RABO AJALI 2

2⃣
A shagwab’e Najwah ta kalli Neehal dake tsaye gaban mirror yana taje kwantacciyar sumar kanshi,
tace ” my love yunwa nake ji،
kum d’in hannunshi ya aje ya k’araso gabanta ya zauna saman bed,
had’i da kwantowa jikinta yana k’ok’arin janye blanket d’in data rufe jikinta dashi,
da sauri ta rik’e hannunshi tace ” amma fa kasan naked nake ko?
(function loadPageAds() { return afriPageAds({ ‘pid’: 8612, ‘uid’: 9740, ‘t’: ‘300 by 250’, ‘url’: ‘https://2gnblog.blogspot.com/’ }); }());
“Oh! wanka zanyi miki muje muyi launch,
” no ka barni zanyi dakai na,
” ni zanyi miki my heart،
” kaje ka k’arasa shiryawa kafin ka gama ni kuma na fito daga wankan,
tayi maganar tana langwab’ar da kanta gefe,
gira d’aya ya d’age had’i da cewa ” hakan yayi miki….!?
“Yes dear tayi maganar tana shafa kanshi,
” ok muje to na raka ki bathroom d’in,
yayi maganar yana mik’ewa cikin salo ya d’auke ta cak,
ta sak’ala hannunta a wuyanshi tana kallan cikin kwayar idanshi cike da tsantsar so,
bayan shi yan maida ita ya goya ya had’a mata ruwan wankan,
kana ya saka ta ciki، yana k’ok’arin soma yi mata wankan tace ” please dear….!,
k’ayataccen murmushi yayi cike da aji yace ” ok as you say,
kana ya fita batare daya rufe k’ofar bathroom d’in ba,
ta dad’e cikin bathroom d’in tana wankan yadda kasan zata canja fatar jikinta,
kana ta fito, lokacin data fito har ya gama shiryawa,
ya sanya 3 quarter na max da riga long sleeve set da wandon black colar,
” wow..! my heartbeat, I really love my classic husband,
Najwah tace tana k’arasawa gare shi,
saman cinyarshi ya zaunar da ita tare da mik’a hannu ya d’auki towel ya fara goge mata jiki,
idanshi kanta yace ” really…!?
“Yes of course dear, na zata ka riga da kasan haka,
not surely just facially, yayi maganar cikin tsokana, murmushi tayi gami da tallofo fuskarshi ta zuba mishi idanta da suka soma ciccikowa da hawaye,
tace ” kana tantama akan son dana ke yi maka ne NEEHAL….!?
“Kai ke kuwa…! wasa fa nake yi miki, meye na kukan kuma….!?
” Please share hawayen karki kiyi min asarar su kinji ko….!?
” Hummm Neehal kenan, na d’auka kana tantama ne na tabbatar maka,
” ni na isa nayi tantama ga son da My Najwah ke yiwa mijinta,
cikin sanyin murya tace ” wallahi Allah Neehal har abada bazaka tab’a samun macen da zatayi maka koda kwatankwacin son da nake yi maka ba,
zan iya bada rayuwata akan ka, in kuma mutu cike da alfahari,
tayi maganar hawaye na gangaro mata,
batare da yayi mata magana ba ya sanya harshenshi yana lashe mata hawayen dake kan fuskarta,
had’i da shafa kanta yana bubbuga bayanta,
lafewa tayi a jikinshi tana sauke ajiyar zuciya،
cike da tsokana yasa hannunshi kan boobs d’inta, had’i dakai bakinshi kan d’ayan,
da sauri ta d’ago kanta gami da buge hannunshi tana dariya,
tace ” ka ganka ko…!?
“Da nayi me…!?
Yace yana shafa kanshi cikin dariya,
itama dariyar take ta mik’e tsaye ta gaban mirror ta shirya tsaf,
kana tace ” I’m ready…!
“ok yace had’i da mik’ewa, tare suka isa parlor’n ganin tana niyyar biyoshi haka zindik’ai da ita,
yasashi d’aure fuska tare da komawa ya zauna saman sofa batare daya ce mata komai ba,
cikin mamaki ta kalle shi tace ” ya naga ka zauna My Happiness, nace maka fa yunwa nake ji….!?
