallonta ganin hawayen dake idon mahaifiyarsa ya ajiye yaran ya mike ya isa gabanta ya durkusa cikin rawar murya yace "Noo Mami pls kar ki xubar da hawayen ki a kai na, na maki alkawarin na daina duk abinda nake daga yau, ki gafarce ni don Allah mamina" duk ya rikice mata, Mami na hawaye tace "Ni idan na gafarce ka Allahn ka fa? Wani tsinannen taimako ne wannan without the consent of ur parent, wani taimako ne wannan kuna rayuwa gida daya kamar mata da miji, yanxu ba don na san halin ka ba ance maka baxan yarda yaranka bane wa enan yaran?" Idonsa ya kada sosai cikin raunin murya yace "Mami nayi abinda nayi ne domin taimako amma daga yanxu na bari in sha Allah, forgive me plss Mami, nasan ban kyauta maku ba" Mami tace "Ka hada ina ka ina ka ka koma Damaturu yau ba sai gobe ba, sannan ina jiran makullin gidan yanxu ka same ni gidan Hajiya Rukayya" Tana fadin haka ta juya ta fita a parlon, kai kana gani kasan tana mugun son d'an nata ne, Hajiya Rukayya tace "Heed to what ur mother said right away Aliyu, ita kuma idan tace bata da iyaye ai baxa ta rasa dangi ba ta tafi wajensu" shi dai sudais bai ce komai ba, Hajiya Rukayya ta juya ita ma ta fita, Sudais ya dafe kansa da yyi masa nauyi, gaba daya tunaninsa ya dagule ga kukan Khadijah da yake ji har ransa, su kansu yan biyun kuka suke, lkci daya idanuwansa suka kada, mikewa yyi daga durkushen da yake ya wuce dakinsa ya dau makullin mota ya fita gidan gaba daya, Nanny da duk taji abin da ya faru ta iso gun khadijah dake kuka sosai ta dafa ta a hankali tace "Dama ba mijin ki bane mutumin nan maman twins?" Khadijah ta dago tana kallonta hawaye na sakko mata ta girgixa mata kai tace "Taimako na kawai yayi tun ban haifi yaran nan ba, ni bani da kowa sai shi yanxu" Hawaye ne ya cika idon Nanny tace "Dangin ku fa?" Cikin rawar murya Khadijah tace "Ban san dangin Mahaifiya ta ba, dangin Abbana kuma baxa su karbe ni ba, Ummata kuma ta tafi ta bar ban san inda xan ganta ba" tana kai wa nan ta fashe da matsanancin kuka tace "Ni yanxu ban san ya xan yi da yaran ba" kuka sosai Nanny take duk jikinta yyi sanyi ba kadan ba, ta jawo ta jiki cikin sanyin murya tace "Kiyi hakuri wataran sai labari Allah baxai hanaki yanda xa kiyi ba, kar ki sake kuka don Allah" mikewa Nanny tayi ta tafi gun su Shureim dake ta kuka wai Sudais ya fita ya bar su. Bayan awanni kusan uku Nanny ta gaji da lallashin Khadijah da ta ki hakura da kukan da take, xuwa lkcn kuma su Shureim sun yi bacci, Da kyar Nanny ta lallaba ta taje tayi sllh don duk a sanyaye take, tana xaune kan darduma Sudais ya shigo gidan, kallonsa Khadijah ta dinga yi har ya xauna kan kujera, a sanyaye ta taso ta durkusa gefensa tace "Am sorry I caused you all this, kayi hakuri don Allah ka yafe min" Tana magana hawaye ce idonta, ya kirkiri murmushi yace "It's nothing Amira, tafi ki hada kayan ki gaba daya a sama" shiru ta yi tana kallonsa gabanta na faduwa, ya gyada mata kai cike da assurance, tashi tayi jiki ba kwari ta wuce sama, ya kalli Nanny da ke parlorn ita ma duk a sanyaye yace "Ki hada kayan yaran da naki gaba daya" mikewa tayi ta wuce sama ita ma, Nanny ce ta fara sakkowa parlorn da jakunkunan kayan su shureim, Sudais dake kallonta yace "Ki kai cikin booth, its open" fita tayi waje da kayan, tana dawowa yace ta je ta taya khadijah, Kuka Nanny ta samu Khadijah nayi a dakin, bata iya tace mata komai ba ta shiga taya ta hada kayanta, Nanny ce ta sauko da jakan ta kai cikin motar, shi dai Sudais na xaune yyi nisa tunanin da