FITAR RANANOVELS

RANA DAYA BOOOK 2 CHAPTER 17

RANA DAYA BOOOK 2 COMPLETE HAUSA NOVEL | BY HALIMA ABDALLAHI K/ MASHIBY HALIMA ABDALLAHI K/ MASHI

Tamkar Shatima ya sani Amna shawarma kadai ta ci sai madara. Nafisa ma kadan ta ci da alamu ita ba mai cin abinci ba ce. Duk da har da kishi da suka gama, ya ce su koma kan kujeru yana da magana da su.
Ya ce, “wa zai bude musu da addu’a.” Salma ta cafke, don sun saba yin addu’a in anje gidan gaisuwa ko taya mura daga Islamiyarsu. Sai dai shi ne ya karasa addu’ar da fatan Allah Ya basu zama lafiya, ya hada kansu.
Ya ce, To yana son sanar da su kamar yanda suka sani Aliya ce uwargida don ta dan girme su. Yana son su bata girmanta. Ita kuma yaja hankalinta da cewa tayi musu adalci, sannan ya ce dukkansu ga amanar Salma, yarinya ce kankanuwa yana son in tayi ba daidai ba su sa ta a hanya.
Ita kuma ya ce ta bi kowa sau-da-kafa. Ya bukaci jin ta bakinsu. Aliya.ta ce, “Insha Allahu zata yi fiye da yanda yake so.” Amna ta lumshe ido cikin isa ta ce, “Zan kula.” Nafisa ta ce, “Naji, amma da ka ce ga amantar,wannam yarinyar shi ne ban dauka ba, don ba a rainon kishiya ko jaririya ce.

Salma dai burinta a gama maganar ta kalli cikin dakunan gidannan, don haka da ya ce Salma ba ki ce komai ba? Ta ce, “Ni Yaya duk yanda ku ke so wallahi haka zan yi.” Kafin yayi magana ta ce, “An gama mu kalli dakunan?”
Tausayin Salma ya tsirga mishi, yarinyar babu komai a cikin zuciyarta. Daga shi har matan ba su gabanta. Ya ce “Za ku gani ki bari a gama magana.” Ta ce, “To.”
Ya ce, “Sai batun kwana, ni dai in sona ne in yi kwana daya a dakin kowaccen ku, amma ku ya ku ka gani?” Aliya ta ce, “Yayi.” Amna ma ta ce “Yayi.” Nafisa ta ce, “Ai dama sai hakan, don in ya wuce haka sai bayan wane lokaci za ka ga mijinka?”
Ya ce, “Ke wai fadin to ne matsala?” Ya dubi Aliya, “Yau nan ni ke kenan?” Ta ce, “Haka ne. Suna tashi Salma ta ce “Zaku tafi ba mu gani ba.` Nafisa ta ce, “Ke bakauyiya sai kiyi ta kallo.”
Aliya dai yi tayi kamar an kira wayarta, tasa a kunne ta fita tana fadin “Hello! Hello!! Salma kuwa sai da ta leka ko’ina, Shatima yayi mata jagora. Sai fadi take “Aljannar duniya!”
Suka dawo falo inda Amna ta harde a kan kujera ta ce, “Anty guri ya yi kyau Allah ya kara

arziki.” Amna tayi dan murmushi, sannan ta ce “Amin.” Suna fitowa Salma ta ce “Tsorona daya fa Yaya zan kwana ni daya yau, in aka dauke wuta zan firgita.” Ya ce, “Ba za a dauke ba in Allah Ya yarda, to a haske ki ke kwanciya?” Ta ce, “Sosai ma. Jiya sun dauke wuta Allah yasa Anty Badi’atu tana nan, na kankameta.”
Ya ce, “Dama ke sarkin tsoro ce?” Ta ce, “Kai, Allah ko da ranar nan tsoro nayi ta ji.” Ya ce, “Muje in raka ki, kiyi addu’ar bacci babu abin da zai same ki.”
Bayan ya sa ta ta rufe kofa, ya nufi dakin Aliya yayi wanka yasha sabbin kaya, ya dauki makullin mota ya fita.
Kajin Amarci ya siyo da madara mai sanyi, da
sauran kayan zaki, don ya lura Amna tana son
shan zaki ko ya ce an saba musu da shan zaki.
Kai tsaye gurin da motocin ta suke ya wuce, ya saka tashi. Sannan ya fito da ledojin ya nufi falon Amna. Yana shiga ya kulle kofar, don yasan ba zai fito ba sai gobe.
Dakin da ta sanar da shi cewa nan ne nashi, nan ya nufa. Karan ruwan da ya ji daga cikin bandakin shi ne yasa shi tunanin tana ciki. Sai ma ya ga kayanta da ta cire a kan gado.
[8/16, 21:53] Ummi Tandama????: _
????️RANA DAYA BOOK 2????️

