Noor AlbiNOVELS

NOOR ALBI 25

Tsaye yake sanye cikin farar jallabiyar data bayyanarda wani Hasken daya qara Wanda ke bayyanarda bayajin dadin shima Amma ba’a wani ganewa, sauraron nurse da zata tafi yagama Yi kafin ya dago oily eyes dinsa da har lokacin Basu Gama dawowa daidaiba yayi Mata kallo daya ya dauke idanuwansa Yana juyawa ya fice Dan ganin yanayinta na rashin kaya sbd towel din jikinta qarantarsa Tayi yawa gashi rashin qarfin jikinta yasa takasa dauresa dakyar riqe kawai take dashi saman saman kirjinta Yana Dan bayyana.

Jiki mace ta iya saka Riga Mara tsayi Takoma tasanya jallabiya tayi sallah a zaune kafin ta lallaba ta koma gado tana kokarin kwantawa aka shigo Mata da breakfast batada apatite Amma Sbd magani da zatasha Dole Tasha tea da kidney sauce Mai kwai aciki Tasha maganin Takoma ta kwanta wani baccin yakuma daukanta.

Sai yamma ta farka lokacin zazzabinta ya Dan rage Amma dai tana Jin pains kadan kadan ajikinta Dan Haka takuma komawa tasakarwa kanta ruwan zafi.
Wayarta a kashe ta wuni Kuma Bata kunnaba Saida takwana biyu zuwa Lokacin taji sauki ba laifi tana iya fitowa daga bedroom dinta Amma iyakacinta kitchen kokuma qaramin palo wadda bazata hadu da Wanda batason haduwar dashiba.

Kwana biyu tasake samun sauki sosai suka koma school Dan Haka ta fara fita school ta rage zama gida Sosai sbd mum Na’ima Bata dawoba har lokacin,
Abin daya faru tsakaninta da Abban ta dannewa zuciyarta ta Hana kanta tunawa sbd ta dauka hakan babbar qaddara wadda tariga ta faru tunata kamar tunawa kanta kuskuren dayariga ya faru ne Dan Haka ta danne ta talastawa kanta Yi kamar Bata tana sanin wani abin makamancin hakan ya faruba ta saka kanta zama busy Sosai a karatu
Danma kada ta bar duk wani tunanin dazai tunatar da al’amarin saita sake sosai tana yin rayuwarta Kamar koyaushe acikinsu Cindy.

Sai Bayan sati biyu Mum Na’ima ta dawo gidan lokacin Bata Nan tana dawowa school taganta wani irin Abu taji Yana bugawa a zuciyarta na tsananin kunyar Mum Na’ima din Mai tsananin qarfi da baqin cikin kanta Dan kuwa sai tanajin kamar ta zama babbar butulu saidai tayi alqawarin qin saka zancen wannan al’amarin cikin kanta Dan Haka ta qaraso da murmushi a Kan fuskarta da murnar ganin mum din ta rungumeta kamar yanda ta ware Mata hannu tana cewa”

I’m back princess.

Murmushi tayi Mai sauti tana cewa”

We miss you mum.

Dariya Mai sauti Ms Na’ima tayi ta farin ciki Dan kuwa da farin ciki ta dawo sbd abinda sukaje Yi sunyi komai cikin Jin Dadi yanda sukeso na kasuwancinsu tace”

Nayi kewarki sosai My baby keda Abbanki gashi nadawo shima bayanan tun last week Yana Nigeria yatafi.

Dan murmushi tayi tana cewa”

Mum lemme go and freshen up, I’m morethan tired.

Bedroom dinta ta Isa ta tube tafada toilet tayo wanka ta fito ta shirya cikin qaramar Riga mara nauyi da skirt tayi sallah ta fito ta nufi kitchen ta hado Krispies tafito tanaci ta zauna tareda mum din daketa Mata labarin boutiques da sabbin shagunanta da za’ai launching.

Da daddare tare sukaci abinci a dining Kamar yanda aka Saba tunda mum din tadawo Kuma qarin samun nutsuwarta a dining din daga ita sai mum din Dan Haka har fira sukai sai 10 ta shige tayi wanka ta kwanta.

Da anty Sa’adah sukai waya wadda take fama da Dan rashin lafiya kwanakin Amma dai tasan bazai wuce stress na karantun datake Shirin kammalawaba,
Tunda wannan abun yafaru da ita Bata iya waya da Anne sbd wani irin nauyi Mai girman gaske takeji duk da tasan har abada Babu Wanda zaisan hakan ya faru Amma ta kasa Hana kanta Jin tsananin nauyin Annen,
Annen da kanta take kiranta Amma hakanan sai Bata wani Gane Kan Laylan sbd yanda take magana cikin rashin sakewa bayan suna murnar lafiyarta data Dade da samuwa saidai Bata damuba sbd tasan bazai wuce yanayin jiganiyar karatuba itama.

MAMUH

Previous page 1 2

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button