yake, jin wayarsa na ring ya dauka da sauri yana kallon mai kiran, tashi yyi ya daga wayar yace "Mukhtar ka iso ne" daga daya bangaren abokin nasa yace "Ehh ina waje" fita yyi ya samesa waje, Mukhtar yace "You mean wannan gidan xaka siyar Barrister?" Sudais ya shafa kansa yace "Ehh shi" Mukhtar yace "Haba, Toh ai wannan yafi wancan wllh, ya xaka siyar da abu ka siya wanda bai kai sa ba kuma har da ciko, amma sun ma same ka da yawa" Sudais yace "kai dai bani takardun wancan gidan, and don't forget gidan is almost furnished" Barrister Mukhtar ya bude motarsa ya fiddo envelope ya mika ma Sudais ya karba yace "Duk da haka dai, duka duka kayan nawa ne a ciki" Sudais ya amsa envelope din yace "Nagode, bari in dauko nawa" daga haka ya koma ciki ya wuce bedroom dinsa ya dauko wani envelope dake dauke da takardun gidan nasa yana dawowa ya mika ma colleague dinsa yace "Kafin dare xa a kwashe komai na nan din, soo you help me explain to them" Mukhtar da mamakin Sudais ya cika sa ya karbi envelope din yace "Toh shkkn" daga haka suka yi sallama Mukhtar ya wuce, Sudais na komawa ciki ya sa Nanny ta dauko twins suka shiga mota, Ganin Khadijah bata fito sudais ya wuce sama ya bude kofar dakin duk da kukan da ya sameta tana yi kawai cewa yayi "Ke nake jira Amira" daga haka ya juya ya fita, Khadijah ta mike tana goge hawayen da ya ki tsaya mata ta fita, a gaban motar ta xauna Nanny kuma na xaune da yaran a baya suka bar gidan bayan Sudais ya sauka ya rufe gate, tafiyar kusan minti ashirin suka yi sai kallon agogo sudais yake har suka iso wani anguwa, anguwa ce mai kyau shi ma kamar wancan, yyi parking dai dai gate din wani bungalow babba ya fita ya bude gate din ya ja motar suka shiga gidan, sosai gidan ya hadu bayan yyi parking ya bude motar ya fito yana kallon Nanny yace ta fito da yaran da xuwa lkcn sun tashi daga baccin da suke, kallon khadijah yyi ta bude motar ita ma ta fito, Sudais ya nufi entrance din shiga gidan ya bude kofar da makullin dake cikin envelope sannan ya shiga, parlorn na da girma amma bai kai na can gidan sudais ba, sannan dakuna uku ne ko wanne da bayi sai kitchen da dinning area, da kuma bathroom da toilet a parlorn, gidan ya hadu, sai dai fa bai kai na sudais ba, Har TV akwai a parlorn bayan kujeru da center table da dinning table da chairs a area din da aka tanadar don ajiye su, kasa xama khadijah tayi a parlorn, Sudais dake tsaye shi ma ya nuna mata kujera ta xauna, sai a sannan ta xauna cikin sanyin jiki, ya dau little sudais dake ta daga masa hannu wai ya daukesa, Sudais na kallon Nanny murya can kasa yace "Madam ina son ki min alfarma daya na xaunawa tare da su even if it's just for few years to come for the sake of this twins, I will pay all the money in sha Allah" Nanny da jikinta yyi sanyi tace "Ba damuwa yallabai, Allah ya saka da alkhairi" Nan take sudais ya bata check na shekarun da ya fada, sannan ya nufi Khadijah yana kallonta ya ajiye mata envelope din hannunsa a kafarta a hankali yace "Gashi Amira this is for my boys, da sunansu na siya gidan nan don haka na su ne, mallakin su ne" kasa cewa komai tayi tana kallonsa, ya durkusa gabanta a raunane yace "I have always wanted the very best for you Amira, like... sending you out to UK kiyi karatu ki xama likita, a ko da yaushe hakan yana rai na amma saboda kananun yaran ki.... I decided sai sun kai ko da shekaru biyu ne sai ki tafi tare da su.... Am sad I couldn't fulfill that but you can ur self, promise me ko bayan babu ni, xa kiyi karatu ki