NOVELSUncategorized
RAGGON MIJI 6-10

*Dedicated to SIS ZULAIHAT RANO*
a zaune kan roba-robar shi kallo daya tai mashi ta dauke idanunta, jikin bango ta jingina kanta na kallon sama ta cije baki saboda Marar ta data murda ,
Shi ko yana ganin fitowar ta ya mike tsaye yana gyara riga ganin ta jingina a bango tana ya mutsa fuska yasa shi jin badadi,
Bakomi yasa faseelat dauke kai ba se dan ganin kara jiya da yau, shadda ce jikinshi fara kall ya kawo farar hula akanta ga takalmi fari, wayaga balbela????
Shi gashi baki abin se ya dagule, itada tafito ganin canji se taga gara jiya, shaddar se sheki take tsabar fari.
Shi ko be samu ganin fuskar taba saboda kanta na facing up ganin Sun kusa minti ukku yasashi cewa “barka da fitowa”
Batare da ta sauke kanta ba ta dan juya shi ta zuba mai jajayen idanunta wanda suka kumbura saboda rashin barci da kukan da tasha ,
Yace “subhanallah, faseelat lpya kike? “
Ta juya sannan tace “ban lpya ”
Cikin jimami yace”miyasameki?”
Tace “fever”tana tabe baki.
Yace “ayyyah “da karfi wadda tasa seda ta mike daga jikin bango saboda yadda gabanta ya fadi, Ya cigaba da cewa “Allah shi sawwake shi baki lpya “
Faseelat kamar ta dora hannu aka tasa ihu haka takeji, ashe ba karamar illa takeso taiwa Kanta ba ko magana be iya ba, shi ga bahaushe wani abinda ta dan lura dashi shine kamar maganarshi daga hanci take fitowa.
yakatse mata tunani da cewa “ga wannan”
Ta kai kallonta ga ledojin da yake miko mata, daya babba daya karama, dan dole ta mika hannu ta amsa can ciki ciki tace “Nagode”yayi kamar be jiba sema yace “dama zuwa nai mugaisa gashi bakya jin dadi yanzu ni zantafi se munyi waya ga waya nan da sim da komi “
Batare da wata murna ba ta kalli ledar hannunta ta yamutsa fuska.
Yace “se anjima agaida ummi “
ta juya kawai ta shige gida tana saka da warwara , yadda zata kuma ganinshi in ya dawo dan kullum kara gano muninshi takeyi.
tana shiga gida ummi tayi shimfida kan barandar gidansu kafafunta a mike tana huce gajiyar hidimar da tasha, ta je ta kwanta kan kafafunta,
Ummi tace “sannu faseelat kode mutafi asibity? “
Ta girgiza Kai ummi ta kai dubanta ga ledojin da suke zube ta jawosu tana fadin “shi ya baki wannan?”
Faseelat ta daga kai idonta na kawo ruwa batare da ummi ta dubeta ba ta Fara bude ledojin, daya cosmetics ne kawai ciki, danginsu perfume, Nivea lotion, roll on, powder irin big pack dinnan wadda Zaka samu su concealer da foundation, da janbaki duk a ciki, se lip gloss.
dayar kuma waya ce ciki me suna infinix hot 6, ummi tace “aaa!masha Allah Allah yasa alheri, faseelat kinga kaya ko? “
faseelat da duk abinda zaa daga wani kululu ke tokare mata makoshi tace “ihhhhm “
Ummi tace “to ga waya faseelat tunda wayarki tasamu matsala har yau alhaji babba be aiko da wata ba toga khalil ya hutar dashi “
faseelat ta mike tsaye zata wuce dakinta dantagaji da jin maganganun ummi, kawai wayar tafara ringing, ummi tace “zo zo gashi har ya kira ashe a bude take “
Faseelat takoma ta amsa kamar zatai kuka tashige daki tana shiga ta danna ta a key dif ringing ya tsaya ummi duk a tunaninta faseelat ta dauki wayar ne, kiran na yankewa shiru be sake kira ba faseelat ta tabe baki,
Ta haye gado tana tunanin rayuwar da zatayi nangaba,
Hannunta ta dora kan kirjinta taji yadda yake fat..fat ta fara hawaye.