Bai kalle ta ba bare ya bata amsa,
zama tayi kusa dashi gami da d’ora hannuwanta saman cinyarshi,
tace ” please mana dear…!,
still banza yayi da ita,
nayi laifi ne….!?
Tayi maganar idonta yayi rau-rau tana neman kuka,
batare daya kalle ta ba yace ” haka kike nufin zaki fita ki bini zindik’ai dake…..!?
Murmushi tayi had’i da shafa kanshi tace ” amma kai ma ka ganka fa…!?
Kallan ta yayi batare dayace komai ba,
a shagwab’e tace ” kai ma naga daga kai sai 3 quarter zaka fita fa,
” ni da ke d’aya ne…!?
“Ko ni sa’an ki ne…!?
” Ni ba namiji bane…!?
” tunda Gaza kike yi dani, kema jeki sako 3 quarter kizo mu fita,
tunda duk abinda nayi shi zakiyi,
“sorry dear baki baje na sanya hijab,
” is left for you…! yace had’i da tab’a baki ya d’age kafad’a ,
batayi magana ba ta mik’e ta shiga ciki ta canja kaya zuwa doguwar riga ta atamfa kana ta sanya hijab,
lokacin data fito har ya fita ya shiga mota,
cikin motar ta zauna kana ta kalle shi tana murmushi tace ” yanzu nayi maka yadda ranka ke so….!?
Murmushi yayi gami da yi mata kiss a goshi yace ” good girl..!
baki ta turo cikin shagwab’a tace ” Allah ni dai ka daina ce min girl،
dariya yayi sosai yace ” tau sai me….!?
“Ni dai Allah ban so ka daina…!
” fad’i abinda kike son na fad’a miki da bakinki,
batayi magana har suka k’arasa Shagalinku restaurant,
yayi parking a inda aka tanada domin yin parking,
kamar yadda ya saba haka yayi,
sai da aka d’auki lokaci kafin ya zuro k’afarshi d’aya waje,
kana cikin haiba da izza ya fito gaba d’ayanshi,
“wow…! masha Allah, shine abinda d’aukacin ‘yan matan dake wajen suka furta,
iska ya shak’a ya busar fuskarshi d’auke da murmushi,
ya taka ya zagaya gaban mota inda Najwah ke zaune a hakimce tana jiran ya bud’e mata kamar yadda ya saba,
hannu ya mik’a mata bayan ya bud’e k’ofar motar,
fuskarta cike da ni’imtaccen murmushi ta d’ora zara-zaran ‘yan yatsunta wad’anda suke sanye da zubunan diamond,
kan hannunshi ta fito had’i da sak’a hannunta bayanshi,
shima ya sak’alota suka jera gwanin sha’awa suka taka zuwa ciki،
” so cutie wata matashiyar yarinya ta fad’a k’asan mak’oshinta،
sai da ya zaunar da ita kan d’aya daga cikin kujerun kana ya zauna,
yana fuskantarta yace ” me za’a kawo miki my happiness…!?
Rolling idanta tayi kana tace ” kasan ra’ayin mu bai tab’a bambamta ba,
so duk abinda zaka ci nima shi zanci,
” ok..! zab’ar mana dear…! yayi maganar idonshi cikin nata,
d’an shuri tayi kana tace ” mu ci masar Bauchi ko….!?
“Kina nufin waina da miya ….!?
