WUTSIYAR RAKUMI 39

*_NO. 39_*
……….Abdul-Waheed dai ya tafi yabar Ummukulsoom da nazari, gashi Bily ce abokiyar shawarar amma ta botsare mata, maman Ahmad kuma yaya Attahir na gida, shiyyasa babu sakewa sosai.
Kiran da baba ya sake matane ya saka hankalinta tashi, dan kuma jaddada mata maganar yakeyi, hakan yasakata fahimta lallai akwai abinda ke faruwa baba na ɓoye mata, anya ba magar bata da aure bane ya fasu kuwa?.
Tasan a bakin murja kawai zata iya samun ƙarin bayani, itakuma sai mijinta na gida suke iya gaisawa. Wayarta ta ɗauka ta kirashi, cikin sa’a kuwa ta shaiga. Bayan ya ɗaga daga can suka gaisa, kafin ta tambayi ƴar uwarta.
Daga can yace, “Kash aiko Umma ansamu akasi, dan jiya-jiya na baro gida yanzu haka ina nan kan hanyar legas, amma itama fa shekaran jiya ta nemeki bamu sameki ba ne saboda natuwak”.
Cike da zumuɗi, Ummu tace, “ALLAH saiki, lafiya dai ko?”.
Jimm yayi kafin yace, “Eh to da sauƙi kam, wata dai ƴar magana ce keta yawo a gari akanki”.
“A kaina kuma? Tami kenan?”.
Shiru yay kamar bazaice komaiba.
“Inajinka, karkaji komai ka sanarmin dan ALLAH”.
Cike da jin nauyinta yace, “Umma kiyi haƙuri, haka aketa cewa wai aurenki ya mutu, randa aka kaiki a washe gari mijin ya sakeki amma shine baba yarufe yaƙi faɗa, kuma wai….”
Hawayene suka cika idanun Ummukulsoom, haba itakam tayi mamakin azalzalarta da baba keyi a tsakanin nan akan batun aure, bata bukatar jin ƙarshen zancen dan haka kawai ta yanke wayar tana haɗiye kukanta, zuciyarta taf da mamakin ya akai wannan maganar ta fito a ɗilau? Gashi harma an canja salon zancen gaba ɗaya.
Zafin da kanta ya ɗaukane ba tare da tunanin komaiba ta turama A-Waheed saƙo akan ta amince ya tura magabatansa kawai.
Tana turawa ta kashe wayarta gaba ɗaya ranta duk a matuƙar dagule.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
A ɓangaren basiru kuwa tun daga wannan ranar Abu yaketa bin duk hanyar da zata sadashi dashi koda suna tare da Meenal ne, ahankali sai shaƙuwa ta fara shiga tsakaninsu, basiru ya fara sakin jiki da Abu, bakomai yasa Meenal ƙyalesu ba sai fahimtar da tayi shima Abu ɗan masu farcen susa ne, ita haka kawai ma sai taji ya kwanta mata a rai, dan shima yaron babu laifi akwai kala.
Yau ma dai tare suka fito yawo a motar Abu, danshi baseeru fa inhar bada Meenal zai fita ba koyaushe take bashi mota ba, hakan na ɓata ransa, balle idan ya kalli jibga-jibgan motocin meenal ɗin dake a harabar gidan, ɗan gidan gwamnatin ma ƙiri da muzu saidai taje ita kaɗai shi banda shi, kusan yanzu ma acan take yini ita.
Tunma yana nuna mata sha’awar son zuwa tana basar dashi harya haƙura ya ɗauke hankalinsa a wajen badan bayajin haushiba, sai dan kawai yana ƙaunartane da iya gaskiyarsa, sam bayason abinda zai ɓata ranta.
Wani ƙaton boutique Abu ya kaisu na ƴaƴan manya, kayane na samari ƴan ƙwalisa masu shegen tsada da ƙyau, shi kansa Basiru saida ya rikice da wajen tamkar ba a cikin katsina ba.
Duk yanda yaso karya ɗauki komai saboda tattalin arziƙinsa bai kaiba sai da Abu ya matsa masa, gudun kar Abu yay masa kallon raini bayan yaga gidan daya masa ƙarya matsayin nasa saiya biye masa suka ɗiba kaya sosai.
Bayan sun kammala sukaje wajen biyan kuɗi, na Abu aka fara dubawa, ana faɗa masa ya miƙa ATM aka cire.