        CHAPTER 5 

BY HALIMA ABDULLAHI K/MASHI

Wannan littafin na kudi ne akan farashin 300,idan kuna bukata zaku turo kudin ku ta wannan account number????????

 Halima Abdullahi Access bank       sai ku turo shidar biya ta wannan number 09028485925```

*Ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427 Ga masu son Audio na littafin RANA DAYA shima muna dashi cmplt ku turo kudin ku ta account number din da muka bada can sama????????????????ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427  idan baki shirya siya ba ki bari sai kin shirya sai kiyi magana*

*Masu son  tallata masu hajar su suyi magana ta wannan number 09068032427  zamuyi maku cikin sauki*

Mun tsaya 

kunnansa daidai bakinta “Me ki ka ce?”
Ta ce, “Tsawona ba zai kai ba.” Ya ce, “Zan taimaka miki.” Ta matso ta dan yanki kasan, ta kalle shi a zatonta zai durkuso ne tasa mishi, sai kurum taji caf! Yayi sama da ita, ya rike kugunta.
Ta kalmashe kafafunta tamkar masu rawar
turanci, sannan ta saka mishi a baki. Gurin ya dauki
sowa. Maimakon ya dire ta sai kurum ya shiga juyi
da ita. Guri kuwa ya dauki ihu da sowa.
Sannan ya sauke ta, kowa ya koma mazauninshi, aka shiga ci da sha. Ba a tashi ba sai sha biyu da mintuna.
Tun da aka dawo daga Dinner Salma ke zaune a barandarta, ga makulli a hannunta amma bata iya bude kofar ba, don tun kafin su Yaya Hadiza su tafi suka kulle suka bata makullin tasa a jaka.