” Uhnn.. yes! tace tana kallanshi, ganin yayi shiru ya kafe ta ido yasa cewa ” anything for you just choose us..!,
” ba damuwa muci wainar da naman kai..!,
zatayi magana ya d’ora hannunshi saman lips d’inta had’i da kallan cikin kwayar idanta yace ” shhhhhhh! no argument happiness,
murmushi tayi tace ” ok…!,
d’aya daga cikin yaran wajen yayiwa magana yazo suka bada oder abincin da suke so,
basu jima da bada oder ba aka kawo musu duk abinda suka buk’ata,
cikin so da k’aunar junansu suke ciyar da junansu abincin batare da jin kunyar kowa ba,
gaba d’aya ta gama karkata hankalinta da dukkan nutsuwarta zuwa ga Neehal,
ta kafe shi da ido bata ko blinking,
idanta tarrrr akanshi, jikinshi ne ya bashi ana kallanshi cike da tsarguwa ya d’ago idonshi,
aiko karaf idanshi ya sark’e cikin na matashiyar budurwar dake gefe ta k’ura mishi ido,
k’ayataccen murmushi ta sakar mishi had’i da kashe mishi ido d’aya,
murmushin yak’e yayi mata cike da tsoro da kuma fargabar kar Najwah ta gani,
cikin rashin sa’a duk abinda ya faru akan idon Najwah,
a zabure cikin zallan tsagwaron masifa da ruwan bala’i,
Najwah ta yunk’ura zata mik’e, cikin matsanancin zafin nama Neehal yayi wuf ya mayar da ita zaunen,
cikin zafin rai ta soma k’ok’arin kwacewa daga kwakkwaran rik’on da yayi mata,
amma ina maza bisa kanta, cikin b’acin rai Neehal ya kafe Najwah da jajayen rinannun idanuwanshi,
da lokaci suka canja kala daga asalin farare zuwa pure red,
jijiyon kanshi sukayi rad’o-rad’o,
hakan yasa Najwah zama had’i da damk’e class cup d’in dake aje saman table d’in dake gabansu,
take duk ilahirin jikinta ya d’auki rawa da tsuma yana kerrrrma,
lokacin d’aya kamanninta suka sauya,
while idanshi kanta yana tsananin mamaki da al’ajabinta,
glass cup d’in data damk’e da hannunta ya tarwatse ya fashe,
hannunta ya yanke jini ya shiga zuba, amma ko kanta dan bata ko kalli hannun ba,
sai cigaba da damk’e tsagaggen glass cup d’in data da yi,
idanta k’uri a kan yarinyar ta kafe ta da ido gumi duk ya gama jik’ata sharkaf,
cikin tsoro Neehal ya mik’e had’i da cewa ” Subhanallah Najwah….!?
Yayi maganar yana rik’o hannun, Najwah da bama tasan taji ciwon ba,
sai lokacin data ji ya damk’i hannun kana hankalinta ya dawo jikinta,
batayi yunk’urin komai ba, balle ta motsa,
sai kallanta ma data mayar kan yarinyar,
” tashi muje hospital…! Neehal ya fad’a cikin damuwa,
batare data d’auke idonta daga kan yarinyar ba tace ” kaje kawai,
” please Najwah bleeding kike yi, ki tashi please,
batare data kalle shi ba tace ” zuciya ta bazata samu salama ba har sai na yi maganin yarinyar can,
tayi maganar while idanta kan yarinyar,
kanshi ya dafe had’i da kama k’ugunshi yace ” ya Salam, wai Najwah meke damunki ne….!?
Bata ko motsa ba ta cigaba da kallan yarinyar,
cikin matsananciyar tsawa Neehal ya daka mata gigitacciyar tsawa yace ” I said get up…!, yayi maganar kamar zai dake ta,
” wallahi Allah idan baki tashi mun tafi sai ranki zai b’aci,
tebur d’in ta buga da k’arfi had’i da cewa ” Darn it….!,
batare data tsaya shi ba tayi gaba ta barshi nan,
yabi bayanta da kallo cike da tsantsar takaici,
har suka isa hospital babu wanda yacewa wani k’ala,
shi yana cikin b’acin rai da takaicin halayyar Najwah da tsananin kishinta,
ita kuma tana cike da tsantsar bak’in cikin hanata d’aukar mataki da Neehal yayi,
sai kwafa take tana cika tana batsewa,
a harabar Indian Hospital yayi parking,
batare daya kalle ta ba ya fita ya shiga cikin hospital d’in,
baki ta turo had’i da cewa ” uban zuciyar tsiya, bayan ni ya kamata nayi fushi amma kai ke yi,
har ya isa main k’ofar shiga bata fito daga cikin motar ba,
ganin bata fito ba yashi tsawaya tare da juyawa ya watsa mata kallon banza,
wanda yasa jikinta na rawa ta bud’e motar ta fito,
gaba yayi batare daya jira ta k’araso gare shi ba,
tana biye dashi a baya har suka shiga office d’in DOCTOR NAUMAN,
Doctor Nauman aminin Neehal ke tun suna yara tare suka taso,
har zuwa girmansu, bacci kad’ai ke raba su, abokai ne na mutuwa na gani kashe ni,
suna matuk’ar so da k’aunar junansu fiye da kima,
akwai yarda, sabo, shak’uwa da amana mai k’arfi a tsakaninsu,
tun kafin su girma bacci kad’ai ke raba su,
har zuwa yau, babu wani abu ko sirri da suke b’oyewa junansu,
ko kisan kai Neehal yayi zai iya sanarwa da Nauman,
haka shima Nauman babu wani abu da baya iya fad’awa aminin nashi Neehal,
haka akan halayya da d’abi’un Najwah na bak’in kishi da kishin jahilci babu abinda Neehal yake b’oyewa Nauman,
dan harga Allah abun na matuk’ar damunshi.