khalil yana be koma gida ba se 2pm dan daganan school ya wuce,
Yana shigarda mashin dinsa yayi hanyar dakinsa Hjy saratu da ke alwala zatai salla tabar alwalar tana bin bayanshi da kallo har ya kusa shigewa Hjy tace “kai zonan khalil”
ya juyo yaisa wurinta dan slope din dakinta da take kai anan ya zauna tana kallonshi tace “lpya kake naga ka dawo haka kamar marar lpya? “
ya cire hular kanshi yana fifita yace “Hjy naje gidansu faseelat na sameta bata da lpya sosai “
Hjyar tace “ummm se akai yaya? “
yace “shine nakeji nima bani lpyan “
Hjy saratu tai kasake tana kallonshi shi kuma dagaske yake maganarshi ,Hjy tace “to Allah ya sawwake ,saboda bata lpya shine kake wannan yaushin? kamar ba namiji ba, tashi da Allah kaban wuri “
Memakon ya tashi se yace “Hjy yaushe zakije ganinta? “
ta banka mai harara “se ran da na shirya “
“to me ze hana kije yau? “
Cikin haushi tace “saboda ban ga dama ba “
Ze kara magana tace “aa da Allah kyaleni fita xanyi yanzu idan na dawo zan biya ingano tan “
yace “tom “ya mike zakadai -zakadai ya shige dakinshi, wata kan jiya daga jiya zuwa yau faseelat ta zama wani bangare na cikin jikinshi, ku jifa ????kunsan irin su dasaurin shiga hannu ,
wayar shi ya fiddo a aljihu ya kara kiranta bata dauka ba faseelat lokacin ma batasan inda kanta yake ba dan gabadaya masassara ta rufeta tana cikin bargo tana kyarma lokacinma ummi na wurinta zaune tana jiran abba yazo su tafi asibity.
Koda kiran ya tsinke ajiye wayar yayi shi a kaidar shi baya missed call biyu, (audu ka’ida kenan)
Hmmm shifa ba ordinary mutum bane shi rayuwar shi daban take da yadda aka saba gani kude biyoni muji tasu salon soyayyar.
Au ????nayi mistake, kaso a soka ai shine so, kaso a ki ka fa?shi kuma me zaakirashi?
[7/12, 10:58 PM] Maman Mamy: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LBBVKSXqmrj3oaalNYWqmS
➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰
By
*MAMAN MAMY*
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION????????????~*
*~❄We beare’s of soon golden We writer’s assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*
7⃣
Dedicated to *SIS ZULAIHAT RANO*
Abba na zuwa ummi ta kama faseelat da temakon kaninta abul saboda ko tafiya bata iyayi ga zazzabi ga ciwon mara ga tension abun da yawa, har cikin mota akasakata, babansu yana da mota amma ta kwana biyu sede batayi tsufa can can ba ,yayan abba wanda sunansa salisu suna kiranshi baba babba ummi kuma na kiranshi alhaji babba mutum ne me kirki da arziki duk da de bawani arziki ne me yawa ba amma ba laifi tunda yana da zuciyar temakon yanuwan sa shi yakai su ummi hajji ya siya wa abba mota shine ya dauki nauyin karatun ya umar, kuma a gidansa yake zaune a Niger Republic din da yake shi alhaji salisun shima dan kasuwa ne yana yawan zuwa can shine yayi aure kuma yabar matar a can kasar.
Shi kuma abba tuni ya dena zuwa Niger din iyakar shi nan gida Nigeria duk da ummi can duk ilahirin dangin ta suke amma alhaji be bari ya zauna a wani gida ba se a gidanshi wannan kenan.
Asibiti suka kaita da zuwan su aka sa mata ledar ruwa, bayan allurai da aka mata,
Se bayan laasar ta farka likita ya shigo yana tambayarta mike damunta yanzu,
Jiki ba kwari tace “ciwon mara da nan “
Ta fada tana nuna setin zuciyarta likitan ya dan kura mata ido ta glass sannan yayi yan rubuce rubuce,
Ya juya wurin ummi da ke tsaye tanajin duk abinda ke faruwa yace “Hjy ire iren ciwon marannan inba aure akayiwa yaranba zeyi wuya ya barsu, sannan batun ciwon heart din rashin cin abinci ne da isashshen bacci wannan kesa ulcer ke kama mutum wuf daya, se akiyaye duk abinda na fada banda abu me tsami ko yaji ko mai da yawa arika bata abinci akai akai “ya juya bayan ya gama jawabin yana kara kallon faseelat,
ummi tace “insha Allah zaa kiyaye, kuma ankusa yin bikin ta ma “
Likitan ya Mike tsaye yana gyara ta kaddun hannunshi, shi da har ya fara tunanin ya samu ta ukku, matanshi biyu, ya killace a gida dukansu farare ne tass dan yanada gurin ajiye fararen mata kuma dukansu a asibity suka hadu daya ma kauye take daga amai da gudawa ya aure ta.
Fita daga dakin yayi yana fadin ,”Allah ya sawwake, “
ko da abba ya dawo hospital din samu yayi an sallame su dan lokacin kusan 6:40 ya biya Bill suka wuce gida.
Bakin wani pharmacy suka tsaya abba ya Shiga ya siyo magungunan da aka rubuta musu sannan suka wuce .
suna isa ummi takama faseelat suka fito har zuwa dakin ta ta kwantar daita malt da milk ta hado mata tasha tasha magunguna ta kwanta baadade ba bacci ya dauketa.
