NOVELSUncategorized

QANIN MIJI 8

_Jinjinar ban girma ga gaba ɗaya writers ɗin pure moment of life, da writers ɗin  fasaha, ku ɗin mutanen kirkine da kuka kai ajinjina muku, kai gaba ɗaya writers ɗin online ina jinjina muku domin kun nuna min

soyayya wallahi, Allah ya so ku kuma, musamman bayin Allahn nan

Aunty Ruky
Mom uswan
Sadnaf
ummie garkuwa
swerry
ummiexeey
smarsher
my heenat
meerah mmn lateef
Maryam salis maidala
Janaf
my lashminzy
Ummu Rahma
My cwt dota, Billyn Abdoul
Wallahi kuna da yawa, wasu ban ambaci sunansu bane ba wai dan basa raina ba, sai don manage ɗin page amma zaku ji inshaa Allahu, domin soyayyar da kuka nunamin ta kai in ambaci sunayen naku, godiya cikin jirgin titanic and 143 forever and ever????
*
Tambayar da ake min shine fingering na kawo aljanu?, toh ki ji ‘yar uwa, wallahi, billahil azeem fingering na kawo aljanu jikin namiji ko mace, musamman ga ɗiya mace, zaki jawo Jinnul Ashik shiga jikinki, sai ki ga yarinya budurwa a sanadiyar karance karancen batsa da kalle kalle shi wannan aljanin ya aureta, wataqil ya zo wucewane, sai ya ga tana aikata abinda take aikatawa, sai ya ji sha’awarta sai ya shige jikinta ya dinga biya mata buqata, a cikin barcinta ko a farke, wata sai ki ga har Allah Allah take yi ta kwanta bacci aljanin ya zo ya kwanta da ita cikin mafarki, shi kuma wannan Ashik ɗin ba wai saduwa kawai zai dinga yi da ke ba, wallahi wataran sai ya sakaki kin yi tsawa wa mahaifiyarki ko mahaifinki da suka haifeki, zaki iya rufe ido ki ci musu mutunci sai daga baya idan ya nisanceki ki fara tunanin how comes?, sannan ya fara sanya miki tsanar alqur’ani da masu sauraronshi da duk wani abu da ya jiɓinceshi, bayan nan wallahi duk kyanki da iya kwalyarki matuqar saurayin da zai aureki ya zo toh wallahi sai ya koreshi, masu nemanki da lalata kawai zai bari shaiɗanu ‘yan uwansa daga cikin mutane, idan kin biye musu shikenan kin zama karuwar gida, duk a silar fingering, karki yi shakkar maganata, idan kin san kinayi ko ke matar aurece sai sun munanta fuskarki a gurin mijinki, ya ji ya tsaneki, ba kya burgeshi, baki bashi sha’awa, ko yasa kiyi ta wa mijin rashin kunya, ba tare da kin sani ba, baiwar Allah idan kinayi kina kuma kokonto kan maganata toh ga addua kiyi kafin bacci zaki gane kin fara samun hari ko farmaki, farko in zaki kwanta kar kiyi fingering ɗin, ki je kiyi alola, ki karanta fatiha da bismillah qafa bakwai bakwai a ruwa, sannan kiyi ayatul kursiyyu sau uku, falaqi, nasi, ikhlas, sau uku uku, sai ki shanye ruwan ki shafa sauran a jikinki, sannan in kin iya qur’ani ki karanta baqara zuwa wattaba’u kafin ki kwanta, sannan kafin barci ya ɗaukeki kiyi ta maimaita la ilaha illallahu wahdahu lasharika lahu lahul mulku wa lahul hamdu wa huwa ala kulli shai’in qadir,  ‘yar uwa, a ranki kawai in kika ji ba za ki iya wannan ba toh ya tabbata kin wa kanki illah ta gayyatoh sheɗanu jikinki, ko kuma kina farawa bacci ya bugeki ba tare da kin sani ba, ko idan kin tashi yi ki ji ranki ya ɓaci ko hankalinki ya tashi, ko cikin barcin ki ganshi ya zo anma gashi dai namijine yana son kwanciya da ke ya kasa, ke dole sai kin ga wata alama saidai idan ke ɗin daki dakace tubalin toka, Allah ya shiryar damu da matasan musulmi, amma ki gwada
8
Harara ta banka masa cikin wani irin salo tace
“ni dai da hankalina, ban son haka gaskiya”
“ke wasane fa kawai, kin yi wani kici kicin da fuska”
“wasa?, kai mijina ne”?
Buɗe baki yayi irin na mamakin nan yace “au, toh ni mene ne idan ba mijinki ba, ka ji min matar nan”
Hararan wasa ta masa tace “mijinta dai ba ni ba, wanda ya biya sadaki daban kai kuma ka zo qato da kai kai ne mijin”?
Wani irin shaiɗanin kallo ya mata yana aika mata da murmushin ɗaga hankali yace “nima ai sadakin ba gagarata yayi ba, zan iya biya idan an min izini”