Domin babu wanda yaje a cikinsu. Ranar dama yinin yunwa suka yi tunda ba a kawo musu abincin. ‘yan jere ba, wa ma yasan sun zo wani jere? Shi yasa suka ce ba za su je wata Dinner ba.
Tana shawarar yanda zata yi, taga mota ta shigo. Taga abokan Ango ne suka rako shi, taje kusa da Munnir ta ce, “Yaya.” Ya waiwayo.
“Lafiya ba tun dazu aka maido ku ba?” Ta ce, “Ban iya bude kofar ba ne.” Shatima ya fito a motarsu da ta shigo daga baya.
Munnir ya ce, “Ango kazo ga Amarya ta kasa bude kofa.” Ya iso “A’a, Salma dama tuni kina nan? Ina su Hadiza?” Ta ce, “Sun tafi tunda muka zo wai suna jin yunwa ba za suje ba gurin Dinner.”
Ya ce, “Subhanallah! Da yunwa suka tafi?”. Salma ta ce, “Eh.” Yaje ya bude mata sannan ya ce “Za ki iya kwana ke kadai?” Ta ce, “A’a, ina jin tsoro. Ya daga wayarshi ya kira Badi’atu, ta daga cikin
yanayin bacci ta ce, “Yaya” Ya ce, “Dan fito gani a
nan cikin harabar gida, za ki taya Salma kwana?” Ta ce, “To.” Da ta fito ya ce, “Yanzun daga dawowa har kin soma bacci?” Ta ce, “Na gaji Yaya.” Ya ce, “To ku shiga.” Badi’atu ta ce suje su kwanta don bacci take
ji.
Tare da Alkalamin
Sai taga Salma ta kwanta da kayan jikinta. Ta ce, “Yaya zaki yi bacci da kaya masu kyau? Zama ki iya bacci da wannan kayan?”
Ta tashi zaune a kan Gadon tare da fadin “Nima duk na gaji ne.” suka bude akwatin kayan ciki hade da na bacci. Ta ciro mata wasu kayan baccin ta ce tasa.
Salma ta dago wasu irin masu shara-shara din nan. Dan wando ne da ‘yar riga. Ta ce, “Yanzun wannan ma sai a sa?” Badi’atu ta ce, “Me zai hana, ran da mijinki ke dakin ki za ki sa.”
Salma ta ce, “Tabdijam! Wallahi ba zan iya ba.” Badi’atu ta ce, “Ke da za ku yi gasa!” Salma ta ce, “Ni ba ruwana.” Ta dago wata bireziya ta ce, “Dubi fa wannan ina zan kaita, duk kayan ciki sun yi min yawa.’
Badi’atu ta ce, “Ai ba a zata Karama ba ce shi
yasa, kuma Yaya bai tambayo size din ki ba ne ko?”
Salma tana dariya ta kalli kirjinta.
“To ni me zan sa ma bireziya a nan, ban fa dade da farawa ba, da kirjina shafe yake. Kawai Anty Badi’atu ki kwasa.”
Badi’atu ta ce, “Wai! Kar Yaya ya ji kina ce min Anty ba zan dauka ba, ki bár su nan gaba sai ki saka, masu tsada ne fa.” Salma dai ta dage sai da Badi’atu
ta diba guda biyu pant biyu, don suma din sun yi
mata yawa. Ta ce, “Amma ki fada ma Yaya sai ya sai miki daidai ke.” Salma ta zaro ido “Sai kuma in ce ya sai
min pant!” Badi’atu ta ce, “To ba mijinki ba ne?”
Salma ta ce, “Ni ba zan iya ba.” Haka kayan shafa Salma ta ba Badi’atu damar ta zaba, Sun jima kafin suka hau gado suka yi bacci.
Nafisa tana ta juyi a kan gado, kadan-kadan tana jan tsaki, ranta kuwa wani kunci ne ke damunta. Ta tashi ta sauka a kan gadon tana kallon su Shahida, da sauran su suna bacci.
Ta kalli gurin da Badi’atu take kwance. Yayanta ya kirata. Ina ya tura ta oho. Ta kalli madubi, taga yanda tayi kyau, ga lalle tasha, ban da gyara da aka yi mata irin na Amare, amma yau duk sun tashi a banza.
Darenta na farko, daren da kowace ‘ya mace ke burin gani. Amma Angon yana can gurin wata. Hawaye suka zubo mata. Ranar dai bata runtsa ba sai da sanyin dare ya ratso, sannan ta kwanta bacci yayi gaba da ita.
Ba za ka gane yanayin da Amna take ciki ba. amma dai da ka kalle ta za ka fahimci tana yin
nazarin wani abu. Har yanzu bata samu amsar da zata ba ‘yan’uwanta ba a kan Salma.
Domin ita kanta tana bukatar sanin wacece Salma. Kenan ita ma matarshi ce? Ta sani mata biyu suka yi magana duk da ita ne ta uku, kuma tayi iyakacin tunaninta don ta tuno ko ukun suka yi lissafi, amma bata tuna ba. In ko haka ne ya fara karya kenan?
Lokacin da abokan Angon suka shiga dakin Aliya, ita daya ce zaune a falon ta rufe fuskartą. Sun dan yi wasa irin nasu na abokai, sannan suka yi addu’o’i da kuma shawarwari, suka yi bankwana suka tafi.
Bayan sun ajiye mata abubuwa na al’ada. Ya ce, “Gobe fa za ku zo ku sake raka ni wani dakin.” Suka ce “Kayi kadan, mun yi maka wajibin sauran ya rage naka.
Bayan tafiyar su ne yazo ya samu Aliya, “Tashi muje ciki.” Ya kalli kajin da abokanshi suka kawo ya ce, “Wannan kuma ya zan yi da su?”
Ta ce, “Guda nawa ne?” Ya ce, “A’a ka bari kowacce randa zaka shiga gunta kaje a matsayin Ango da kajin ka da abubuwan da ake zuwa da shi na al’ada.
Amma duk wadda ka ba yanzun ka fita daga dakinta zata ji babu dadi.” Ya ce, “Haka ne, amma kwana nawa ya kamata in ke yi a tsakaninku?” tayi dan murmushi, “Wannan ka bari sai da safe in ka tara mu, ko ba za ka yi mana nasiha ba?”
Ya ce, “Zan muku mana, kin san fa har yanzun ban yi ma Amna zancen Salma ba, na rasa yanda zan yi.” Ta ce, “Kada ka damu, insha Allahu za ta fahimce ka.” Suka ci naman kazar sama-sama, sannan ya ce “Muje muyi sallah don godiya ga Allah tare da addu’ar neman albarkar da ke cikin aurenmu.”
Aliya ta ce, “Kash! Ina fashin sallah.” Ta fadi tare da kallon fuskarsa. Ya kuwa canza fuska, sai taji hakan bai mata dadi ba, domin itama a burinta ta zama ita ce ta farko da zai kusanta a cikinsu. Ta sake kallon shi. “Don haka kayi hakuri.” Ya
dan yi murmushin yake, “Haba ba komai, ai ba
laifin ki ba ne.” Ta ce, “Ko za ka je gurin wata daga ciki?”
Ya taso yazo ya rungume ta. “A’a ba gurin wadda zan je, na sani ko dukkanku ma kuna da larurar a yau.” Ta ce, “Ba zai zama haka ba insha Allah. Ya ce, “Na hakura zuwa gobe.”

