NOVELSRANA DAYA

RANA DAYA BOOOK 1 COMPLETE

RANA DAYA HAUSA NOVEL COMPLETE [BOOOK 1]

CHAPTER 16 KARSHE BOOK 1

BY HALIMA ABDULLAHI K/MASHI

Wannan littafin na kudi ne akan farashin 300,idan kuna bukata zaku turo kudin ku ta wannan account number????????

ACT<<0700549935
Halima Abdullahi Access bank sai ku turo shidar biya ta wannan number 09028485925“`

Ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427 Ga masu son Audio na littafin RANA DAYA shima muna dashi cmplt ku turo kudin ku ta account number din da muka bada can sama????????????????ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427 idan baki shirya siya ba ki bari sai kin shirya sai kiyi magana

Masu son tallata masu hajar su suyi magana ta wannan number 09068032427 zamuyi maku cikin sauki

Mun tsaya

Wanka ya fada, da ya fito yayi sallah tun daga lokacin ya fara nuna shi ango ne. Gizna ce ya sha fara sol sai aikinta mai ruwan kasa da ratsin gwal.Aka soka hula kube
takalmi. Turare kuwa yanda ka san zai yi
magana. Ya sakko suka hadu a falo.
Hajiya tana aiken Direbansu, ta tsaya tana kallonshi. Yayi mata kyau sosai. Ya ce, “Hajiya sannu da fitowa.” Ta ce, “Kai ne da sannu Ango, wannan irin wanka haka?”
Ya ce, “Ai karamin wanka ne wannan sai ma anjima.” Ta ce, “To zo muyi magana mana.” Dakinta suka shiga ta ce, “Naji Alhaji yana cewa wai za a daura aure da safen nan?”

Shatima yace “Na Kano ne?” Ta ce “A’a Idan da na Kano tunda asubahi fa naji yana ta waya wai saboda abokanka ko mene ne?”
Shatima ya ce, “Ok, na Aliya ne za’a daura yanzun da safe, saboda ‘yan nesa, in mun yi walima za su tafi.”
Hajiya ta fadada fara’a “Ayya, na gane. To ya za ayi da abincin daurin auran tunda ba mu san za’a zo da zancen ba?” Ya ce, “Ba akwai snacks da nama ba?”
Ta ce, “Eh to, bari sai in sa a zuba a take away.” Ya ce, “Yauwa to sai su Munnir su zo su dauka.”
Gurin abokansa ya nufa inda suka yi masauki,
ya same su kwance wasu kuma suna danne
dannen waya. Ya ce, “Don Allah ku tashi ku

shirya daurin aure karfe takwas.”
Nan suka shiga yabon kýan da yayi. Ya ce
“Ko zama ba zan yi ba kar su yamutse.” Cikin zolaya ya yi maganar. Haka dai ya matsa musu har suka shirya wasu

suka wuce gurin Hajiya don dauko abin da za a
ci a gurin da abin sha. Sun je kofar gidan su Salma Karfe bakwai da
wani abu. Babu kowa, Shatima yaje har kofar
gidan ya yi sallama Auwal ya fito, yaga ko
wanka bai yi ba. Ya ce, “Auwal kun manta ne?” Ya ce, “Muna
sane, yanzun zan yi wanka.” Shatima ya ce, “Ka zo kawai ga abokina kuje da mota ku dauko kanin Baban naku.”
Haka ya matsa musu aka tafi, shi burinshi kawai a daura auren nan, dama motocinshi uku duk suna gurin, da wadda a ka ba shi a gidan su Amna, da wadda ya zabo abokin Babanshi ya bashi.
Da kanshi yaje gidan waliyyin ya fito dashi cikin shiri. Shatima ya dan ji dadi ya ce, “Dama nazo ne in ji ko ba ku manta ba.”
Ya ce, “Ai lokacin bai cika ba ko?” Shatima ya kalli agogon hannunshi, “Eh saura minti talatin.” Ya ce, “Ba komai, shi Auwal ko ya tafi ya zo da dan uwan Baban nasu?”
Shatima ya ce, “Na hada shi da abokina su
tafi.” Ya ce, “Nan ma na sa an sanar a Masallaci,
kuma da safen nan nasa an fadawa makota.”
Shatima yayi godiya ya koma gurin abokansa, sannan ya ce “Munnir don Allah ka je ka taho da su Alhajin ku.”Munnir ya ce “Shatima wai me yasa ka kasa nutsuwa ne? kar ka manta ba wannan ne kadai auran da za a daura maka ba ko?”
Shatima ya ce, “Ni dai burina a daura
wannan, don shi kadai ne me matsala.” Munnir
yayi tsaki, sannan ya wuce.