xama babban likita, I mean ki min alkawarin xa ki cika min wannan burin nawa a kan ki" jin bata ce komai sai kallonsa take a tsorace ya kamo hannunta yana kallon kwayar idonta, he understand she's shock, ya lumshe ido ya mika mata check na kudi, da farko kasa magana yyi can yyi gathering courage with a breaking voice yace "Am going Amira, this is a check of 20 million, I think that all I've got for now, kiyi kokarin ganin with this little am giving you kin inganta rayuwar ki da na boys din ki, sannan ki ci gaba da rike mutuncin ki na 'ya mace duk inda xa ki samu kan ki, I wish na yi kokarin nema maki Umman ki kafin in tafi, I wish na kwato maki hakkin ki a gun dangin mahaifin ki, amma duk hakan bai yiwu ba Amira, ki kyale su xa su mayar maki a lahira idan Allah ya yarda, as for the twins.." Kasa ci gaba yyi, yyi shiru na wani lkci bai son ta ga hawayen idonsa, can yyi karfin halin cewa "I knw i will always love them tamkar yaran da na haifa a cikina, kar ki bari su yi rashi na Amira, ki dinga masu abinda nake masu, I mean ki so su kamar yanda nake son su, you are all they've got now, ke kadai gare su, idan kuma kika samu abokin rayuwar da kika ga ya kwanta maki kiyi aure amma ki fara sanar da shi ke wacece, a duk xaman mu Amira idan na taba saba maki da sani na ko akasin haka ki gafarce ni" kansa a kasa yace "I think that's all, akwai foodstuffs da na siyo daxu a kitchen, goodbye Amira, it's great knowing you in my life, wishing u better future ahead...." Ganin xai tashi Khadijah ta sakko kasa ta rikesa ta fashe da matsanancin kuka cikin rawar murya tace "Na shiga uku, don Allah kar ka tafi ka bar ni ni kadai, you are all I have with my kids, ka ce min fa baxa ka taba barina ba, don girman Allah kar ka min haka Aliyu, idan ka tafi ya xan yi..." Kasa kallonta yyi, ta daura kanta a kafarsa tana kuka sosai cikin raunin murya tace "Kasan ni marainiya ce, I don't have anybody, ya xan yi da yaran idan ka tafi ka bar ni da su Aliyu, don Allah kar ka tafi ko don su, ban san inda xan ga ummata ba kar ka tafi ka bar ni ni kadai a duniyar nan" Hakan da khadijah ta fada yasa Nanny ta fara kuka tausayin khadijah da yan biyun ya cika ta, Sudais yyi iya kokarin ganin hawayen idonsa bai sakko ba amma hakan bai yiwu ba, ya dago ta da kyar shi ma hawaye na xubo masa yace "Life goes on with or without me Amira xaku yi rayuwarku da yaran, you just have to manage the little I gave you cos I knw living in Abuja is expensive, surely watarana xa ki hadu da ummanki har ma da dangin mahaifiyar ki, I have to go now saboda Mamina, baxan iya tsallake maganar ta ba kiyi hakuri, ke dai kiyi min alfarmar kula da yan biyun ki, kuma ki daina jin haushinsu ki ja su a jiki, su kenan gare ki a yanxu, kar ki shafa masu laifin mahaifin su" daga haka ya mike ya isa gun twins din ya duka yana kallonsu a sanyaye, dariya suka fara masa suna daga hannu ya daukesu, ya manna masu kiss gaba daya ya lumshe ido murya can kasa yace "Long life to you both in sha Allah my boys, Allah ya albarkace rayuwarku ku xamto *hasken rayuwar* mahaifiyar ku" tashi yyi ya nufi kofa trying hard to control his self, Khadijah na kuka sosai cikin sanyin murya tace "Thanks very much Aliyu, Allah ya biya ka abinda kayi mana, and I will always pray for you in my life, kai din ka xame min _hasken rayuwa_ a lkcn da rayuwata tayi min duhu, daga ranan da na fara ganin ka ka yaye min bakin cikin dake tare da ni, you will always be the *light of my life* Aliyu" Sudais bai iya ya juyo ba