Sai kuma oga Basiru, bayan ta kammala dubawa.
Tace, “Kuɗinka 2.3m… Ne”
Matar ta faɗa tana kallon basiru dake danna waya ya wani basar sai shan ƙamshi yakeyi, shi a dole babban yaro.
Wani irin mugun wantsalawa hanjin cikinsa sukai, tuni zufa ta fara tsatstsafowa goshinsa, ya fara laluben aljihu cike da basarwa tamkar yana neman ATM.
Zulfah dake laɓe tana kallon komai tai murmushin ƙeta tana fitowa cike da takun ƙasaita, ATM ta miƙama matar tana nuna mata kayan basiru,
“Ki cire kuɗin kayansa”.
“Ok ma” mai karɓar kuɗi ta faɗa tana karɓar ATM.
Basiru ya kalli Zulfah yana wani cijewa, “Ji mana hajiya, bana buƙata”.
Zulfah tai masa wani kallon raini ta cikin eyeglasess ɗinta baƙi dan tasan baya ganinta, sai dai kuma fuskarta ɗauke take da murmushi a zahiri.
Ko cikanka batace masaba ta karɓi ATM ɗinta tabar wajen tana ɗaga masa yatsu biyu alamar bye.
Ƙafafunsa sunyi sanyi ƙalau tamkar an makesa, har Zulfah ta fice daga wajen.
Abu ya matso kamar baisan komaiba yana faɗin, “Woow, wannan bab ɗinfa my man?”.
Cike da basarwa basiru ya taɓe baki yana faɗin “ohoma ƴar wahala”.
Dariya Abu yay a zuciyarsa, afili kuma yace, “Koma dai miye kaci banza, aiba kai kace ta biya makaba”.
Tsaki basiru yaja kamar gaske, nanko a zuciyarsa jiyake kamar yafara taka rawa, “Kai nifa bazan ɗauki kayannanba, inma na ɗauka ƙyauta zanyi dasu”.
“Ƙyauta kuma? Dan ALLAH karkayi haka abokina, ka saka abunka tunda dai mu muka zaɓa abinmu ai”.
“shikenan, ammafa dan kaine zan saka, duk randa muka sake haɗuwa kuma zan bata kuɗinta”.
“Yauwa to hakanma dai nake ganin zaifi”. Cewar Abu yana matse dariyarsa da ƙyar.
Kayan aka fidda musu, Zulfah naganin sun fice ta fito ta dawo cikin boutique ɗin.
Hannu ta bama matar suka tafa tana mata godiya, dama komai sunyisane cikin shiri, kayanma Abu ne yayta nuna masa wanda zai zaɓa bisa ga shirinsu.
Godiya Zulfah ta sake mata ta fice.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
*_KD_*
Idanu Dad ya kafe Attahir dasu kafin ya nisa yana gyara zama da maida hankalinsa ga Abba.
“Humm Attahir kenan, bayan na koreka shine kaje ka ɗakkomin Aminina?”.
Murmushi Alhaji Abubakar yayi, “To tinda anƙi sauraren buƙatar ɗana badole aje a kinkimoni ba Alhaji Mahmud ”.
“Alhaji Abubakar ka barni da yarannan, yanzu shi Fodio har idonsa yakai tsaurin da zai aikomin Attahiru akan yasamu matar aure? Bayan kuma a gabanka ya watsamin ƙasa a ido? Toni minene nawa kuma yanzu Alhaji Abubakar?, tunda rayuwar da yaga ya zaɓama kansa kenan basai yayiba”.
Cikin kwantar da murya Attahir yace, “Kayi haƙuri Dad, wlhy nima da farko naƙi saurarensa sam, amma fahimtar danai yana cikin damuwa sai naga ya kamata na sanar muku”.
“Attahiru ka barsa ya dawwama cikin damuwarsa da….”
“A’a ba ayi hakaba Alhaji Mahmad, Kayi hakuri dan ALLAH, Inaga mu ɗauki hakan matsayin ƙaddara kawai, tunda itama yanzu aurenta ma zatayi, tunda harya nuna auren yake sonyi mu sake bashi dama, yanzu dai ai zaɓinsa zai kawo”.
“Alhaji Abubakar nifa nariga na zare hannu gameda auren Fodio, inhar zai tsufa a haka baiyiba ya rage nasa”.
“A dai yi haƙuri, kai Attahiru a ina yarinyar da ya ke son take ne?”.