Haka suka rungume juna suka kwanta. Saboda gajiya, har makara ya yi. Shida ya farka, yayi sallah sannan yayi wanka ya maida kayanshi don bai zo da kaya ba.
Yaga har Aliya ta hada ruwan zafi ta jera kayan karin kumallo, dama har da kayan tea suka shigo mai yawa, jiya da za’a rako shi daki. Ya kalla sannan ya ce, “Bari in leka sauran mutanan gidannan, bai kyautu in zauna yin karin kumallo ba tare da nasan halin da suke ciki ba. Ta ce, “Haka ne.”
Har ya nufi gefen Salma, sai yayi tunanin zata ci masa lokaci da shirmanta, don haka sai ya juya zuwa sashin Amna. Sai da ya kwankwasa sannan wata tazo ta bude.
Ya ce, “Ba ku tashi ba ne ni na tashe ku?” Ta ce, “Mun yi sallah, mun koma ne.” Ta juya zuwa dakin da ta fito. Ya leka dakin da ya ke zaton Amna tana ciki.
Sumayya ya gani tana danna waya. Ya ce, “Har kin tashi sarkin chart?” Tayi murmushi, sannan ta gaida shi. Ya ce, “Ina honey take?” Ta kalli kan gadon “Gata can.” Sannan ta tashi ta fita.
Yabi dakin da kallo, an zuba dukiya mai yawa. Ya kalli kan gadon tana kwance a tsakiyar gadon
ta rufe jikinta da bargo, gashin kanta ya sauka a dokin wuyanta, tayi kyau da baccin.
Ya matsa kusa da ita, ya saka yatsun shi na tsakiya, ya kwashe gashin ya maida kan filo. Sannan ya sunkuya ya sumbaci kumatunta. Tayi mika sannan ta sake gyara kwanciya, bargon ya dawo kan cikinta, sannan ta koma rigingine.
Rigar baccinta bata da nauyi, don haka yana kallon kirjinta ta leshin da aka yi kwalliya da shi a kirjin. Tsigar jikinsa ta tashi.
Ya juyo ya fita falo. Sumayya tana kan kujera ya ce, “Ashe tana bacci.” Ta ce, “Eh da ka tashe ta ai.” Ya ce, “A’a bar ta ta huta. Me ku ke bukata saboda karin kumallo?”
Ta ce, “Bari in kira Antynmu.” Ta shiga wani daki ta kira kanwar Mamansu. Ya gaida ta cikin girmamawa, sannan ya ce “Anty dama ina son in ji me ku ke bukata?” ta ce tana zuwa.
Suna da kayan tea da komai, biredi ne kawai. Sai gas da babu bare su soya wani abu. Ya ce, “Gas dole sai rana tayi, amma bari yaje ya kawo musu biredi.” Sumayya ta ce “Anty akwai abubuwa masu amfani da wutar lantarki a kicin din Yaya Amna.