har ya isa kofa, yaran na ganin xai fita suka fara kuka, bai yarda ya juyo ba har ya bude kofar ya fita yana goge hawayen idonsa, yana fita kuma ya bude wayarsa ya cire sim din da Khadijah ta san sa da shi ya jefar nan cikin flowers din gidan ya fita ya hau motarsa, and that was how Barrister Aliyu left Khadijah and her twins. Khadijah ta shiga hali na damuwa sosai bayan tafiyar sudais, bata da aiki sai na tunani da xubda hawaye bata taba xaton rabuwa da Sudais a lkcn ba, da ba don Nanny dake gidan tana kwantar mata da hankali ba da abun ya mata yawa, gani take kamar sudais xai dawo kullum jiran tsammani take amma shiru wasa wasa har sati biyu, ta rame ba kadan gashi kullum cikin jin ciwo take a kirjinta, ciwon da ta fi shekara bata ji sa ba sai gashi ya dawo mata da karfinsa, hakan yasa Nanny ta tilastata suka shirya suka tafi asibiti don ko baccin kirki bata iya yi da daddare, khadijah bata yi mamakin abinda likita yace game da ciwon da take yawan ji a kirji ba, at anytime xata iya kamuwa da ciwon xuciya, yini biyu tayi asibitin under medication, nanny tayi ta kai kawo da twins xuwa asibitin, da yamma likitan ya sallamesu ya kuma bata shawarari da dama kan abinda ke janyo ciwonta da yanda xata yi preventing tashin ciwon, A hanyarsu ta dawowa cikin Napep da damuwa Nanny tace "Yanxu Mum twins da kike sa ma kanki damuwa haka idan abu ya same ki yaran ki fa? Ko don su baxa ki hakura ki rufa masu asiri ki kwantar da hankalin ki ki rungumi kaddara ba, kar fa ki manta ko wani bawa da irin tasa kaddarar, so why not just accept urs a yanda ya xo maki" Khadijah ta goge hawayen dake xuba idonta a hankali tace "Ban san ya xan yi ba" Nanny ta kwantar da murya tace "Cire komai xa ki yi a ran ki, kiyi facing sabuwar rayuwar da xa ki fara da yaran ki, bawan Allahn nan ya tafi, ya kuma ya maki duk abinda ya kamata kafin ya tafi yanxu the ball is in ur court, sai kiyi abinda ya kamata ki kuma rike addu'a sai komai ya xo maki da sauki, as a mother nake baki shawara Khadijah... For the sake of ur boys ki yi hakuri ki cire ma kan ki damuwa don Allah" a hankali khadijah tace "Toh nagode sosai" suna isa gida Khadijah ta sauka ta ba mai adai daitan kudi, xata karbi shureim hannun Nanny ya makalkaleta ya ki yarda, jikinta yyi sanyi tana kallon yaron, Nanny tayi murmushi ta fito da duk yaran biyu, khadijah ta karasa ta bude gate din sannan suka shiga gidan, ba laifi ta dau shawarar Nanny ganin shi kadai ne mafita a gareta sai dai hakan bai sa fara'arta ya dawo ba, she is always sad, bata taba xaton Sudais xai bar ta so early a rayuwa ba, kusan kullum sai ta yi tunaninsa, magungunan da take sha ya taimaka ya rage mata ciwon xuciyar da take fama da shi duk da baya tasar mata ma sai da daddare taji kamar xata mutu, ba karamin kokari take yi na ganin ta ja su little sudais a jiki ba amma sun ki yarda ko da yaushe cikin gudun ta suke kamar dodo, hakan na kara sa ta shiga damuwa Nanny ta dinga nuna mata a hankali xa su sake da ita kar ta damu, a ranan da yaran suka cika shekara daya a duniya Nanny ta raka Khadijah tayi enrolling kanta a ss1 na wani makaranta dake nan anguwar ta su, idan ba ita ta gaya maka tana da yara har biyu a gida ba in xa a shekara ana gaya maka baxa ka yarda ba, a lkcn kuma shekarunta sha bakwai a duniya, kana ganinta kasan she is a teenager, a hankali khadijah ta fara kokarin yakice tunanin sudais a ranta domin tayi concentrating a karatun ta, idan ta fita tun safe sai hudu take dawowa gida, sannan ga islamiyyar