NOOR AL HAYAT 31-40

Girgixa kai Sudais yyi bayan ya dauke idonsa daga kallon da yyi ta ma Yusuf yace “I didn’t blame you Dr, why?? Because am very sure kafin ka xo gidanmu yanxu daga club din da ka saba xuwa kake, and definitely idan ka je club dole sai ka sha ruwan can na sani, soo no offense, u are drunk….” Dariya kawai Yusuf yake yace “Kai kuma tun bayan haduwarka da marainiyar nan ka daina xuwa can koh? Thank God we where both drunkards before” Sudais da yyi mugun hade rai yace “Drop me here my frnd” Yusuf yyi parking yace “Ji dan iska kamar wani driver din sa wai drop me here my frnd” Bude motar Sudais yyi ya fice ya juya yana masa wani kallo, da yatsarsa yyi masa xagin turawa yayi wucewarsa, dariya kawai Yusuf yake ya ja motarsa ya wuce gida, Da kafa Sudais ya karasa gidansa, Mama suwaiba kadai ce parlor tana cin abinci TV a kunne, tana ganinsa ta mike da sauri tana masa sannu da xuwa yace “A’a yi xaman ki mama” Mama suwaiba ta koma ta xauna tace “Toh nagode” yana son tambayarta khadijah amma yyi shiru, can ya mike ya wuce bedroom, kwance ya ganta tayi bacci tana rufe da bargo, ya karasa kusa da gadon yana kallonta, dukawa yyi dai dai fuskarta murya can kasa yace “So early?” Ko motsi bata yi ba alamar ta jima da yin baccin, a hankali yyi murmushi ya kai hannu dogon hancinta ko mai ya tuna yyi saurin withdrawing din hannunsa ya mike ya kashe mata wuta ya fita daga dakin, Sallama yyi ma Mama suwaiba ya nufi kofa ta bi sa da kallon mamaki, yau ma da ya dawo baxai kwana gidansa tare da matarsa ba, wannan wani irin aure ne a gantale, har ya rufe kofa kallonsa take baki sake. Washegari lahadu Khadijah na xaune parlor da tuwo da miyar kuka da mama suwaiba tayi mata, da cokali take cin tuwon mama suwaiba kuma na kitchen tana wanke wanke, bude kofa aka yi ta daga kai da sauri sudais ya shigo parlorn rike da babban jaka, ajiye jakar yyi yana wara ido yace “Kaiiii yanxu xa ki iya cinye wannan tuwon Amira?” Rufe fuskarta tayi da kujera da sauri tace “A’a fa xan rage in ci anjima” dariya yyi ya juya ya fita ya shigo da daya jakar ya ajiye sannan ya xauna kan lallausan carpet da take xaune yace “Ci da yawa abin ki kin ji, sai ki haifo mana yara masu karfi” bata dago kanta ba har lkcn yyi murmushi ya bude zip din jakar ya fara fiddo kayan ciki, sai bayan da ya Ciro kayan jakunkunan gaba daya sannan yace “Here… you like them?” sai a sannan khadijah ta dago a hankali tana kallon kayan, kayan babies ne masu tsada ko wanne set biyu, shiru ta yi tana kallon kayan, ya ware nata dogayen riguna masu kyau gudu hudu yace “Wannan kuma naki” sauke idonta da ya kawo ruwa tayi a hankali, ya hade rai yace “Baki so ne xa ki min kuka” bata san lkcn da ta fashe da kuka ba ta hade kanta da kujera, yyi shiru yana kallonta, can ya fara mayar da kayan gaba daya jaka yana gamawa ya kai jakunkunan daki sannan ya nufi kofa ya fice daga gidan ya shiga motarsa ya wuce. Har bayan kwana biyu Sudais bai je gidan ba duk da he is just trying not to go amma hankalinsa gaba daya na can, sosai hankalin khadijah ya tashi don tasan kilan fushi yake ne ya sa, tana son kiransa amma ta kasa, ganin baxata iya jurewa ba kuma ta kira sa, a lokacin yana gida bedroom din Mami suna hira da Anty Maryam, ganin kiran yyi ta kallon screen din kafin yyi silencing wayar ya mike yace “Mami bari in tafi in shirya xan fita yanxu” daga haka ya bar dakin bayan yayi ma Anty Maryam ma sallama, Mami ta tabe baki tace “Kwata kwata Aliyu ba shi da gaskiya yanxu, I really don’t knw what he is up to, tun ma kafin ya bar kasar months back na lura da haka kuma gashi ya dawo ya ci gaba da behavior din, there is something big he is hiding kuma shi ya hanasa auren ma, dubi fa yanda ya axalxalemu a kan jiddah duk ya daga mana hankali shi aure amma lkci daya kinga kuma abinda yyi, ni na haifesa ba shi ya haifeni ba don hka I will fish out what he is up to soon” ita dai Anty Maryam bata ce komai ba sai kallon yayarta