Duk da kallon nasa ya fara taɓata haka ta daure tayi dariya tace
“hey gaye no sisi, sai mijina ya san maka fa”
Harara ya banka mata bayan ya haɗe fuska yace
“Allah ya kiyaye, ni da kaina na dogara ba da wani ba”
“tafi can, mai qarya”?
Tace cikin dariya
“ke !, waye me qaryar”?
“kai” ta sake faɗi tare da kanne idanu
Zaburowa yayi ya tashi yana cewa “ni”?
Eh tace tare da haramar gudu dan ta ga alamun  binta zai yi kamar yadda suka saba
ai kuwa ya bita da gudu suka zuba suna zagaye falon tana dariya qyal qyal tana cewa “dan Allah hafeez ka bari, wallahi bana so ka bari”
Shi kuwa shashashan yana cewa “wallahi yau sai kin faɗa min me qaryar zaki sani”
Ai kuwa haka yayi ta bin ta har ya ritsa da ita ya cafkota ya haɗata da qirjinsa ya rungume
Dariyar da take yi ta daina ta fara cewa “hafeez dan Allah ka sake ni, wallahi bana son irin wannan wasan, bana so”
Maimakon ma ya saketa kamar yadda ta buqata sai ma qara matseta da yayi da qirjinsa hannayensa kan qirjinta yayin da ya fara sauke mata numfashi a wuyanta, tuni hankalin fareedah mai dubun sha’awa a jikin ya fara tashi,  kasalalliyar maganar da ya fara mata a kunne ita ta yi nasaran kashe mata jiki da rufe mata baki
“wa…kike…kira..maqaryaci….”
Shiru fareedah ba magana, sai idanunta da ta rintsesu tana karɓar baqon yanayin da hafeez ya sanyata dan yanzu ba ta da lakar qwacewa
“na ce wa kike cewa maqaryaci…..”?
Ya sake cewa tare da qara matseta still hannayensa na kan qirjinta, saidai nan ma ba magana,
yoh toh waɗanda mazajensu suke sauke musu hakkinsu ma yaya suka cika da irin wannan wasan balle fareedah da take ɗauke da sha’awarta ki da yaushe
Shiru suka yi ba magana sai karɓar yanayin suke yi abinsu, sai can hafeez ya sake tausasa murya kamar me raɗa yace
“toh ki sake qaryatani ki gani, zaki ga hukuncin da zan miki, kin ji ko”? Ya qarashe da sake rage murya sannan ya fara saketa a hankali har ya raba jikinsa da nata yayi saurin barin gurin zuwa ɗakinsa yayin da ita kuma Fareedah take tsaye har a lokacin idanunta rintse, sai da ta farga da ya saketane ta zube akan gwiwowinta ragwab tana mayar da numfashi, ta daɗe a gurin kafin ta tashi itama ta wuce ɗakinta ta kwanta lamo a gado, iya qololuwar sha’awa hafeez ya ɗaga mata, ji take yi ma kamar zazzaɓi zai kamata, har wani sanyi take ji tare da rawar jiki, hakan ya sanya ta janyo bargo ta lulluɓe jikinta ta qudundune, saidai ta gagara nutsuwa, sai wani mutsu mutsu take yi tana juye juye, yanayin da ta shiga a yayin da take qirjin hafeez ya qi ya bar brain ɗinta, a haka har aka yi magriba, isha’i ta shigo sannan ta iya daurewa ta tashi ta je tayi wanka dan wankan ya kamata dole sannan ta zo ta yi sallolin a jere a lokaci guda
***
A ɓangaren hafeez shima hakane, tunda ya shige ɗaki ya kasa samun nutsuwa, hankalinsa gaba ɗaya ya tashi, ya buɗe videos kala kala duk dan nutsuwar ta zo masa amma ko qamshinta bai jiyo ba, fareedah kawai shaiɗan yake qawata masa, musamman yanzu da ya lura itama sha’awarta ta motsa, ya lura da kyau a kwanakin tana cikin yanayine irin nasa, a daddafe yayi ta amfani da hanunsa  gurin nemo wa kai nutsuwa sannan ya je yayi wanka ya tafi masallaci ba dai a cikin full nutsuwarshi ba, dan Allahu akbar ɗin kawai yake iya ji a kunnensa, dukkan hankalinsa na ga fareedah da halittun jikinta
***
Halin damuwar da fareedah ta shiga ya sanyata kiran fa’eez don ta ji yaushe zai  dawo
Tayi kira yayi biyar kafin faeez ya ɗaga wayar cikin kasalalliyar muryarsa kamar kullum , a daddafe suka gaisa kowa sha’awa na walagigi dashi, yayin da shi sheɗaniyarsa take jikinsa tana masa wasannin da suke ruro wutar sha’awar a jikinsa
A shagwargwaɓe tace “my man wai ni yaushe zaka dawone, ni fa wallahi ba zan iya jurewa ba”