Ni dai zan gasa biredi kuma zan soya kwai.” Ta kalli Shatima. “Yaya ka siyo mana me yanka yanka.” Ya ce, “To Sumayya.”
Daga nan dakin Nafisa ya shiga. Kaf! Din su suna dakin da Nafisar take, ya shiga suka yi ta gaishe shi. Ya duba bai ga Nafisar a cikinsu ba. ya ce, “Ina Amaryata?” Suka ce, “Tana wanka.” Ya ce, “Me ku ke bukata?”.
Shahida ta ce, “Dama yunwa muke ji.” Ya ce,
“Akwai kayan tea ne nan?” Momi kanwar Nafisa
ta ce, “Sosai ma, gasu can a store.” Ya ce, “Bari in
kawo muku biredi.” Hamida ta ce, “Yaya Nafisa
kuwa bata cin biredi.” Ya ce, “To fa! Yanzu me zan kawo mata, me take ci?” Momi ta ce, “Ai naga akwai Indomie sai ayi mata.” Ya ce, “To bari yaje ya kawo musu biredi.
In ta fito a ce, yana gaida ta kafin ya dawo. Ya shiga gurin Salma itama sai da ya Kwankwasa kofa. Tazo ta bude, ya kalle ta. Sanye take da kayan bacci, sun yi mata yawa. Sai gashinta da ya sauka a bayanta. Sannan ga abin risho a hannunta tana ta kici-kicin sawa da zabori, tasa daya tana fama da na biyu.
Ya ce, “Mene ne wannan? Ta ce, “Abin risho ta durkusa “Ina kwana Yaya?” Ya ce. ne.

“Lafiya. Na ce miki ni ba Yayanki ba ne ko? Yanzun me za ki yi da wannan?”
Ta ce, “Zamu sa ruwan wanka ne, kuma zamu karya.” Ya ce, “Tashi daga tsugunno mana, ba ki da butar jona ruwa ne?”
Ta girgiza kai, “Bani da shi.” Ya ce, “To ai babu kalanzir din da za ki kunna rishon ko?” Ta ce, “Babu.” Ya ce, “Kina da flask din ruwan zafi?” Ta ce, “Bari in duba.” Ta fito dashi a cikin kwalinsa ya ce “Ciro.” Ta ciro, ya amsa ya ce, “Bari in je sai Aliya ta dafa miki. Ina Badi’atu?”
Ta ce, “Tana bacci.” Ya ce, “To ina zuwa.” Yaje gurin Aliya ya bata filas din ya ce, a sa ma Salma ruwan zafi a nan.”
Ta ce, “To.” Ya ce, “Bari in je in siyo musu biredi.” Ya dauki makullin mota. Ta ce, “To amma wanda ba shi da kayan tea ga wannan da su Munnir suka shigo da shi.” Ya ce, “Su duk suna da kayan tea Salma ce kawai.” Ta ce, “To in ka zo sai ka kai mata.
Da yawa ya siyo, kofar Amna ya tsaya ya ba Sumayya ta dibi wanda zai ishe su, itama Shahida ta dibar musu. Sannan ya koma gurin Aliya.
Ya ce, “Gashi in za ta kara.” Ta ce, “Nasun nan ma ya yi yawa.” Ta bashi kayan tea har da ragowar kazar da suka ci jiya, ta ce ya ba Salma.
Ya dubeta cikin jin dadi ya ce, “Allah Yasa yanda ki ke bani hadin kai da na zauna lafiya, sauran ma su bani.” Ta ce, “Za su ba ka insha Allah.”
Ya kai ma Salma, sannan ya dawo suka karya suna ‘yar hirarsu irin ta masoya. Da suka gama ya ce bari yaje inda su Munnir suka kwana. Ta ce, “Har da Munnir aka kwana a nan?”
Ya ce, “A wannan dare ina zai koma Zariya?” Ta ce, “To kaje musu da abin kari.” Ya ce, “A’a masaukin da suka sauka akwai gurin cin abinci, nasan yanzun sun ma karya. Kila tare za mu wuce Zariya da su in kwaso kayana.”
Yana gaida Hajiya, Mustapha ya shigo. Ya gaishe shi, Shatima ya ce “Don Allah Mustapha ka hada min duk kayana. Sannan kuma in an gama zirga-zirga ka dauki motar nan tawa ta da.”
Dadi ya rufe Mustapha, ya shiga godiya. Hajiya ta ce, “Kafar yawo ta karu, ai dole kayi murna.” Mustapha yace Ai na huta, in na ari motarki, ko ta Alhajinma, sai a kira ni a ce dawo min da motata yanzun nan.”
[8/18, 09:54] Ummi Tandama????: _____
*????️RANA DAYA BOOK 2????️* 