“Wlhy Abba ban sani ba nima, dan yaki gayamin wacece yake son, duk sanda na tambayesa sai yace min koma wacece zan gani”.
“Kaji ba Alhaji Abubakar, duk yanda kake zaton tsaurin idon Fodio ya wuce nan, yanzu haka ɗiyar dangin yarabawan ya sake kwaso muku?”.
Murmushi Abba yayi yana faɗin, “Kai Attahiru tashi kaje, zuwa ƙarshen sati kuzo tare dashi idan zakazo amsar kuɗin su mai sunan Hajiya”.
“To Abba godiya muke, Dad ALLAH ya ƙara girma, ayi hakuri damu dan ALLAH a gafarcemu”.
“Yo Attahir da ba’a haƙuri daku ai da tuni kun shiga wani hali, ALLAH ya ƙara shiryawa”.
“Amin” Abba ya faɗa.
Bayan fitar Attahir Alhaji Abubakar ya kalli Alhaji Mahmud yana fadin, “Mu cire komai a ranmu dan ALLAH Alhaji Mahmud, mu ɗauki komai matsayin ƙaddara, kuma kaga bayan faruwar abun ya nuna nadamarsa, danma kaine kaƙi bashi dama da wlhy komai ya daidaita”.
“Shikenan Alhaji Abubakar ALLAH ya shiryesa, amma maganar komai ya daidaita ma ai bata tasoba, yariga da yabar shirin tun rani, shima kuma yasan bana magana biyu, ba gashi ALLAH ya bata wanda ya fisa ba”.
“Ba mace haka da sauri ba ai, tunda itama sai ƙarshen satin nan zasu kawo kuɗin nata, har yanzu bamuga wanene mijinba, duk da dai binciken Attahir ya nuna yaron mutumin kirkine”.
“Alhmdllh, ai nama fiso tafara aure kafin shi yayi, dan sam banso maganar auren nasuma ya shigo kusan time ɗaya ba wlhy”.
Murmushi Alhaji Abubakar yayi, “Aƙara hakuri damu dai to dan ALLAH, kasan ɗan nawane ɗan gado, sai dai shi harya zarta ne kawai”.
Dariya sukayi irin tasu ta manya.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
A ranar Attahir ya koma Lagos, dama kuma ranar yazo.
Basu sami haɗuwa da Amaan ba sai dare, kaf yanda sukayi da Dad ya zayyane masa, buyagin da Dad yay masa naƙin saurarensa sam da farko, da Momcy ma ta saka baki wajen roƙonsa sai abin yaso dagulewa, sai da yaje yakira Abba sannan Dad ya sauraresu, “yanzu dai haka yace weekend ɗinnan mu koma, kasan nima zanje saboda kuɗin auren yarannan da za’a kawo gida”.
A wani irin yanayi Amaan yake kallon Attahir, ya lumshe idanunsa ya buɗe yana turo iska ta bakinsa, “ALLAH ya kaimu”. ya faɗa da ƙyar’.
Attahir yay ƴar dariya, “Nifa mamaki kake bani matuƙa gaya Ajiwa, wai kaine kake faɗin da bakinka kanason yin aure yanzu, tuzurancin ne ya isheka halan?”.
Harara ya dallama Attahir yana ɗauke kansa.
“Oh hararata ma kake? Ai na gama maka mai wahalar shiyyasa, amma gobema ai ranace”.
“Ta jibima ta fita, dalla malam tashi kaje ka isheni da magana”.
“Kutmelesy, Ajiwa ni ɗin? A lallai kaci abinci, wlhy zakasan dani kayi”.
Murmushi ya saki yana kallon Attahir ɗin, har cikin ransa yana ƙaunar Attahir fiye da tunanin mai hasashe, yana jinsa matuƙa a cikin jikinsa da zuciyarsa matsayin ɗan uwa, amini na hakiƙa.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Tsakanin Ummukulsoom da A-Waheed kam yanzu kullum sai sunyi waya, duk dai hirar bata wani kirki akeba, yafi sakewa yay mata magana ta chart, ita da bata damu da charting ba sai yafara zame mata jiki yanzun, ga karatu yasha kanta sosai, saboda suna gangarar ƙarewa.
Lamarin Umar ne kuma ke ɗaure kanta, yana gombe abunsa ya makale, koda yaushe sukai waya saiya ce mata wani uzurine ya riƙesa, abinda ta fahimta daga garesa dai kam akwai matsala, yana ɓoye matane kawai.