take. Sudais na barin gidan ya tafi can gidansa, Khadijah na kitchen tare da Mama suwaiba suka ji an shigo parlorn, fitowa tayi tana ganinsa ta turo baki, ya karaso parlorn ya xauna yana idonsa a kanta, ta sunkuyar da kai ta isa kusa da shi ta xauna a kasa, yace “How are you?” Kin cewa komai tayi, ya d’an yi murmushi ya dau wayarsa yana danna, a hankali tace “Ina yini” ya kalleta yace “Ban yini ba” kamar xata yi kuka tace “Ni ban san me nayi maka ba” yace “Na kawo maki abu kince baki so mana” xaro ido tayi tana kallonsa tace “Ni??” Yace “Ehh” murmushi tayi tace “I don’t knw how to thank you that day, that was why….” Hawaye cike idonta ta kare maganar, Kallonta kawai yake bai ce komai ba. Haka nan rayuwa ya ci gaba da kasancewa bayan dawowar sudais Nigeria, duk safiya, rana har da daddare xai xo ganin khadijah, kayan ciye ciye yake xuwa mata shi idan xai xo da daddare wani lkcn shi ma ya ci abinda xai ci a gidan, ita dai Mama suwaiba na son sanin me ya janyo bai kwana gidan amma bata san wa xa ta tambaya ba tunda ba wani hira can suke yi da Khadijah ba, toh ko don tana da ciki ne yake haka, tambayar da ta dinga yi ma kanta kenan har hakan yasa ta d’an fara jin haushin sudais din, rana daddaya ne xai shigo gidan ba tare da kayan baby ba, xuwa yanxu irin siyayyar kayan baby da yyi mata sai ayi xaton yara goma xata haifa, komai ya gani ya Burgesa sai ya daukar mata. A haka har watan haihuwar Khadijah ya tsaya, mama suwaiba bata yi kasa a gwiwa ba wajen bata taimako irin na gargajiya don tausayi take bata, kusan duk yamma sudais sai ya lallaba Yusuf sun je gidan kawai don ya dubata, har ransa yake fargabar kar abu ya sameta, wani sanyi tayi gaba daya a kwanakin ko da yaushe a kwance xaka ganta, idan ya tambayeta ko akwai inda ke mata ciwo sai tace babu ko ina. Ranan Sunday da sassafe ya shirya ya fito parlor yana kallon Mami dake dinning yace “Mami xan fita in dawo” tace “Ranan lahadin ma?” Murmushi yayi yace “Mami it’s urgent ne, kuma akan…” Katse sa tayi tace “Aliyu” ya dago da sauri, bata fuska yayi yace “Mami wllh duk kika ce min Aliyu sai gabana ya fadi, cos u always call that name when serious” ta masa wani kallo tace “Toh da meye sunan naka?” Yar dariya yyi yace “Sudais mana” tace “Ni na sa maka sudais?” Dariya yyi sosai yace “Ni na sa ma kaina Mami Aliyun sunan tsoffi ne I….” Ta katse sa tace “What ever…. kaje duk inda xaka ka dawo ka sameni in sha Allah gobe xa a kai kayan can da kasa nayi jere da su a daki” yace “Allah ya kai mu Mami” daga haka ya fice daga parlorn, gidansa ya nufa direct. Mama suwaiba na kitchen tana aiki, bai jira sun gaisa ba ya wuce daki, xaune ya ga khadijah ta takure waje daya, Ya durkusa kusa da ita da sauri yace “Are you okay Amira?” Ta girgixa masa kai da kyar, da damuwa yace “What’s wrong? Kina jin ciwo ne jikin ki?” Karfin halin nuna masa bayanta tayi, yace “Yana maki ciwo?” hawayen da ya gani idonta ya rikitar da shi lkci daya ya dagota yace “Let get to the hospital…..” Kwace kanta tayi ta koma ta durkushe a wajen tana rintsa ido tace “Ya daina” Allah ma yasan daurewa kawai take, ga ciwon kamar ana kara mata take ji, bata san lkcn da ta sakar masa kuka ba a hankali tace “Wayyo ka taimakeni plss” bai sake saurararta ba suka fita dakin, Mama suwaiba bata ma san sun bar gidan ba tana kitchen, har suka isa asibiti Khadijah bata sani ba duk ta rikice, wani asibiti me tsada ya kai ta banda Wanda Yusuf ke aiki, bbu bata lkci nurses suka amsheta da wani likita, yanda Sudais ya daga hankali sai ka rantse ance masa mutuwa xata yi, khadijah bata yi fatan kara experiencing kwatankwacin irin wahalar da ta sha na labour ba har ta bar duniya, tun da suka je take wahala amma shiru, Sudais ya kira Yusuf ya sanar da shi suna asibiti, Yusuf yace “Me yasa baka kawo ta asibitin mu ba” Sudais yace “Just” Yusuf yace “Toh wani asibitin ku ke?” Sudais ya gaya masa, tabe baki Yusuf yyi yace “Kudi ya ma yawa ne, any way idan ta haihu ka