Salma bata san ma wai an dawo da daurin auranta na safe ba, don ita ko kunshi bata yi ba, ta bari sai da rana tukunna.
Umar ne ya shigo yana cewa “Mutane sun taru a waje.” Yaya Hadiza da wata kawarta itama lokacin sun zo za su amshi kudin cefane gurin Inna suje kasuwa, suka ga guri tam! Da ta shiga take tambayar Inna.
Ta ce, “Ummi ni dai wannan lamari ina nan
ina ta addu’a, jiya fa har mun kwanta ya buga
gida, wai a maida daurin aure na safe.”
Hadiza ta ce, “Insha Allahu alkairi ne.” Itama Salman sai lokacin taji. Hadiza ta dube ta, “Wai Salma kin tsefe kanki kuwa?”
Ta ce, “Na tsefe da dare.” Ta ce, “To in an watse ki dauki wannan man da na ciro miki a akwati na shampoo din ki je shagon wankin kan.Ta ce, “To, kuma wadda zata min kunshin ta ce karfe goma zata zo.” Kawar Hadiza ta ce, “A fara yi mata kunshin mana shi ne mai wahalar.” Salma ta ce, “Nima haka naga zai fi.”
Iyayen Shatima sun iso cikin zauran gidan aka sa tabarma suka zauna, sauran mutane suna waje. Guri fa ya cika tankam. Nan aka daura auren Salma da Muhammad Ja’afar Shatima.
Ana gamawa abokan suka shiga raba-abin da

suka zo da shi. ‘Yan unguwa kam sun shaida
lallai Salma ta tako.
Daga nan kai tsaye suka soma daukar hanyar Kano don karfe tara ta gota. Shatima ya ce, sai ya je gida ya canza kaya, Munnir ya jira shi. Bayan an ragu ya kira Auwal ya ce ya kira
mishi Salma. Dogon hijabi tasa ta same shi a
zaure. Ya kalleta cikin mamaki, ya ce “Salma ya
ban ga kina kyalli kamar sauran Amaran ba?” Gabanta ya fadi, “Wai da gaske ka ke yi mu hudu ne?” Bata san lokacin da tambayar ta zo mata ba. Ya ce, “Wannan ce amsata.” Ta dan yi shiru, sannan ta ce, “Nima ban sani ba, kila don ban wanke kai ba ne sai anjima zan yi.”
Ya ce “A’a su fa naga fuskarsu duk tana ta kyalli, ga kunshi, ke in ga hannunki.” Ta nuna mishi. Ya ce”Haba Salma! Me yasa za ki yi haka?”
Ta ce, “Zan yi ai.” Ya ce, “Je ki shirya ki zo in kai ki gurin da za’a wanke miki kai.” Ta ce, “Yaya zan je Allah.” Ya ce, “Ai daga yanzun na koma miji ba Yaya ba, kuma ba a musu da miji.”
Ta ce, “To.” Ta juya ta koma ciki ya fito, Munnir ya ce, “Ka zo muje don Allah kada lokaci ya kure.”
Shatima ya ce, “Ai yanzun ma gurin gyaran gashi zan kaita.” Munnir ya ce, “Don iskanci ka bar ni in tafi tare da mutane ka tare ni.” Ya jeho masa makullin sabuwar motarsa, “Ga makullinka, bari in bi su Bello don a karshe ba zuwa zaka yi ba.”

Shatima ya ce, “Ka bari mu bi jirgin karfe יי goma.” Munnir ya ce, “Goman dare ko? Duba agogonka kafin muje filin jirgin ma ai ‘yan daurin auran sun juyo, kaga ni bari in bi su sai mun dawo, don nasan kai ba zuwa zaka yi ba kana gurin wannan yar mitsitsiyar yarinyar.”
Shatima yayi murmushi. Ya ce, “To Allah Ya tsare, amma ina mai tabbatar maka ina gabanka can zaka same ni.” Munnir bai sake magana ba ya shiga motar abokansu wadda da suka tsaya za su jera tare, ya ce, “Ku mu je wannan angon ba zuwa zai ba.”
Salma ta sanar da Yaya Hadiza yanda suka yi da Shatima, Hadiza ta ce “Muje muji ta bakin Inna.” Inna ta ce, “Anya kuwa sa fita?”
Wata kawarta ta ce, “Ai yanzu matarsa ce.” Hadiza ta ce, “Shi ne nima na gani.” Inna dai tayi shiru.
Hadiza ta ciro mata jallabiya baka da mayafinta, sai takalmi mara tudu duk na cikin lefan, ta ce “Gashi ke ko wanka ba ki yi ba.”
Salma ta ce, “Bari in dauraye jiki.” Suka bata turaruka ta fesa ta dauki saitin man da zata yi amfani da shi.
Yana jingine a jikin mota, ta fito ta nufo shi.
Ya bude mata gaba ta shiga ya zagaya ya shige.
Ya dan dube ta bayan sun hau titi.
“Bana son kazanta fa, amarya har yanzun bata gyara kai ba.” Ta ce, “Zan gyara dama, ni ban san da safe za’a daura auran ba.” Ya ce, “Amma ya ki ka ji da aka ce ya dawo na safe?”
Tayi dan murmushi, “Ban ji komai ba.” Ya ce, “Har yanzun ba ki fara sona ba ko?” Ta dan ja mayafinta ta rufe fuska. Ya ce, “Ina jin ki.” Ta ce, “Ai ban san so ba ni. Ta yiwu ina yi maka.” Ya ce “To na baki lokaci ki soma sona kafin mu hadu, ki bincika ki san ya ya ake so? Ya ya so yake? Kuma mene ne so?” Ta kalle shi tayi
murmushi ta ce, “To.”Katon shagon da ya kaita lokacin ma suke budewa. Ya ce suyi mata gyara me kyau amarya ce. Ya ji mamakin ganin gashin kanta mai cika da tsawo. Ya ce, “Dama kina da gashi haka?”
Tayi ‘yar dariya. Duk da kiran da ake ta yi ma

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button