            CHAPTER 7 


*BY HALIMA ABDULLAHI K/MASHI*


*Wannan littafin na kudi ne akan farashin 300,idan kuna bukata zaku turo kudin ku ta wannan account number????????*

ACT<<0700549935
Halima Abdullahi Access bank sai ku turo shidar biya ta wannan number 09028485925“`

Ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427 Ga masu son Audio na littafin RANA DAYA shima muna dashi cmplt ku turo kudin ku ta account number din da muka bada can sama????????????????ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427 idan baki shirya siya ba ki bari sai kin shirya sai kiyi magana

Masu son tallata masu hajar su suyi magana ta wannan number 09068032427 zamuyi maku cikin sauki

Mun tsaya

Bayan ya sa ta ta rufe kofa, ya nufi dakin Aliya yayi wanka yasha sabbin kaya, ya dauki makullin mota ya fita.
Kajin Amarci ya siyo da madara mai sanyi, da
sauran kayan zaki, don ya lura Amna tana son
shan zaki ko ya ce an saba musu da shan zaki.
Kai tsaye gurin da motocin ta suke ya wuce, ya saka tashi. Sannan ya fito da ledojin ya nufi falon Amna. Yana shiga ya kulle kofar, don yasan ba zai fito ba sai gobe.
Dakin da ta sanar da shi cewa nan ne nashi, nan ya nufa. Karan ruwan da ya ji daga cikin bandakin shi ne yasa shi tunanin tana ciki. Sai ma ya ga kayanta da ta cire a kan gado.

A ranshi ya ce, “Wannan yarinyar wanka a gurinta ko kifi sai haka.”
Ya cire hularsa ya ajiye a kan durowar da ke gefen gado. Tana fitowa daure da babban Tawul, ta rufa da karami tana goge jiki. Ya sakar mata murmushi, tare da cewa, “Koma kiyi alwala muyi
wa Allah godiya.” Dan jim din da tayi sai ya ji tsoron kar dai itama bata sallah! Ya ce, “Kin ji ni kuwa?” Ta ce, “Ina tunanin kamar nayia alwala, amma bari in
sake.” Shi ne yaja musu sallah suka yi raka’a biyu, ya dafa kanta yayi addu’o’i kamar yanda ya zo a sunna. Taje gaban madubi zata shafa manta wanda take shafawa in zata kwanta, ya zo bayanta, “Kawo in shafa miki.”
Ta kalle shi ta cikin madubin, ya kashe mata ido daya. Tayi murmushi, “A fuska kadai zan shafa.” Ya ce, “Eh kawo.” Tamkar yana shafa kwai a kan kanta haka ya yi wa fuskar. Ya kalli ledar da ya shigo da ita ya ce, “Ina zuwa.”
Yaje ya dauko plate da wuka da cokali mai yatsu. Ya samu tana saka rigar bacci. Ya ciro kajin da sauran abubuwan ciye-ciye. Ta kalle shi, “Me za ayi kuma? Ba dai cin abinci ba?” Ya ce, “A’a
cin kazar amarci zamu yi.” Ta waro ido, dole ne cin kazar?” ya daga mata gira.