Can ana kiran sallan ishai se ga Hjy saratu kamar daga sama tana sallama ummi da fitowar ta wanka kenan ta amsa tana mata marhaba Hjy saratu ta shiga ummi tai mata iso har daki,
bayan sun gaisa take tambayar ummi ya me jiki?
ummi tace “dasauki dazunnan ma aka sallamomu daga asibity dan seda suka saka mata ruwa”
Hjy saratu tace “Abu beyi dadi ba Allah ya sawwake ya bata lpy ai tundazun naso zuwa se kuma na makara wajen fitar diyar kanwata ta haihu shine muka tafi suna tundazu inata so na taho se yanzu Allah yayi ina rokon Allah yabata lpy “
Ummi tace “amin”
Hiya saratu tace “tunda Khalil ya koma naga ne ba lpya ba dan kamar kwai ya fashe masa a ciki haka yayi “
Ummi tai dariya “khalil kenan ai dazun da yazo ya cika faseelat da abun arziki harda su waya a cikin kayan, Allah de ya kara budi na alheri “
Hjy saratu tace “amin amin,bari naje na dubata na wuce gida”
Suka mike suka fita zuwa dakin da faseelat ke kwance,
Har lokacin tana bacci ummi tace “bata tashiba kila cikin drugs da aka bata akwai na saka bacci ciki “
Hjy tace “to ni zanwuce Allah ya kara bada lpy “
Ummi tace “amin “
Ta na mata tattaki zuwa bakin kofa seda suka kai can ummi ta dawo ta shige daki ta’ida shiryawa, sannan tafito.
Ana gama isha’i duk suka hallara ummi takawo masu babbar cooler datake zuba musu abinci se plates da spoons suko sunbaje akan tabarma, kowa ya dibi nashi suka fara ci, Mubarak yace “ummi ni de nakoshi tunda yaya bata lpya”
Ummi tace “haba dan auta na, ka daure kaci ga faseelat can tana cin Nata itama “
Yace “dagasske ummi? “
Tace “eh kai sauri ka gama cika cikin ka se kaje wurinta yace to “yafara buga loma.
Su ummi basu dade da barin dakin ba tafarka ba laifi massaran ta sauka tun asibity ciwon ma ya lafa, sede ciwon da zuciyarta ke mata, baa jima ba taji wayarta na vibrate taja dogon tsoki kamar ba marar lpya ba afili tace “dan wahala”
Hjy saratu na’isa gida take bawa khalil labari tace “ashe haka faseelat ke jin jiki ?umminsu tace dazun har seda aka kwantar dasu asibity”
Yace “Hjy suna asibitin yanzu? “
Tace “a, a an sallamo su agida na samesu “
Ya tashi tsaye daga shi se jallabiya ga zungureriyar casbahar shi yana ja yace “bari na dawo hjy “
Hjy na kallonshi tace “kai dawo nan ina zaka? “
yace “yanzu zan dawo fa hjy gidansu zanje “
Tace “Kai baka da hankali da zaka je gidansu yanzu? “
Kawai ya juya “sena dawo “ya fice
Niko nace hjy barshi kinsan dogo dama be cika hankali ba ????????
Ya fidda babur dinshi yaja akan hanya ya tsaya wata supermarket ya siyi chivita da hollandia da malt da short cake da big biscuits gefen shagon ya siyi fruit irinsu orange, banana da pineapple
daya wuce gidansu, lokacin kusan karfe 10pm dan har Sun kulle gida ya yi parking machine dinsa ya fara kwankwasa gidan,
Be dade da fara kwankwasawa ba ishak ya fito bema sanshi ba hakanan yace masa “inayini “
Khalil yace “lpya lau, ya me jiki? “
ishak yace “dasauki “
Khalil yace “Allah shi kara afuwa, ga wannan ka kai mata “
Ya mika masa ledar ishak ya amsa yace “injiwa? Za a ce?”
Yace “khalil “
ishak ya juya yasaka sakata ya shiga cikin gidan abba da yake zaune shi ma yace “waye ne ?”
Ishak yace “yace khalil ne kuma yabada wannan yace abata “
Abba yace “kai ma ummi tana can wurinta
Ya juya zuwa dakin ummi kadai ya tadda tana gyara wa faseelat gado ita kuma tana toilet yace “ummi gashi inji khalil yace yana gaida me jiki “
Ummi tace “oh cikin darennan ya taso to kawo “
(function loadPageAds() { return afriPageAds({ ‘pid’: 8612, ‘uid’: 9740, ‘t’: ‘300 by 250’, ‘url’: ‘https://2gnblog.blogspot.com/’ }); }());
Ta amsa ta ajiye shi kuma ya fita baa jima ba faseelat tashigo dakin,
Wajen wardrobe dinta tawuce ta kimtsa kanta sannan ta dawo ta zauna kan bed.
Ummi tace “ga kayan marmari ankawo me zakisha? “
Faseelat tace “nakoshi ummi ruwan zafi kawai nakeso insha “
Ummi tace “to bari in je inhada miki amma ki tashi ga ayaba nan kici ko kadanne kinsan tana rage menstrual cramps “
Tace “to “
Ta amsa ta bare tana ci tana yamutsa fuska.