da ta shiga na yamma, hakan yasa still babu wani interaction tsakaninta da yaranta tun da ba xaman gidan take ba, amma har ga Allah yanxu ji tayi tana son abun ta duk da tsoronta da suke ji har lkcn. Haka rayuwa ta ci gaba da kasance ma khadijah har ta gama ss1 lafiya, xuwa lkcn abu uku ne ke damunta a xuciya, Rashin Ummanta, gudun ta da yaranta suke sai kuma ciwon xuciyar da ya sa ta gaba abu kamar wasa kusan ko da yaushe hanyar asibiti take wanda hakan ke sa ta fashin makaranta don ma tana da kokari, Sudais kam ta rufe sa a babin rayuwarta sai dai duk sllh sai tayi masa addu'ar Allah ya saka masa da alkhairi abinda yyi mata a rayuwarta da yaranta. Yau lahadi suna parlor, Nanny na feeding Sudais da shureim da yanxu shekarun su biyu da yan watanni a duniya indomie ta dafa masu take basu, yaran sun yi wayo sosai babu inda basa xuwa sai dai fa da ka gansu kaga Aliyu barin sudais komai na Abban nasa ya dauko, sau da yawa sai Khadijah tayi ta kallonsu, wani lkcn tayi murmushin takaici, wani lkcn kuma tayi hamdala ga Allah da ya bata yan biyun, Nanny ce ta katse shirun dake tsakaninsu tace "Mum twins to ya xa ayi da cefanen, wa enan ba yarda xa su yi in tafi in bar su ba, kuma wahala kawai xa mu je mu sha idan muka tafi gaba daya" Khadijah ta ajiye novel din hannunta tace "Nanny kawai da wayo xa ki tafi ki bar su" a tare yaron suka kalleta, Nanny ta kyalkyale da dariya tace "Toh ai kin tona, wa yace maki basa ji, sarai sun ji abinda kika ce" murmushi khadijah tayi tana mamakin sharpness din twins din, tuni shureim ya kara matsawa kusa da nanny, Khadijah ta tabe baki tace "Toh bari ni in je" Hijab har kasa ta daura kan kayan jikinta sannan ta dau kudin ta yi ma Nanny sallama tana daga ma boys din hannu ta nufi kofar fita su ma suna daga mata, jikinta yyi sanyi ganin in dai uwa xata fita yaranta sun dingi kuka kenan xa su bi ta, but why is her own case different, ko a jikin yan biyun dake cin Indomie da nanny ke basu har ta fita, to ita bata san kuma ya xata yi yaran nan su saki jiki da ita ba, iyakar kokari tana kokarin kwatanta masu abinda sudais yace Kafin ya bar su amma sun ki sakewa da ita, tana tsaye bakin titi tana jiran abun hawa a ranta kuwa tunani take ko dai abinda sudais ya fada kan nonon da bata basu ba gaskiya ne, kenan haushin ta suke ji? Ji tayi da ma basu girma ba ta basu nonon yanxu, tsabar yanda jikinta yyi sanyi bata lura da motar da har ya wuce ta da farko ya fara reverse a hankali yana dawowa ba, tana ankarewa ta dauke kai da sauri hade da tsuke fuska don hakan ma yasa bata son fita, tana mamaki da jin haushin me yasa in dai xata fita sai an tsayar da ita, ita ba wannan ne gabanta ba kuma bata jin xuciyarta xai kara kula wani d'a namiji har ta bar duniya, ganin mai motar ya fito daga motarsa ta bar wajen da sauri tana tafiya fuska daure ba tare da ta damu ta kallesa ba, ji tayi ance "Khadijah?" ta juyo da sauri suka yi ido hudu da shi, ya dinga kallonta kamar me son kara tabbatar da ita ce ko ba ita bace, ita din ma kallonsa take da mamaki, yace "Baki gane ni ba Khadijah?" Jikinta yyi sanyi lkci daya tayi murmushin da ya bayyana fararen hakoranta tace "Na gane ka, am just trying to be sure ko kai ne ko ba kai bane" ya wara yace "Maa sha Allah, Imagine we met after 3 good years" murmushi ta kuma yi tana kara kallonsa da kyau ganin yyi mata tsayi fiye da yanda ta san sa a da tace "Sure, to ya bayan rabuwa" ya rike chin dinsa yace "Waow kin girma Khadijah, just look at how calm you are now, kin