FITAR RANANOVELS

RANA DAYA BOOOK 2 CHAPTER 17

RANA DAYA BOOOK 2 COMPLETE HAUSA NOVEL | BY HALIMA ABDALLAHI K/ MASHIBY HALIMA ABDALLAHI K/ MASHI

.
[8/18, 17:36] Ummi Tandama????: _
????️RANA DAYA BOOK 2 ????️

      CHAPTER 10 

BY HALIMA ABDULLAHI K/MASHI

Wannan littafin na kudi ne akan farashin 300,idan kuna bukata zaku turo kudin ku ta wannan account number????????

 Halima Abdullahi Access bank       sai ku turo shidar biya ta wannan number 09028485925```

*Ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427 Ga masu son Audio na littafin RANA DAYA shima muna dashi cmplt ku turo kudin ku ta account number din da muka bada can sama????????????????ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427  idan baki shirya siya ba ki bari sai kin shirya sai kiyi magana*

*Masu son  tallata masu hajar su suyi magana ta wannan number 09068032427  zamuyi maku cikin sauki*

Mun tsaya 

Shatima ya kalli agógonshi, sha dayan dare sam bai so ya kai wannan lokacin ba, alhali yana dakin Nafisa, domin shi ya san korafi ta da mita, har bai so ya mata wani kuskure, don baya son tun yanzun ya fara nuna fushinsa.
Kuma fita ce ta kama shi ta dole za su ga Gwamna. Daga can suka wuce bikin wani abokin aikinsu. Shatima ya mike tare da dafa na kusa da shi.
“Abubakar ba zan iya jira a gama wannan Dinner din ba. domin iyalaina suna zuba ido.” Shima ya mike, “To ai dole nima in tashi tun da

kai za ka sauke ni a kawo, ka manta motana tana can gurin aiki?” Shatima yayi fakin ya fito, duk da yayi ma
Nafisa sako ta waya cewa sun fito, amma haryanzun gaban shi yana faduwa.
Ya kwankwasa kofar, kusan sau hudu, sannan ya kira layin ta sau uku, amma bata daga ba, ya saka makullin mota yana kwankwasawa.
Ranshi ya soma ɓaci, domin yasan taji. Har ya fusata zai tafi mota ya shiga ya kwanta, don ba zai je dakin wata ba ya zama sabuwar matsala. Sai ya ji karar bude kofa. Ya waiwayo, ta bude ta leko fuskarta murtuk!
Ya ce, “Saboda wulakanci kina jina ina buga kofa
amma ki ka kasa zuwa ki bude min, na kira ki nanma ba ki daga ba?”
Juyawa tayi, shi kuma ya bi ta ranshi ɓace. Ya shiga dakinshi, ita kuma ta wuce nata. Ya gama al’amuran rayuwarshi da ya saba kafin ya kwanta. Sannan yayi kwanciyarshi.
Nafisa tayi tsammanin ya shigo ya roke ta, ko ya lallasheta. Sannan ya yi alkawarin ba zai sake yi mata irin haka ba, amma sai taji shiru. Ta tashi tayi ta kai-kawo.”