[7/12, 10:58 PM] Maman Mamy: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰
By *MAMAN MAMY*
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION????????????~*
*~❄We beare’s of soon golden We writer’s assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*
8⃣
Dedicated to *ZULAIHAT RANO*
Lokacin da ummi ta dawo har faseelat taci biyu, mika mata tea din ummi tayi tana fadin “bansa sugar ba amma nasa miki citta da yawa saboda tana koro jini da wuri “
Faseelat ta amsa “Nagode ummi “
Ummi ta zauna tana kallon faseelat tace “dazun Hjyarsu khalil tazo kina bacci tana gaidaki da jiki “
Faseelat tai shiru bata ce komi ba,
Ummi tace “baki tambayi wanda ya kawo miki fruit dinnan ba “
Faseelat ta kurbi tea tace “nayi zaton abba yakawo “
Ummi tace “a, a khalil ne ya kawosu yanzu da darannan “
Kuts-kuts ta zubdo tea din bakinta wani kuma ya sarketa tafara tari,
Ummi tace “kibi a sannu mana inya miki zafi kibarshi ya huce tukun “
Faseelat ta goge gefen bakinta taajiye copyn tea din tai shiru tana mamakin wane irin mutum ne khalil itade ba sakarmishi fuska take ba sannan bawani sabawa sukai ba ballatana ya dinga yi mata wadannan abubuwan,
Ummi ta katse mata tunani da cewa “kind ace da miji faseelat alamu duk sun nuna haka yaro me kunya da tarbiyya, duk dade bansan halinsa ba amma ina mai kyakykyawan zato, Dan Allah faseelat ki saki jikinki sosai naga tunda yazo kike ciwo bansaniba ko hakanan kika amsamin amma baki son auren shi “
Faseelat tace “ummi gaskiya na amince ne saboda kawai kiji dadi ba dan inason shi ba “
Ummi tace “ai nangaba zakiso shi “
Faseelat tace “hmmmmm “
ummi tai dariya “kiyi magana mana nasan nangaba ko ance auren hadi akai muku mutane bazasu yarda ba danni nasan nabaki many lessons daga tasowarki zuwa yanzu Wanda ko bankara da komi ba sunisheki zaman gidan miji, kuma kina da komai da zakija hankalin namiji dashi inde har kinmeda hankali mallake namiji baze miki wuya ba ,zaki so shi ki haifa masa yara Kema kizama uwa me koyarwa kamarni”ummi ta’ida maganar da murmushi fuskarta.
faseelat batace komi ba batasan komi ze faru nan gaba ba amma bata tunanin zataso khalil ko ta so shi bawani so sosai ba, saboda tadan fahimci wasu abubuwa dangane dashi.
Ummi ta katse shirun da cewa “ga kayanda ya kawo ki dauki abinda kikeso na kaiwa yanuwanki sauran “
Faseelat tace “ni nakoshi ki tafi dasu kawai “
Ummi tace “to ki sha tea din kar yayi sanyi kuma “ta dauki ledar tai waje
Faseelat ta yi tagumi ji yadda komi ya jagule mata lokaci daya saboda kawai ummi ta kamata tana wankan janaba inda bataganta ba bazata matsa mata haka akan aure ba, faseelat sede taji hawaye Sun zubomata anata abubuwa kamar gobe ne auren why?
ita tai kanta haka ne haka Allah ya halicceta mata nawa ne irinta? Maza nawa ne Irinta suma haka iyayensu ke matsa masu akan aure ko se ita dantana ya mace tilo gun mahaifiyarta? Ta share hawayenta tana daga kai cikin zuciyarta tace bazan kara zubda hawaye na akan batunnan ba zanyi kokarin hakan.
(yo anya zata iya?)
ummi nafita ta kaiwa abba kayan ya gani tace “me zaabaka? “
ya dauki hollandia yace “wannan yayi “
Ta tashi su ishak nata fira abul na gefe yana duba handout ummi ta zauna tsakiyarsu tace “Mubarak kawo wuka”
Ya tashi domin daukowa,
Abul ya kalli kayan “wai ummi waye ya kawo kayan nan “
Tace “kubakusan antinku aure zatayi ba? “
Ishak yace “wannan kai “
abul yace “yaakayi ne”
Ishak yace “lokacin da na bude gida naganshi tsaye ya bani tsoro dogo ne sosai nazata ma aljani ne “
Ummi ta rumtse masa baki da hannuwanta tace “ubanka so kake ka kara tunzura yayarku”ta juya tana kallon wajen dakinta
Abul ya kece da dariya ,”ummi kibarshi ya ida mana”
Ummi ta harareshi “kayi dede Allah yayi maka albarka “
daya daga cikin sirrin ummi ko wane laifi zaaimata sede tace Allah yayi albarka bata taba cewa komi fiye da wannan sede harara.
Mubarak ya dawo da wuka hannunshi yana mita wai wukar can karkashin kwandon wanke wanke ya ganta ummi tace “to me kauda kayan bata lpya se inta tashi tukun “ta yanka kayan marmarin suka fara sha sunayi suna labari.