kirani” Sudais ya katse wayar ya jinginar da kansa da kujera yana mai yi ma khadijah addu’a a xuciyarsa, bayan awanni biyu ya sake kiran Yusuf, Yusuf yace “Ya? is she delivered” a hankali Sudais yace “Har yanxu” Yusuf yace “Toh fah, ko dai cs xa ayi mata, dama am thinking it will be difficult ta haihu da kanta, any way bari in taho yanxu” bayan wani lkci Yusuf ya xo, dariya Yusuf ya shiga yi ganin yanayin sudais yace “Kaiiii… To ai ko jiddah ke labour sai haka bawan Allah” Shi dai Sudais bai tanka sa ba, yawanci likitocin asibitin duk Yusuf ya san su, don haka har labour room yaje gun khadijah, ya ji tausayinta ba kadan ba ganin irin dauriyarta, baxa ka taba cewa haihuwar fari xata yi ba tsabar karfin halinta, bayan wani lkci Yusuf ya bar asibitin bayan ya kwantar ma da Sudais hankali yace labour kawai take babu wani matsala, wasa wasa dai shiru ake ji wanda hakan yasa likitocin suka kira Sudais office nan suka nuna masa it’s better ayi mata Cs kada yaran da ita kanta su samu matsala, kusan ba da son ransa yyi signing takardar da aka basa ba, bayan wasu yan mintuna aka fitar da Khadijah labour room xuwa Theatre, anan kuma aka yi nasarar ciro mata boys dinta, sai dai sun jigata kamar yanda ita ma ta jigata. Khadijah ta bude ido a hankali ta ganta kwance wani ward, Mama suwaiba dake gefenta ta sakar mata murmushi tace “Sannu Amira, Allah ya baki lafiya” tashi xaune take son yi taji kamar an danneta ta kasa tashin, Mama suwaiba ta mayar da ita ta kwantar tace “Aa kinga ba ki da lafiya ki yi kwanciyar ki kawai kinji” sai a snn taji wani axaba tun daga cikinta har xuwa kafafuwanta, wasu hawaye suka shiga sakko mata cikin rawar murya tace “xafi nake ji” fita Mama suwaiba tayi sai ga ta ta dawo da likita, likitan ya duddubata ya mata Allah ya sauwake sannan ya fita, Nurse ce ta shigo ta mata allura ta fita, bayan fitar ta sai ga Sudais ya shigo khadijah ta bude ido tana kallonsa, ya karaso gefenta cikin sanyin murya yace “Amira….” Bata iya ta amsa sa ba, a hankali ya sa hannunsa cikin nata cikin sanyin murya yace “Be strong Amira, you will get better in sha Allah..” Hawaye ya sakko idonta sai dai bata ce komai ba, ya sakko da fuskarsa dai dai nata yana murmushi a hankali yace “Baki tambayi yaran ki ba ko bakya son su?” Ta gyada masa kai, shiru yyi yana kallonta, can yyi murmushi yace “Toh sai ki bani su” Murya can kasa hawaye na xuba idonta tace “Na baka” ya fadada murmushin fuskarsa yace “Sure?” Throughout ranan Sudais was by her side tare da Mama suwaiba, Yusuf ma ya xo yyi mata barka ya wuce, ba a nuna mata yaran ba kuma bata tambaya ba har ta sa a rai kila ma mutuwa suka yi wanda tunanin hakan yasa mata nutsuwa sosai don har ga Allah bata ma son ganinsu, haka kawai taji bata san su, Sudais dake lura da cewa she was so depressed ya dinga kokarin ganin ya sa ta walwala sai dai ta kirkiri murmushin karfin hali, sallah kadai ke sa shi ya bar gefenta, tun karfe shidda mama suwaiba ta koma gida dauko kaya, duk kiran da aka dinga ma sudais a waya kin dagawa yyi daga karshe ma ya sa wayar a silent, A daren ranan bayan sudais yaje sallar magrib da ya tashi dawowa ya shigo rike da daya daga yaran wata nurse na biye da shi da dayan, tun da suka shigo khadijah ke kallonsu, yana murmushi ya ajiye babyn a gefenta, sosai gabanta ya fadi ta dinga yi ma jaririn wani kallo ganin kamar Aliyu yyi kaki, babu abinda new born din ya mance na ubansa tun daga haske, hanci, kai har bakinsa… Nurse din ta ajiye mata daya carbon copy din yaron dake gefenta kusa da d’an uwansa tana murmushi tace “Congrat mum twins, Allah ya raya su” daga haka ta fita, a hankali Sudais yace “Ain’t they cute? I mean the innocent new souls” khadijah bata san lkcn da ta fashe da kukan takaici ba cikin rawar murya tace “Don Allah ka tafi da su, wllh bana son su, ni dai bana son su ka maida masu su” kuka take sosai kamar xata shide, ganin haka Sudais ya mike ya dau yaran gaba daya ya fita da su dakin.