“kamar yaya ba za ki iya jurewa ba”? Yace yana me haɗe fuska kamar tana kallonsa
Kamar za ta yi kuka tace “ni dai gaskiya hakurina ya gaza, ina da buqatarka a shimfiɗata”
“ehem, daman na san abinda zaki ce kenan, ke kenan kullum a kwanta dake shine damuwarki, kamar kece uwar ‘yan sha’awar duniya, toh ni ya aka yi na jure, hakurin nawa har yanzu bai gaza ba”?
Kukan shagwaɓa ta fashe masa da shi tace “ni dai komai zaka ce na yarda, ka dawo kawai ko kamin izini in taho inda kake, dan wallahi ba zan iya ba”
Cikin jin haushi faeez yace “kar Allah yasa ki iya, ni ba zan dawo yanzu ba domin ban gama abinda na zo yi ba, kuma ba zan yi izinin ki zo ɗin ba, ke dawowata ma ba yanzu ba, sai na ɗora wata akai ko biyu, daman na faɗa miki zan iya kaiwa hakan, atoh”
Kuka ta fashe masa da shi, shiko ya ja mata dogon tsaki yace “toh in kin gama kukan kya nemeni muyi wata maganar, ba wannan ba”
Yana gama faɗin haka ya datse kiran ya wurgar da wayar ya janyo Tina suka shiga duniyar mashaarsu, yayin da baqin ciki ya sanya fareedah kuka tsawon wannan dare, har jikinta yayi zafi ga damuwa ga sha’awa, saidai sheɗan ya hanata tunawa da ambaton Allah, saidai yau ko fingering ɗin ba ta yi ba saboda baqin ciki
**
Breakfast take haɗa musu ita da hafeez saidai ba ta da wata walwala, aikin take yi sukuku, ba tare da ta san da shigowarsa ba ta ji hannayensa kan fuskarta ya rufe mata idanu
Ya raɗa mata “morning dear” ta ɗan tsorata kaɗan kuma ba tare da ta shirya ba ta kwanto masa a jiki tana sauke numfashi, ganin ya ɗan samu dama sai ya sake mannata a jikinsa yace cikin raɗa still
“na tsorataki ko”?
Lumshe idanu kawai tayi tai shiru, fuskarta ya juyo da ita suna fuskantar juna ya ɗago haɓarta ya kira sunanta cikin wani irin sauti mai matuqar kashe jiki
Idanunta da suka rine ta buɗesu kan fuskarsa saidai ta kasa magana, yana kallon cikin idanunta cikin kallon ‘yan maye da qunar baqin wake dan bai san makomar zancensa ba,  yace
“fareedah na fahimci kema kina jin abinda nake ji ko?”
Ba ta iya magana ba sai mayar da idanunta da tayi ta lumshesu
Hakan ya bawa hafeez daman sake wata qundunbalar ya sunkuyo kusa da fuskar fareedah ya fara hura mata iskar hancinsa a fuska, shaiɗan kuwa ya fara buga musu gangarsa  yana ingiza zukatarsu tare da qawata musu yanayin, ganin fareedah ta fara fitar da numfashi da sauri da sauri ya sanyashi tallaɓo haɓarta ya daidaita bakinsu ya fara mata zazzafar kiss cikin salo mai rikitarwa, tuni fareedah ta rikice, a hankali ta fara maida masa martani domin taimaka musu gurin jin daɗin ɓarnarsu, qaurin abincin ne ya farfaɗo dasu daga duniyar da suka dulmiya, da qyar suka sake juna hafeez yayi jarumtar fincike socket ɗin electric stove ɗin ganin kaskon ya fara kamawa da wuta
Idanunta a runtse tana jin gine a bangon kitchen ɗin tana mayar da numfashi ta ji hannayen hafeez a jikinta ya sunkuya ya ɗauketa kamar baby, lafewa tayi a jikinsa idanunta still a rufe, ba ta san inda suka nufa ba sai jinta tayi a kan gado wanda hakan yasa tayi saurin buɗe idanunta
Bakinta na rawa ta buɗe ta fara cewa “ha…ha..feez…”
Bai bata dama ba ya haɗe bakinsu guri guda wanda yayi sanadiyyar fara gangarowar hawaye daga cikin idanunta yayin da shi kuma ya fara gigitata da mahaukatan wasannin da suke ratsa brain ɗinta saidai ba ta daina hawaye ba, sai ma shessheqar da ta fara yi tana kuka, hakan ne ya sanya hafeez cin burki tare da ɗago idanunsa suke burkice yana kallonta, ganin tana kuka cikin rawar murya ya fara magana
‘yar uwa kar ki yarda qanin mijinki ya miki wannan rainin da tozarci, ki ci ubansa idan kika ga zai kawo miki wargi, duk tsiyar da za ayi aje ayi, amma ya kwanta da ke, hmmm sunanki sorry
ISLAM IS MY IDENTITY

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button