Hjy najin motsin mashin din khalil tafito waje seda yayi parking tace “kai dogore seda kaje dinko? “
alhajinsu ya leko tunkan khalil yayi magana “ai gwara da yaje zasu kara ganin yadda take da mahimmanci a wurinshi “
Hjy ta rike haba “ah to yayi ka ganta ko? “
Yayi shiru ya shige daki.like mother like son wajen shegiyar tambayar yaya akayi aka haifi uwarka.
The following day…….
[7/12, 10:58 PM] Maman Mamy: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰
By
*MAMAN MAMY*
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION????????????~*
*~❄We beare’s of soon golden We writer’s assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*
9⃣
Dedicated to *sis Rano*
Ta kama ran Friday salla day awurinmu musulmai, bayan ya dawo daga masallaci da asuba ya shiga ya gaida Hjy ta amsa ciki -ciki yace “Hjy lpya? Ko nayi miki wani abu ne? “
tai shiru ya kara memetawa
Tace “da Allah tashi kaban wuri “
“Hjy dan Allah kiyi hakuri innayi miki laifi bada sani naba “
“bakasan laifin da kayi ba kenan? Jiya ban hana ka zuwa gidannan ba da daddare amma seda kaje, tunda kaje kaga yarinyar nan shikenan ba saura ba kingi duk ka zauce, aka gaya maka haka akeyi ? ko dama can kana santa bansaniba?”
Maganganun hjy sun matukar bashi mamaki yace “haba Hjy kefa kikayi wannan hadin ni ina zan santa ma bare na so ta, kuma ni wlh hjy banga wani abinda nikeyi ba dede ba, jiya kuma Banyi tunanin tafiya ta zata bata miki rai ba, kiyi hakuri “
Tace “to naji why kake ta kashe kudi har haka danna ce kai mata kyauta aiba cewa nai kaita kashe kudi ba .
Shiru yayi kanshi duke tambayar kanshi yake mi yasamu Hjyarsu.
can zuwa yace ” bawani kudi bane fa sosai waya kawai na siyo mata se cosmetics that’s all “
Ta Harare shi “eh ba kudi bane masu yawa tashi kaban wuri, ai gwara ayi ai auren ko kasamu kanka, ni wlh dama kauye naje nasamo maka yar yarinya”
ya tashi tsaye ya shafi sumar kanshi can zuwa yace “Allah yabaki hakuri “ya fita
Tace “amin”
Khalil kusan Karo sukayi da alhaji yayi saurin zukunnawa gaida shi alhaji ya amsa ya wuce ciki.
Khalil ya tashi ya tafi saboda shirin makaranta .
Alhaji yana shiga yafara wa hjy fada “wato de sararu bazaki bar halinki na banza ba ko? saboda nasan halinki fa shiyasa ban kara aure ba danna san duk wacce na aura kashe ta kadai ke bakiyi, yanzu kuma ga matar danki zaki koma, to kibi Ahankali wlh tun kafin yaronnan ya fahimci manufarki “
komi batace ba ta tabe baki a ranta tace “aini ma bansan haka yake ba nazata ze cigaba da halinsa na rashin son auren.
7:30 khalil ya fito da shirin shi yau kam yayi kyau wani yadi ne ash color yasa mishi bakar hula da bakin takalmi rigarde tazarce ce da alamu duk haka dinkunansa suke hular ma tayi gaban goshi sosai shima da alama haka yake saka hular shi, ya leka kitchen hjy se diminiya take dan kawai karyayi kalacin danwake ne zatayi amma tai nan tai nan batare da ya damu da rashin hada kalacin ba yace “Hjy natafi “
Tace “Allah ya bada saa “fuskarta ba yabo ba fallasa.
Ko damuwa beba ya bar gidan se sannan hjy tagama danwaken,
karfe 9 siyama ta shigo gidan tareda yaranta biyu “Fatima da farida “
hjy saratu tace “oyoyo oyoyo yan albarka “
siyama tana fara’a tace “hjy ina kwananku “
“lpy lau ya jikin kwana biyu da kikai ba lpy kamar kin kwana goma wajen sunan ramla se tambayarki suke “
Tace “eh wlh hjy amma jiya na aika mata da sako kuma Bayan kwana biyu zanje gidan na gano takwara, ai wlh naji jiki hjy danbana iya komi, abdulkadir ke komi har girki “
hjy tace “Allah yasa kaffara ne,”
siyama tace “amin su yaya ana makaranta “
hjy tace “uhm antafi ai yayanki ya kusa zama ango “
siyama na murna tace “dan Allah Hjy wacece yarinyar “
Hjy saratu tace “eh ba wata bace se faseelat “
Siyama tana murna tace “faseelat de wadda nasani Hjy? “
“itafa “
siyama tace “gaskiya naji dadi hjy Allah yasa alheri ai faseelat full option ce komi yaji, tana dariya tace “finally yaya zaayi aure “
Hjy tai dariya siyama ta mike tsaye “Hjy mi zaa dafa muku yau ?”