Ta shafa ciki, “Gashi na koshi ne da yawa honey.” Ya cire rigarsa farar singileti kar ce a jikinsa, ya ce “Bari in ba ki kadan.” Ta hau tsakiyar gado ta zauna. Ya dauki tiren ya hau shima, yasa wuka ya yanko naman ya tsira da cokali ya ce, “Bude baki.”
Sau hudu ta karba ta ce ta koshi. Ya bata madara, shima kurɓarta daya. Ya sauka yayi shirin bacci. Yana hawa gadon ya ce “To tashi in fada miki abinda zai biyo bayan kazar nan da ki ka ci.”
Ta ce, “Ka kwanta ka fada min.” Ya kwanta, sannan ya dagota zuwa saman cikinshi. Ya kai hannu ya latse fitilar dakin.
Ya fito daga bandaki, ya zo ya sake jan yatsunta. Tashi mana honey kiyi wanka muyi sallah. Da kyar ta sauko ya jirata tayi wanka da alwala.
Shi ne ya ja su sallah, sannan suka koma kwanciya, ya janyota jikinshi. “Jiya kin hana ni bacci.” Ta ce, “Ka hana mu dai Honey.” Cikin shagwaba tayi maganar, suka rufa sai bacci.
Kamar jiya ya shiga dakin kowacce ya duba lafiyarta tare da tambayar bukatarta. Su ukun
kowacce tana bukatar Gas don dafa abinci. Salma kuma tana bukatar kalanzir tun da wuri ya ba kowaccen su abin da take bukata.
Salma da Aliya ya siyo musu kayan abinci, kayan miya ne ya ce bai san ina zai samo ba. Ya tambayi Maigadi, ya ce a ba shi ya siyo. Aliya ce ta rubuta mishi kuma ya ba shi kudin mota zuwa kasuwar Kawo.
Da aka kawo ta raba hudu, ta ba da na kowa. Kafın yamma duk ya sallame su. Ranar dakin Nafisa zai kwana, kuma washegari zai koma aiki.
Itama dai yasai Kaji da sauransu kamar dai na Amna. Ya ji dadin darenshi da Nafisa, domin ta kasance mai shagwaba tare da kokarin faranta mishi, kuma da sassafe ta hada mishi abin kari. domin ya fada mata dan hutun da aka ba shi ya kare office zai koma.
Tana rataye da jakar a kafada ta rike wayoyinsa, ta ce “Sweety muje in raka ka mota.” Ya ce, “To.” Suna fitowa barandarta ya ce, “Bari in duba yanda sauran ‘yan uwanki suka kwana.”
Ta dan taba baki, tare da fadin “To.” Dakin Aliya ya nufa, wadda dama tana tsaye a windownta na falo tana hango lokacin da suka fito, kan ya Karaso ta koma cikin uwardaki da sauri.
Taki amsa sallamar har sai da ya nufo dakin da ya san zai same ta a ciki yana kiran “My love!” Ta amsa daga ciki. Ya shiga, ta gaida shi tare da dan yatsina fuska. Ya ce, ” ba dai ba ki jin dadi
Ba
Ta ce, “Na kwana da ciwon ciki ne.” Ya ce, “Shi ne ba ki kira ni ba?” Ta zo ta dafa kafadarsa. “In na taso ka da wannan daren ina za ka neman magani, gashi mu baki ne a unguwar, sannan kuma na tuna kai da Amarya ne zan katse muku
soyayya.” Yayi murmushi, “Komai soyayya ai ciwo ya fi komai.” Ta ce, “Na samu sauki har za ka fita office!” Ya ce, “Eh.” Ta ce, “Allah Ya ba da sa’a, Ya tsare mana kai, Ya saka samo mana halak.” Ya ce, “Ameen.” Ta rako shi har zuwa Barandarta.
Nafisa ta kalli lokaci a wayar hannunta ya dauki tsawon minti tara a dakin Aliya. Ya nufi gurin Salma ya kwankwasa kofar don ya murda ba a bude take ba.
Ya buga sosai sannan ta bude, daga gani bacci ta tashi. Ya shiga ta durkusa ta gaida shi. Ya amsa tare da tambayar kafiyar ta. Ta ce, tana lafiya. Ya mike yana tambayar ta karya kuwa? Ta ce, tun da tayi sallah bacci ya dauketa.
Ya ce, “To akwai abinda take bukata?” Ta ce, “A’a.” Ya ce, “To zai tafi office. Ya koma yau. Ta ce, “To Allah dawo.dakai lfy ya bada sa’a.” Har ya fita ya tuna ya