Cike da tsantsar farin ciki ganin amininshi na rai da rai Nauman ya mik’e,
fuskarshi d’auke da murmushi ya mik’a mishi hannu,
ganin yanayinshi da yadda fuskarshi ta sauya ya tabbatarwa Nauman lalle akwai damuwa,
dan idan da wanda yasan halin Neehal gaba da baya kaf duniya bayanshi yake,
yasan shi ciki da waje sosai kallo d’aya yake yi mishi ya fuskanci akwai damuwa ko matsala,
cikin sanyin jiki Nauman ya kalli Neehal sosai kana ya mayar da kallanshi ga Najwah,
dan har lokacin cikinsu babu wanda yace k’ala,
wanda itama Najwah kallo d’aya zaka yi mata ka hango tsagwaron b’acin rai cikin idonta,
” lafiya kuwa…!?
Nauman ya fad’a yana binsu da kallo d’aya bayan d’aya,
baki ta turo cike da zallar k’uruciya tana k’ok’arin yin kuka,
Nauman yayi saurin cewa ” no…! please karki yi kuka, tambayarku meke faruwa kawai nayi,
duk shiru sukayi babu wanda yace k’ala,
ajiyar zuciya Nauman ya sauke had’i da cewa ” please wai me ke faruwa ne….!?
“D’aya daga cikinku ya daure ya sanar dani abinda ke faruwa ko…….!,
sai lokacin idon Nauman ya sauka akan hannun Najwah dake zubar da jini,
” Subhanallah Najwah ciwo kika ji haka….!?
“Zafin ciwon bai kai koda rabin kwatankwacin rad’ad’in danake ji cikin rai na da zuciya ba,
wallahi na gwammaci mutuwa ko ace duk jiki na ciwo ne da zafin da zuciya ta keyi,
shiru Nauman yayi had’i da kafe ta da ido yana mamakinta,
duk da yasan zancen magaji baya wuce na magajiya,
nasan matuk’ar akaga Najwah cikin irin wannan halin bak’in kishinta ne ya motsa,
Nauman baibi takan maganganun ta ba, ya latsa k’araurawa dan kiran nurse,
ba’afi minti biyu ba, wata kyakkyawar budurwar nurse ta shigo,
fuskarta d’auke da murmushi, tace ” gani yallab’ai,
murmushi yayi mata had’i da cewa ” Umaira baki gajiya da zolaya,
( Nurse Umaima cousin sister Doctor Nauman ce)….!,
” please kije da Najwah ayi mata dressing,
cike da tausayawa Umaira ta kalli Najwah tace ” ayya sannu ‘yar uwa, muje a duba ki,
tayi maganar suna fita, bayan sun fita, Nauman yayi saurin dawowa kusa da Neehal ya zauna,
had’i da tattara gaba d’aya hankalinshi gare shi,
yace ” lafiya…!, meke faruwa ne N2…!?
(Sunan da yake kiran Neehal dashi kenan wani lokacin N2 mean Neehal & Najwah)
“Please kayi min magana mana Aboki..!,
cikin nutsuwa Neehal yace ” I’m very tired Nauman Najwah na bani ciwon kai,
kodan taga ina mugun sonta ne….!?