Hjy tace “komi kikayi yau de jumaa komiye de da miya zaki “
“ayi taliya da miya NE? “
Hjy tace “a, a kide yi shinkafa kinsan khalil beson taliya gwarama in anyita da safe shima se anci saa kawai kiyi shinkafar se ki dafa masa wake, dan kinsan shinkafar ma baya sonta ita kadai “
Tace “to “tai hanyar kitchen.
Khalil ko school ya wuce ,jss classes yake koyarwa duk jiki mace yake komi maganganun hjy nata mashi yawo yanata kara nazarin su,, ga rashin lpyar faseelat data dameshi.
12:30 aka tashi saboda sallan jumaa direct supervision store yawuce ya siyi su peak milk , bournvita,cornflakes,block sugar, golden moon da tea bag, da different sweet , kusa da wurin akwai oasis bakery ya saye big bottle ice cream da snacks ya nufi gidansu faseelat .
yana isa yayi dede da dawowar Mubarak daga school , Mubarak se kallonshi yake, khalil ya jawo shi “abokina zo mugaisa “
Mubarak de yayi tsaye yana kallonshi khalil hannunshi ya kamo yasaka a nashi yace “ummi na gida?”
Mubarak ya daga kai
Yace “yayar ku fa ya jikinta “
Mubarak yace “dasauki dan dazun naganta tafito zatai shara ummi ta hanata “
Yace “good kaje kafadawa ummi cewa khalil yazo yana so ze shigo ya gaidata “
Mubarak yace “to”
ya shige gida seda yafara shiga dakinsu ya ajiye jikkarsa sannan yaje ya fadawa ummi, ummi tarike baki “Allah sarki yaron kirki ,jeka ce ya shigo “har ya tafi tace “Mubarak dawo jirani “
tashige dakin faseelat, faseelat taji sauki sosai dan wayar da yabata tasaka wa tsohon sim dinta, tai checking balance babu kudi ciki tanayin Wanda ya kawo taga 1000 ta tabe baki ta siye data tayi download what’s up tai installing messages sunata shigowa ummi tashigo ,”ke ki tashi ki kimtsa ga khalil nan shigowa “
faseelat tace “khalil ?”tana zaro ido
Ummi tace “eh ki tashi gashinan shigowa “ta juya Tabar dakin faseelat tace “mtssww shikenan fa khalil khalil maganar kenan ta kalli riga da wandon dake jikinta fakistan tace “ni shirye nake danban kara irin gayunnan saboda shi “
Ummi nafita tace yashigo tashige daki ta sako hijab.
Tare da Mubarak suka shigo yana dauke da katuwar bakko,
Har bakin dakin ummi yayi sallama ummi ta amsa tace “maraba ka shigo “
ya dan sunkuya dukda tsayin kofar ya shiga memakon ya zauna kan kujera ya xube kasa, a sannu ummi ta saci kallonshi tace “kambuu da wannan ne faseelat ke kushewa ina laifinsa yanda mazannan sukayi tsada,
Ummi tace “a, a katashi kazauna saman kujera “tana sunkuyar da kai na surukai,
Yace “ina yini, “batare da yakoma ma waccan maganar ba.
Ummi ta amsa akunyace yace “ya me jiki? “
Ummi tace “dasauki “
yace “Allah shi bata lpy dama zuwa nai nagaisheku”kanshi a kasa shima kunyar yakeji
Ummi tace ” amin angode kwarai “
Dama da shigowar shi ya jingina bakkon jikin cushion hannunshi ya cusa cikin aljihu ya zaro kudi a kalla sunkai 10 ya ajiye sannan yace”ni zanwuce “
Ummi tace “to angode bari na kira maka faseelat din “
Bece komi ba ummi tafita Mubarak de na zaune ummi nashiga tacewa faseelat “ki tashi ki shiga ku gaisa “
faseelat da tunda taji sallamar shi taji zazzabi ya fara rufeta ta tashi tafita kamar me koyon tafiya,
Ummi tace “yar rainin hankali har ciwon ya dawo ko “
Faseelat ta shiga da sallama bakinta, wani sanyi ya mamaye zuciyar khalil ya dago kananun idanunsa ya zuba mata, kallo daya ta masa ta samu kujera ta zauna.
Yace “inawuni malama faseelat,”faseelat ta kalli zungure riyar hijab din dake jikinta tai shiru,
yanata kallonta yace “ya jiki?”
ta lumshe ido ta bude tace “naji sauki ai “
Yace “da sauki zaki ce de, tunda baki warware ba “
Tai shiru
Yace “to Allah yasa kaffarane “
Tace “amin “kasa-kasa
Ta dago ta saci kallonshi Sukai 4 eyes seda gabanta ya fadi ta rasa wane irin kallo yake mata, shiko kallon luv ne yakeyi, to da yake de sabon shiga ne se kallon yayi kama da kallon ruruwa????????♀Inajin harda kallon luv se kun koya mishi ????