tuna lkcn da kike yawo ba Hijab da jikakken kaya?" dariya ya bata ta rufe fuska tace "Har da tsokana" yace "Am serious, a Abuja dama ku ke?" Tace "Ehh wllh, ya su mama fa" yace "Suna kt, nima ban dade da fara aiki a nan ba, just 7 months back" Khadijah tace "Allah sarki, toh Allah ya taimaka" d'an shiru yyi yana kallonta, kafin a hankali yace "Ko kin yi aure ne Khadijah?" Kallonsa ta tsaya yi ita ma, lkci daya ta samu kanta da girgixa masa kai tace "Aure kuma, A'a ina karatu ne" yyi murmushi yace "That's good, kar in tsaya ina ta tsurutu da matar aure ban sani ba" murmushi kawai khadijah tayi a xuciyarta kuwa mamakin yanda aka yi ya fara magana ta yi don a lkcn da ta san shi da wuya yake magana sai dai danna waya, lkci daya jikinta yyi sanyi tuna abinda yyi mata a lkcn da take walagigi a katsina cikin yunwa, muryarsa ya katse ta yace "Ina xaki yanxu?" Ta kallesa tace "Kasuwa" yace "Toh shiga in yi dropping din ki" d'an xaro ido tayi tace "Kai da ba d'an gari ba?" Yace "Wata na 7 kice min ba d'an gari ba" murmushi tayi tace "Toh naji kai d'an gari ne" yace "Toh shiga muje" motar ta bude tana murmushi ta shiga, ya xaga ya shiga maxaunin driver suka bar wajen, yana driving yace "So ya rice and stew, and Irish with egg? Kuna nan kuna damawa koh?" Dariya sosai Khadijah tayi ta rufe fuska, yana murmushi yace "Yarinyar nan ta kashe min kudi a lkcn da abincin yan gayu gashi sai Abba ya bani nima lkcn" Khadijah ta dago a hankali tana kallonsa tana murmushi tace "Ae yanxu babu abinda bana ci har tuwo da miyar kuka, da ma kunu da kosai" ya wara ido yace "Da gaske? Anya xan yarda kuwa" ta gyada masa kai tace "Serious..." yace "Hmm that's surprising amma" ta turo baki tace "Baka yarda ba kenan?" yace "Toh ai ban ce komai ba Khadijah" suna isa kasuwa bbu yanda Khadijah bata yi da shi ya tafi ba yace xai jira ta, bbu yanda ta iya haka ta siya abubuwan da tasan xa su bukata a lkcn daga baya sai ta dawo ta siya sauran don bata son ta bar sa yyi ta jiranta, yana parking kofar gidan da ta nuna masa yace "Nan ne gidanku?" Ta gyada masa kai ta bude motar ta fita, yace "Toh ki gayar min da su mama da mutan gida" a sanyaye tana kallonsa tace "Xa su ji nagode sosai" daga haka ta juya xata shiga gate, yace "Wait Khadijah baki ban number ki ba mu dinga xumunci" dawowa tayi ta kira masa numberta yayi saving yana kallonta yace "It's nyc meeting you once more Khadijah" ta kirkiri murmushi ta daga masa hannu ta shiga cikin gida, Nanny na kitchen su sudais kadai ne xaune parlorn ta sa masu cartoon, khadijah ta ajiye ledan hannunta ta isa kusa da su ta xauna tana kallonsu, su ma kallonta suke, ta yi murmushi ganin irin kallon da suke mata ta yi masu kiss gaba daya, Sudais ya goge bakinsa shureim na ganin haka shi ma ya goge nasa, jikinta yyi sanyi sosai tana kallonsu, bata san lkcn da hawaye ya kawo idonta ba ta mike ta wuce daki da sauri, Nanny ce ta shigo dakin ganin khadijah kan gado tana hawaye da mamaki ta karaso da sauri tace "Mum twins me ya faru kuma?" Cikin rawar murya tace "Wai don na masu kiss shine suke goge bakinsu" dariya sosai Nanny tayi kafin tace "kai Khadijah shine har da kuka, to kyalesu xan yi maganinsu" daga haka Nanny ta juya ta koma parlor, taso keyar boys din tayi suka taho dakin, kusa da khadijah ta ajiye su duk suka shiga kkrin sauka daga kan gadon Nanny ta daure fuska tace "C'mon, duk wanda ya sakko xan xane sa, ita ce uwar ku ba ni ba" Kuka suka fara yi kuma basu sauka kan gadon ba, Nanny na kallon khadijah dake