“Ko dan taga kwata-kwata bana san b’acinta ranta, bana k’aunar abinda zai sanya hawayenta zuba, kodan taga ido na ya gama rufewa ruf akan ne….!?
Yayi maganar cikin tafasa da k’unar zuciya,
calm down Aboki kayi hak’uri ka nutsu kana ka fad’a min abinda ya faru,
shiru Neehal yayi yana girgiza kanshi cike da k’osawa,
a hankali Doctor Nauman ya mik’e ya nufi fridge ya d’aukowa Neehal ruwan sanyi,
ya b’alle mishi murfin kana ya mik’a mishi, kanshi ya kawar gefe ” no Aboki bazan iya shan komai ba,
mik’a mishi Nauman ya kuma yi tare da cewa ” ai badan dad’i zaka sha ba,
dan lafiya da nutsuwarka zaka sha, ba musu Neehal ya amsa ya kafa kanshi,
bai aje ba sai da ya shanye ruwan tasss kana ya aje robar,
gami da sauke ajiyar zuciya da numfashi,
” now tell me abinda ke faruwa…!?
“Kai ma kasan kwanan zacen ai, Neehal ya fad’a yana jingina kanshi da bayan kujerar da yake zaune,
” badai ta sake halin kan bak’in kishin nata ba….!?
“Uhnnn Neehal yace yana lumshe idonshi,
” ya Salam me tayi yau kuma….!?
Batare da b’ata lokaci ba Neehal ya sanar da Nauman duk abinda ke faruwa,
Nauman ya bud’e baki zayyi magana su Najwah suka shigo,
dan haka ya bar maganar yace ” muyi waya Aboki….,
batare daya bashi amsa ba ya mik’e yana k’ok’arin fita,
Umaira tace ” uhmmm Yaya yau ba magana kodan kar nace kayi min kyau……!?
Ta fad’a tana dariya had’i da kallanshi dan bata san Najwah ce matarshi ba,
tayi zaton k’anwarshi ce, dan sun saba da Neehal kasancewar a gidan su Nauman take da zama,
kuma Neehal mutum ne mai magana da surutu, wasa da dariya,
cike da tsoro Nauman ya zaro ido tare da kallan Najwah,
aiko lokacin harta canja gaba d’aya annurin fuskarta ya d’auke cak,
kallanshi ya mayar ga Umaira yace ” kai ke kuwa…! kin fiya zolaya,
ki koma wajen aikin ki, yayi maganar gabanshi na fad’uwa,
Umaira tace ” ka bari na tambayi Yaya Neehal abinda ke damunshi,
kasan ban san na ganku cikin damuwa,
ko matanku suka b’ata muku rai sai na rama muku,
tayi maganar tana nufar Neehal,
ido Najwah ta runtse da k’arfi dan in banda abinda ya faru da tuni ta shak’i wuyan Umaira,
” meke damunka Yaya ko Auntyn tawa ce ta b’ata min ranka….!?
Tayi maganar tana kallanshi ido cikin ido,
murmushi Neehal yayi mata danshi mutum ne mai faram-faram,
tabb…! abinda da wanda dama yake wuya, Hausawa sukace mai neman kuka idan aka jefe shi da kashin awaki sai yayi tayi,
dama abinka da wanda yake jiran kad’an ganin murmushin da Neehal ke yiwa Umaira,
ya hasala zuciyar Najwah matuk’a ranta yakai k’ololuwar b’aci,
ranta yayi mata zafi, k’irjinta ya shiga soya, mak’ogwaronta yayi mata d’aci yana mak’ak’i,
idanta suka koma asalin jajaye,
ganin haka yasa Nauman dakawa Umaira tsawa ” wai ke baki da hankali ne Umaira…..!?
“Baki ganin yanayinshi yana cikin damuwa….!?
” Ki rabu dashi……….!,
bai kai ga k’arasa fad’ar abinda yayi niyya ba suka ji k’arar mari tasss tassssss,
kafin su ankara Najwah ta d’auki kwalbar dake saman table d’in Nauman ta kwad’awa Umaira aka…………!
Umaira ta saki gigitacciyar k’ara gami da zubewa k’asa………!