Faseelat ta kauda kai sannan ta dago ta kara kallonshi lokacin ya dauke ido yana magana da Mubarak harda kudi ya bashi, wannan ya bata damar kallon dressing nashi a zuciyarta tace not bad,
Ya mike tsaye yana jifanta da wannan kallon yace “ni zanwuce “
tafara wasa da hannunta,
yace “ba bankwana?”
Tai shiru yace “to natafi amma plss ki rika daukar kira na i have called you several times but you don’t pick my calls why? “
Faseelat seda murmushi ya kufce mata saboda jindadi atleast de yana iya kwantar da murya wajen pleading kuma ya iya turanci daya daga cikin abunda take so wajen mijinta.
akan idonsa tai murmushin wani farinciki ya mamaye shi ganin smile a fuskar ta,
Yace “I’m pleading I hope you will accept my request “
kawai ta girgiza kai dariya tazo kufcemata ta jawo hijabinta ta rufe fuskarta.
yayi dariya yafita ummi bata waje danhaka yawuce har kofar gida Mubarak ya rakashi khalil nata masa labarai,.
Yana wucewa Mubarak ya shigo gidan dede fitowar faseelat daga dakin taci dariyarta se kuma daga karshe ta dinga buga tsoki,
sukayi kicibus da ummi.
Mubarak yace “gaskiya ummi yana da kirki sosai jibi kudinda ya bani “ya fiddo yan 200 guda biyar da yabashi sabbi fill
Ummi batabi kan maganar shi ba hankalin ta na kan faseelat daketa murmushi ummi tace “wai lpya kike ta dariya ke daya “
Faseelat ta daure fuska “bakomi “tashige daki da sauri
Ummi tace “hmmm Allah ya shirya ki “
Ta Shiga dakinta, tana zare hijabin jikinta ta jawo bakkon ta bude kaya niki -niki, ta fiddo Ice cream da snacks din ta ajiye gefe guda,
Kudin da ya ajiye ta kirga nera dubu goma ciff ummi tai murmushi ta jawo wayarta tace “bari na kira hjy saratu nai mata godiya “
Batare da tunanin komi ba ta dannawa lambarta kira…..
[7/12, 10:58 PM] Maman Mamy: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰
By
*MAMAN MAMY*
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION????????????~*
*~❄We beare’s of soon golden We writer’s assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*
????
Ringing biyu Hjy saratu ta daga bayan gaishe gaishe ummi tace “yanzu khalil ya fita yashigo har gida mungaisa, mun gode da abun arziki “
Hjy saratu tana ta faraa kamar duka knan tace “ah bakomi wlh ai anzama miye aciki “
Sukai bankwana ummi Nata godiya sede bata fada mata yakawo wani abu ba Hjy saratu tace “hmmm yanzu haka wani abun ya kai musu, kowa na haramar tafiya masallaci shi yanata surukai,” taja dogon numfashi “nasan abinda zanyi komi zezo karshe “
Shi ko khalil masallaci ya wuce daga gidansu faseelat, hankali kwance, gabadaya jiyake kamar bashi ba, soyayya ta fara sauya masa rayuwa.
Faseelat kau seda ta shiga daki ta kara jan tsaki “komiye na mishi dariya ma? Nan fa se yayi tunanin tafara sonshi ne “ta kara jan tsoki,
Ta jawo wayarta messages sungama shigowa abinda ta lura groups dinta Sun ragu dama inka dade baka online groups fita suke, bin groups din tafara yi taga wadanda suka fitar daita,
Taga kusan group bakwai ta fita, se tafara bin numbers dinta tayi wa friend dinta magana a medata wasu ,akwai wani group sirrin mu mata, shi ta fara shiga saboda tanajin dadin group din, messages din wasu Sun bude wasu basu bude ba, tatura sallama ,suka amsa tace “plss masu group suyi adding dina ko abada number ta asani nadade bani online ne “
Se akafara mata reply da welcome masu turo sticker na turowa, wata me suna maman amira tace akwai wani group amma se kinbiya 500 ake adding naki ana karuwa sosai ciki,
faseelat tace “anayin share and self? “
Maman amira ta turo mata “eh anayi, Ko kati ko BTU ko transfer “
Faseelat tace “kiban no din admin zantura mishi through share and self saboda banda kudi “
maman amira tace “ayya zan biyamiki asaki ki dan jira “
Faseelat tace “amma de Nagode aunty Allah yaraya amira “
maman amira ta turo mata smile face.
daganan faseelat tai taganin new groups na matan aure wasu na novels ana sakata,
Seta bi maman amira PC tana mata godiya maman amira tace karkidamu sister sunanki kawai ya burgeni ,faseelat tace zan’iya adding number dinki?
maman amira tace”yes zakiiya nima zanyi adding taki “
Faseelat ta tura mata thanks you” (the Fateful relationship just begun)
Ko minti 10 baaiba akayi adding nata ta tura” slm “
Maman amira taturo “you are highly welcome friend “
Faseelat tace “I’m grateful “
Fitowa tai a group din tafara bin status daya bayan daya sannan ta sauka online,
fitsari ne ya matseta ta tashi tafita waje dasauri,
Ummi tagani tafito daga kitchen hiyaki ya korota, tai sauri tashige toilet ta biya bukata ta dawo, ta tafi gun ummi “ummi for god sake miyasa kikeson wahalar da kanki nace naji sauki kibari nayi “
ummi tace “ai gwara narinka shiga ciki ko na saba tunda tafiya zaki kibarni ni daya “
Faseelat tace “eh naji amma bari nashiga inbani nan kyayi din “
Ta kutsa kai kitchen din duk da hiyakinsa inda sabo ta saba .