“Yau a nan zan kwana fa!” Shiru yayi yana kallonta yanda tayi tambayar cikin tsoro. Ya ce, “Naga kin tsorata ne.” Ta kirkiro yake, “A’a ban ji tsoro ba, sai ka dawo to.”
Yayi ‘yar dariya,sannan ya fita. Nafisa ta kalli wayar, ya ci minti shidda ya zo zai je dakin Amna. Ya ce, muje tare da na fito zan shiga mota, tunda kin ga motar tana kusa da dakinta. Nafisa ta ce, je ka fito.
Amna ma bata tashi ba, yana tsaye ta bude bayan yayi ta bugu. Kayan bacci ne a jikinta, zai shiga ta rungume shi, suna rungume da juna ya ce, “Zan tafi office.” Ta ce, “To sai ka dawo.” Ya sumbaci kumatunta sannan ya ce, “Zamu yi waya ko?” Ta ce, “Eh.” Ya ce, “Kin ci abinci?” Ta ce, “Yanzun na tashi, ban san me zan ci ba, in da ka siyo shawarma din nan da nisa?”
Ya ce, “Sai an fita unguwar nan, can cikin gari ne. Shi za ki ci?” Ta ce, “eh.” Ya ce, “To bari in tafi da Maigadi sai ya kawo miki. Allah Yasa dai suna da shi da safe nan.” Ta ce, “Amin.”
Leda hudu ya bashi, ya ce ya mika kowane daki. Salma ta yini cikin damuwa da tunani tun da Shatima ya sanar da ita. Duk tsoronta tafi son ta kwana ita daya da ta ya zo dakin.
Da rana ta dafa shinkafa dafa-duka, shirman da Salma tayi ta manta bakinta ne ita daya, ta shirga abincin fal tukunya. Yini tayi ci, bayan ta shake masa kula.
Da dare ma shi zata ci. Karfe shida ya shigo, dakin Nafisa yayi wanka, itama sai da yaje siyo kajin amarci. Yana can ne ma ya ga kiran Amna. Cikin sauri ya daga. Ta ce, “Honey.” Ya ce, “Na’am honey ya aka yi?”
Ta ce, “Ina jin yunwa ne, da rana ma banci komai ba.” Ya ce “Ba akwai danye ba kuma nasa muku Gas.” Ta ce, “Honey indomie kawai na iya dafawa, kuma ta gushe ni, kai kuma ba ka kawo min me aiki ba.”
Ya kasa magana, can ya ce “To bari in zo gidan amma yanzun me ki ke son ki ci?” Ta ce, “Chips.” Ya ce, “Shi kenan.” Leda hudu yayo, ya kuma mika kowane daki.
Lokacin da ya shiga gurin Salma tana zaune cikin kujera sanye take da riga doguwa baka da dan kwalinta. Har kafafunta ta zauna a saman
kujera, zuciyarta cike da tsoro, fatanta kada ya ce zai bukace ta, domin duk wautar ta dai tana da labarin abin da ake yi in an yi aure.
Bai lura da ita ba ya ce, “Salma!” Ta amsa, daga in da take ya waiwayo. “Dama kina nan?” Ta sakko tazo ta tsugunna a gabansa. “Gani Yaya.” Ya ce, “Amshi wannan ki kai ciki.” Ta amsa tare da cewa kicin zan kai?”
Ya ce, “Daki dai ki kai tare da plate da cokali da kofuna.” Ta ce, “To.” Da ta aje bata fito ba, sai ta zauna a bakin gado cikin sake-sake. Ya ce, “Salma!” Ta amsa daga ciki. Ya ce, “Zo.” Ta tsugunna a gabanshi. Ya ce, “Kije gurin Nafisa ki ce ta baki jakata ta office.”
Har ta kai bakin kofa sai ta waiwayo, “Yaya dakin da muka ci abi Anty Nafisa din?” Ya ce, “A’a na farkon.” A bakin kofar ta tsaya ta kwankwasa. Nafisa ta fito ta dan bude ta leko.
Ganin Salma sai ta hada rai tayi, mata kallon sama da kasa. Sannan ta ce, “Lafiya?” “Yaya ne ya ce ki ba da jakarshi ta office.”
Ta sake tabe baki, sannan ta juya. Salma da karambani ta shige ciki don kawai tana son ganin dakin. Cikin sha’awa take bin falon da kallo, har ma bata san Nafisa tana miko mata ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button