ta kallon kyawawan yaran nata tace "Yanxu abinda xa mu yi shine xa su dawo kwana nan dakin, ke xaki dinga masu wanka ki shirya su, ke xaki dinga ba su abinci hakan kadai xai sa su saki jiki da ke" a hankali khadijah tace "Toh" Nanny tace "Don haka duk safe kafin ki tafi school sai kin masu wanka kin shirya su ni kuma in hada masu breakfast sai in baki ki basu" kai kawai Khadijah ta gyada don har ga Allah bata son gudun ta da yaran suke, haka Nanny ta fita ta bar su suna kuka xa su bi ta, amma da yake suna jin magana bbu wanda ya sauka daga kan gadon kamar yanda tace masu, suka gama kukansu suka yi shiru suna kallon khadijah, Sudais yyi tapping dinta yana nuna mata kofa yace "Nanny..." Murmushi Khadijah tayi ta jawo sa jiki tace "Nima Nanny ce ai" hakura yaran suka yi suna ta xaune dakin kusa da ita har bacci ya dauke su, Nanny na ganin lkcn tashin su ya kusa misalin karfe biyar na yamma ta dama masu custard ta dafa masu indomie ta kawo ma khadijah dakin ta fita ta rufe masu kofa, a lkcn kuma suka tashi, duk suka yi jigum suna kallon khadijah, ruwan wanka ta hada a bathroom dinta tayi masu gaba daya sannan ta fito ta shafa masu mansu dake dakin ta sa masu singlet da pant ta xaunar da su kan carpet ta shiga basu custard din suna karba, har ranta ta ji dadin hakan suna gama sha kuma ta fara basu indomie da egg din, shureim na koshi ya fiddo wanda ta sa mashi a baki ya mike ya kai mata bakinta, murmushi tayi ta bude bakinta ya xuba mata abincin ta shiga ci a hankali. Sai kusan karfe shidda Khadijah ta fito parlor da yan biyun nata, cartoon ta sa masu parlorn duk suka xauna kan kujera suna kallo basu bi ta kan Nanny ba, da daddare a kan gadon ta ta shimfide su bayan sun yi bacci, ta gama shirin kwanciya kenan ita ma wayarta ya fara ring, ita dai bbu mai kiranta a waya ban da Nanny sai wata classmate dinta Aisha dake sonta sosai, ta dinga kallon number kafin ta daga, sallama yyi mata jin muryar hankalin ta ya dan kwanta sai dai bata san dalilin kiran ba ta amsa masa sallamar ta gaishesa yace "Ko kin fara bacci ne?" Ta girgixa kai tace "A'a yanxu dai xan yi" yace "Ohk, ya mutan gidan?" Tace "Lafiya lau Alhmdllh" yace "Maa sha Allah" shiru ta yi bata ce komai ba, a hankali yace "Kawai sai kika bar garinmu ba sallama Khadijah" tayi murmushin karfin hali tace "Ummata ce ta xo ta dauke ni ai" yace "Allah sarki, but dama me ya kawo ki gidan tun farko" khadijah da taji kamar kar tace komai kawai ta yi murmushin takaici tace "Ai yayan Abbana ne" yace "Are you serious?" Tace "Uhn" yace "Waow, to me yasa basu baki abinci" ta wara ido tace "Suna bani fa, ni ce ban iya cin abincin ba lokacin" murmushi yyi yace "Allah sarki, kwanaki ma ai kawun naki yyi accident kin sani koh" Khadijah ta bude ido sosai tace "Haba dai, ban sani ba, basu gaya mana ba" Sadeeq yace "Ehh amma da sauki yanxu ina jin ya samu lafiya ma" A hankali khadijah tace "Toh Allah ya kara kiyayewa" yace "Ameen" shiru ne ya biyo baya kafin yace "Kin taba ba Umma labarina" Khadijah da taji jikinta yyi mugun sanyi a hankali tace "Kowa ma ina ba labarin ka, cos you fed me when I was in need of food" Sadeeq yace "Noo I did that for the sake of Allah, not for you to tell everyone" murmushi kawai khadijah tayi a sanyaye, shi ma murmushin yake yace "Sure, yaushe xa ki hada ni da Umma mu gaisa ko kuma in xo har gida in gaisheta, ko baki son mu yi xumunci sosai?" gabanta ne yyi mugun faduwa and she was totally lost of words, a hankali yace "Hello, Khadijah are you there?"