Hjy saratu kau alhaji ta dannawa kira, bayan ya amsa yace “lpy de ko kira gab Shiga salla “
Tace “eh dama so nike ince maka inason zamuyi magana inka dawo “
yace “To saurin mi akeyi da antaso masallaci zanshigo gidan “
Ko to batace ba ta yanke kiran,
Siyama ta fito daga kitchen tana kai abinci daki har ta gama sannan ta zauna tana “wash Allah na “
Hjy ta kure ta da ido tace “wannan dan aikin? To ko de ciki gareki “
Siyama tai murmushi batare da tace komi ba,
Hjy tai dariya “to Allah ya raba lpy “
Siyama tai tsit can tace “bari naje nai salla “
Hjy tace “har lokaci yayi ne “
Tace “eh karfe 1:40pm”
Hjy tace “bari mutashi muma “
Ana saukowa masallaci alhaji ya taho gida yana shiga da sallama bakinsa yaran siyama suka gudu suka tarboshi ya tallabo kawunansu sukayi ciki, yanata jindadi,
Dakinshi ya wuce kai tsaye ya rage kayan jikinshi ya dan kishingida sega siyama takawo masa abincinsa suka gaisa ya mata ya jiki ta fita tareda yaran.
Yana tsakiyar cin abinci Hjy tashigo ta zauna sannan tace “sannu da zuwa “
yace “yawwa yana Kai loma bakinsa “
yace “wai maganar mi cece da baajira na dawo “
Tace “dama bawata magana bace seta khalil da faseelat “
Ya ajiye cokalin hannunsa yace “inajinki”
Tace “nace mi zaihana akai kudin neman aurensu tunda de akwai su, bayan ansa rana se su cigaba da fahimtar juna kafin auren, nasan shima khalil din zeso hakan.”
yadanyi nazari for some minutes sannan yace “yanzu de kifara yiwa mamanta maganar duk yadda kukai se inji saboda kamar abun yayi wuri “
Tace “haba bawani matsala amma bari na kirata “
ta kwalawa siyama kira tace mata ta miko mata wayarta, takawo mata ta juya.
hjy tayi dialing number ummi
Tadanyi ringing sannan ummi ta dauka da sallama,
Hjy tace “kinga na sake kira ko,dama maganar yarannan ce to munyi magana da alhaji kiyi magana da abbansu in anbada izini zaaturo “
Ummi tace “to ba matsala nasan yanakan hanyar dawowa Inya dawo zamuyi maganar duk yadda mukayi zakiji “
Hjy tace “to Nagode kwarai se na jiki “
Ta yanke kiran
Alhaji bece komi ba ya cigaba da cin abincinsa.
Khalil siyama nafita ya shigo tafara zaulayar shi, yana dariya yace “siyama bakiji ni kuma ake zolaya? Ni yayan. “
Tace “hmm yaya kenan ,yanzu de kabar number anty ta mufara gaisawa “
yace “zanbaki amma ba yanzu ba, kije ki daukomun abinci na tukun inna gama se muyi maganar “
Ta kawo masa abincin yafara ci dan mutuminnaku be wasa da k’oto.
Seda ummi tabari abba yagama cika cikinsa da daddadan abincin da faseelat ta dafa sannan tafada mishi yadda akai yace “kunde nace ga hadin nan auren hadi matsala ne dashi in aka samu sabani, “
Ummi tace “insha Allah bawata matsala”
Yace “to yanzu de su bamu lokaci kamar nanda sati daya, dan inaso nayi bincike, bama wannan ba ita faseelat din ta amince ne? “
Ummi tace “eh mana ko akirata ka tambayeta? “
Yace “eh kiramin ita “
Ummi tatashi ta fita kiranta daga can bata dawo dakinba,
Faseelat ta zauna “gani abba”
ya kalleta sannan yace “kinji iyayen khalil zasu aiko me kikace? “
Faseelat gabanta ba karamin faduwa yayi ba tai shiru ta sadda kai kasa,
Abba yace “kin amince? Yanzu kina sonshin? “
Kuka ne yazowa faseelat tai saurin rufe fuskarta da hijabin jikinta,
Abba yayi tunanin ko kunya ce yace “to tashi kije? “
Ta tashi da gudu tashiga dakinta ta fara kuka me cin rai.