LabaraiSadiya Faruk

N5,000 ta sauya rayuwar masu rauni a Kasar nan Sadiya Faruk

Ministar ta kara da cewa tunanin ’yan boko ne cewa N5,000 da ake ba wa talakawa masu ya yi kadan ya fitar da su daga kangin fatara.

Ta bayyana haka ne bayan an tambaye ta hikimar N5,000 da gwamnati ke ba wa talakawa a duk wata da nufin fitar da ’yan Najeriya miliyan 100 daga kangin talauci.

A cewarta, ma’aikatarta ta shaida yadda N5,000 din — da wasu suka raina — da ake biyan talakawa masu rauni ke taimakawa wajen fitar da su daga matsancin talauci.

“Mutanen da ake ba wa N5,000 din tana da matukar muhimmacni a gare su, domin talakawa ne masu rauni, kuma tana kyautata musu rayuwa,” inji ta.

Ta ce duk da haka akwai ’yan Najeriya, “Irina da irinku N5,000 ba ta kai kudin katin da muke sa wa a wayoyinmu ba —bambancin ke nan.

“Amma talakawa masu rauni a karkara har suna iya ajiye wani abu daga cikin N5,000 din da ake ba su; Idan har kudin ba ya yi musu komai, ai ba tilasa su ake yi su rika yin adashin N1,000 ba. Saboda haka N5,000 tana taimakawa.

“Duk wanda ya ce N5000 ta yi kadan, to tunanin ’yan boko gare shi, domin mu ganau ne, mun je yankunan karkara, mun ga mutanen da idan aka ba su N5,000 har kuka suke yi, saboda ba su taba samun ta ba a rayuwarsu.

“Saboda haka kudin na taimakawa wajen inganta rayuwarsu daga wani mataki zuwa wani wanda ya fi shi,” inji ministar.

Ministar ta bayyana cewa matsalar tsaro da ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas da sauran wurare ya kara kawo bukatar agaza wa mutane a Najeriya.

Daga Aminiya

 

               

[ad_2]

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button