Ƙyalesa tayi batare da ta takura kanta damuwar ta saniba, sai dai takan shiga damuwa idan ta tuna taya zata fuskancesa da zancen zata auri waninsa ba shiba.
★★★★
Ranar juma’a sukai shirin tafiya kaduna su duka gidan har Zaid Kamar yanda Abba ya umarcesu, dan za’aje a amshi kuɗin auren su, kuma sosuke su dawo ranar lahadi da safe kodan makarantar Ummukulsoom da Ahmad.
★★★★
“Big daddy!” Ahmad ya faɗa yana fincike hannunsa daga cikin na Ummukulsoom ya nufi Amaan dake fitowa a mota.
Duk da Ummukulsoom ta fahimci wanene ko kallon wajen bataiba, ta cigaba da danne-dannenta a waya, saima masifa take da zuciyarta akan shikuma waya gayyacesa?.
Ko da yake ita hakanma ya mata daɗi, ai koba komai zaisha takaici, dan ta ɗauki alwashin saita ƙunsa masa ƙaton haushi, harma Abdul-Waheed zata gayyato ta kaisa har gidansu.
Shima dai kallo ɗaya yay mata ya janye idanunsa, ko a jirgin ma can nesa dasu ya zauna.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡
“Alhaji Mahmud nadai sake dawowa”.
Dad ya kalli Alhaji Abubakar yana murmushi, “To ALLAH yasa ƙyauta kazo kaimin”.
Dariya Abba yayi, “indai ƙyautace karka damu zan maka da wata bazawara”.
“A lallai ka iya ƙyauta, amma a wannan shekarun ina mu ina wasu mata, waɗan nan dai sun ishemu ai karasa gwagwarmayar rayuwa”.
“Gaskiya kam. Akan maganar ɗana ne na dawo, yau kasan zasu iso insha ALLAH, ni aganina tunda har sun bashi izinin tura magabatansa kawai gobe idan ALLAH ya kaimu bayan an amsa na ƙannen nasu kawai sai mukai nasa dana zaidu ko”.
“Da wuri haka Alhaji Abubakar? Aini sonake ku barshi ya wajigu harma ayi bikin ƴata sannan”.
“A’a ba’ayi hakaba Alhaji Mahmud, mudaije a ajiye magana, wataƙilama su basu shirya anan kusaba, suko mai sunan hajiya banaso ya wuce wata ɗaya wlhy, tunda kaga wata ɗaya dawasu kwanakine suka rage mata ta kammala karatunta”.
“To ai ni banida ta cewa tunda ka ɗaɗɗaureni da jijiyar wuya mai ɗa, ALLAH ya kaimu goben”.
“Amin ya rabbi, nagode sosai”.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Koda suka iso kd Amaan isa ne yaje ya ɗaukesa ya wuce gida dashi, sukuma su Attahir Ummi ce da kanta taje ta kwasosu tare da direban Hajiya yaya.
Yau dai kam gida ya kacame da hayaniya, masu shi sun raya shi, adaren sukaje gidan Hajiya yaya, gwaggo hinde ma tana nan dan Hajiya yaya tace bata barinta ta koma, sai dai su ringayin watanni anan kaduna, suje ɗilau ma tare.
To bayan su Ummukulsoom sun baro su Hajiya yaya acan da ta tashi tahowa sai suka kuma dawowa a tare nan kd, bayan tayi kusan wata uku a ɗilau.
Basu baro gidan Hajiya yaya ba sai kusan sha dayan dare, suna dawowa gida kowa ya gaji, ma kwanci duk suka nema.
Cikin barcin da Ummukulsoom ta farane taji wayarta na ring, ɗagawa tayi dan tasan bazai wuce Abdul-wahed ne ba mai kiran.
Ilai kuwa shine, Sallama tayi cikin yanayin barci.
Da ƙyar ya iya controling kansa ya amsa mata, dan gaba ɗaya muryar tata tayi mugun saukar masa da kasala.
Murya can a ƙasan maƙoshi yace, “har kinyi barcine?”.
“Eh wlhy. kasanfa a matukar gajiye nake da tafiyarnan”.
“Lallai ke dai raguwa ce, tafiyar mintuna zuwa awa ɗaya kikema raki”.
“ALLAH bazaka ganeba”.
Guntun murmushi yayi daga can, “Ok ki kwana lfy”.
“Kai sai gobe zaka iso kenan?”.
“Jirgi ɗaya muka hawo ma” ya faɗa ƙasa-ƙasa.
Hakan yasa Ummu batajiba, tace, “Kace mi?”.
“Kinga yi barcinki”. Yay maganar yana yanke kiran.
Baki ta taɓe kawai ta tura wayar ƙarkashin filon ta gyara kwanciyarta.
*_Washe gari_*
Tunda suka karya basu zaunaba, gyaran gidan suka farayi aka shiga haɗama baki ɗan abun motsa baki mai sauƙi.
Da yake suna da yawa dandanan suka kammala komai kowa yay wanka aka zauna zaman jiran isowarsu.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
“Ni dai Fodio dan kakine kawai, amma yarinyar nan ta gidan Alhaji Abubakar nai maka sha’awarta, to kai matsalarka babu mai tanƙwaraka ne”.
Fararen idanunsa ya ɗago ya kalleta, “Momcy itama wannan ɗin zaki sota ne”.
“ALLAH yasa, nidai fatana kar a daɓa irin aurenka na farko”.
Bai ce komaiba dukda sarai ya jita.
“Kanajina fa ina magana”.
“To ni Momcy mizance”.
Harara ta zabga masa, kafin tayi magana Dad ya sakko cikin shirin tafiya gidansu Attahir.
Kallo ɗaya yayma Amaan ya ɗauke kansa, “Saika turama babanka Abubakar adress ɗin gidan yace”.
Kansa a sunkiye yace, “To Dad nagode”.
Banza Dad yay masa ya fice abinsa, Hajiya Jamila ta taɓe baki tana mikewa tabi bayansa.
Koda ta dawo daga rakiyar Dad ta dawo falon saita iske Amaan ya gudu.
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
Ƙarfe sha ɗaya da wasu mintuna iyayen Muhseen suka iso, tarbace ta mutunta juna ta gudana a tsakaninsu, abinka da manya dattijan ƙwarai, komai ya gudana cikin aminci, babu wani ja’inja aka tsaida ranar ɗaurin aure jin a shirye suke tsaf, dan atake anan suka bada har sadaki.
Hakan yayima kowa daɗi, aka rabu cikin sambarka, sai kuma iyayen Abdul-Waheed ake jira.
Kusan minti talatin da tafiyar iyayen Muhseen amma shiru babu labarin magabatan Abdul, hakanne yasa Abba kiran Ummukulsoom ta kira Abdul a waya ta bama Abba, itako ta samu gudu daga falon.
Duk zubama Abba dake waya da Abdul-Waheed akayi kowa nasonjin mike faruwa…………✍????
No editing????⛹????♀️
_ZAFAFA BIYAR MASU ZUWA A HALIN YANZU????._
*ƊAURIN ƁOYE!* (Safiyya Huguma
*SAUYIN ƘADDARA!* (Hafsat rano)
*KAI MIN HALACCI!* (miss xoxo)
*BURI ƊAYA!* (Mamu gee)
*WUTSIYAR RAƘUMI..!* (Bilyn Abdull)
????????karku bari ayi babuku
*ga mai buqatar littafan zafafa biyar dukansu ko wasu daga ciki sai ya biya 500 ga dukka litattafan,ko 200 ga littafi daya,ko 300 ga littafi biyu,ko 350 ga liitafi uku,ko 450 ga littafi hudu*
*za’a tura kudin ta wannan accnt number din*
Hafsat kabir umar
0225878823
GT bank
Saika tura shaidar biya ga wannan number
08030811300
Ga masu turo da katin waya kuma zaku tura katin MTN ta wannan number din
07067124863
*_ƴan Niger kuma_*
_ZAKU BIYA NE DA KATIN;_
*_MTN ko MOOV_*
*Novel 1 Naira 200 = 350fc,*
*Novel 2 Naira 300 = 500fc*
*Novel 3 Naira 350 = 550fc*
*Novel 4 Naira 450 = 750fc*
*Novel 5 Naira 500 = 850fc*
_TA NUMBER;_
*+22795166177*
Da zarar kin biya kai tsaye zaki tsinci kanki cikin gidan da zaki samu littafin da kika biya.
*Karki bari ayi babu ke, Abari ya huce shike kawo rabon wani*????????????????????????
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*????????????