Yayi rigingine idanunshi lumshe, yana nazari a kan halayan matansa din nan guda hudu. Bai ji shigowarta ba sai dai dan kukanta yaji, ranshi ya kara baci. Ya bude ido, sannan ya tashi zaune.
Itama ta zauna. Cikin kuka ta soma korafi, “Ni kullum in dai girkina ne sai ka nuna rashin kulawarka kaina, ni nasan kafi son su a kaina, nasan ni ke sonka amma kai ba ka sona.
Kana nuna min bambanci karara.” Ya daga mata hannu, cikin daga murya ya ce, “Wai ke ba ki da fahimta ne? ke kullum cikin korafi, bana turo miki message ba?
Ke in dai ina dakinki bani da kwanciyar hankali. Ban san me zan yi miki ki yarda ina sonki
ba.” Ta tsugunna ta hau kuka me karfi. Ya tashi ya
koma falo ya kwanta.
Nan ya kwana, da safe ya shiga dakin shi ya samu bata ciki, yayi wanka ya shirya. Bai ji motsinta ba ya leka kicin babu alamun zata hada mishi abin kari, don haka ya sabi jakarsa ya kai mota.
Ya nufi dakunan sauran kamar yanda yayi tsammani. Haka ya samu Amna tana bacci, a cikin kwana ukun da ba a dakinta yake ba, bai taba samun ta ido biyu ba.
Ya shafi kumatunta tare da sumbatar leбunanta. Ta bude ido. Ya ce, “Honey baccinki yayi yawa.” Ta yunkura ta tashi zaune. Nima ban san wane irin bacci nike yi ba honey ya zauna bakin gadon.
Ta ce, “Baccina ya karu, sai in kai karfe daya fa ban ji na gaji ba.” Ya rungumota zuwa jikinshi. “Ko an samo mana baby me hana bacci ne?” Tayi dariya “Haba dai, lokacin al’adana bai kai ba tukunna. Kuma naga Anty Amarya ta gidanmu tana rashin lafiya sosai, tayi ta amai.”
Ya kai hannu ya shafa damammen cikin ta, “Bani da ajiya ke nan?” Ta ce, “Babu, ina jin dai soyayyar da ka ke kashe ni da ita ne in kana gurina, sai in baka nan ta sani kasala.”
Ya mike tare da cire ta daga jikinshi. “Bari in tafi kada nayi latti, ki tashi ki dan karya sai ki koma bacci, abincin safe yana da muhimmanci a gurin dan Adam.” Ta ce, “To.” Suka yi sallama.
Yana shiga gurin Aliya ya same ta, kwance kan kujera tana kallo. Ya ce, “Kin yi abin kari kuwa don nan zan karya?” Ya fada tare da zama kusa da kafarta. Yasa hannunshi ya dafa kwafrinta. Ta kalle shi sannan ta mike zaune ta gaida shi.
Ya amsa tare da nanata zancen abin kari. Ta ce, “Na zaci wasa ne.” Ta mike da sauri ta dauko
flaks na ruwan zafi tare da jera masa kayan tea a gabansa..
Cikin sauri taje kicin ta soyo masa kwai zuciyarta cike da son jin abin da yasa bai karya dakin Nafisa ba, har wani bangare na zuciyarta yana addu’ar Allah Yasa fada suka kwasa, zata dan bigi cikin shi taji.
Yana ci yana sa mata albarka, kuma a ranshi yana fadin Aliy matar rufin asiri ce.’ Ta ce, “Nafisa bata jin dadi ne?” Ya kalle ta, “Eh tun jiya jikinta ba dadi.”
Gabanta ya fadi, a ranta ta ce, “Kar dai ciki ne?” Tayi murmushi “Allah Sarki, zan je in dubata.” Ya ce, “A’a kada kije, kin san ba kowa ke son sannu ba a ciwo.”
Aliya ta ce, “Haka ne.” Nafisa tana daga cikin wadanda ba su son sannu. Ta ce, “Allah dai ya bata lafiya.” Sai da yayi tam! Sannan ya shiga gurin Salma. Tana zaune kan kujera, yau dai da kewar gida
ta tashi, tun da tazo bata kara jin labarin iyayenta ba, kuma babu wanda yazo dubata.
Bai zauna ba yana daga tsaye ta tsugunna ta gaida shi. Ya ce, “Yau kuma ya naga fuska babu
annuri?” Salma ta ce, “Dama ina son kazo in ce maka ni zan je Zariya yau.”
Ya ce, “Me ake yi a can?” Ta ce, “Ni dai ina son in ga su Inna ne gashi har an yi arba’in din Babanmu, kuma ban je ba.” hawayen da suka taru a ramin idonta suka zubo kan kumatunta.
Ya tako zuwa inda take, yasa hankici ya share mata kumatunta ta inda ruwan hawayen ya bata. Ya ce “Kin ga nayi latti.” Ya fada tare da kallon agogon hannunshi.
“Ki kwantar da hankalinki, in na dawo zamu yi maganar. Ni mun yi waya da Auwal jiya, duk suna
lafiya. Me za ki dafa min yau?”
Ta ce, “Duk abin da ka ce, bayan ko na dafa baka ci, sai ka ce ka koshi?” A ranshi ya ce, ashe tana sane. Ya ce, “Yau ba zan ci komai ba, zan ci naki ne amma ki min tuwo me kyau kar fa ya kone, bana son abu me kauri.”
Ta ce, “Miyar me za ayi?” Ya ce, “Kubewa danya.” Yasa hannu a aljihu, ya ciro dubu daya, “Gashi ki sai abin da ba ki da shi. Ke baki da fridge shi yasa ni ke baki kudin nama, su kin ga suna dashi, ki ba Baba Maigadi ya siyo miki.” Ta ce, “To.” Suka yi sallama ya tafi.
Nafisa ta tabbatar ita ce baya, don yana fita ta biyo bayanshi, taga shigarshi dakin Amna. Yau minti sha daya ma ya kwashe dakin ‘yar gwal dinshi kuma har minti sha uku.
Itama Salma yau ta samu minti tara, gashi har latti yayi saboda ya duba lafiyar wadanda yake so a rayuwarsa. Kila ma ya fada musu cewa sun samu matsala ne tunda ko’ina ya kara lokaci fiye da da.
Nan take taji zuciyarta tayi mata amanna da zargin ta. Don haka tasa sabon kuka ta shige uwar-daka.
Aliya ta gama karinta, dama tuni ta kammala gyaran dakinta. Tayi wanka, riga da siket ta saka na atamfa bata daura dankwali ba, ta yafa gyale ta nufi sashen Nafisa, don tana son sanin ciwon da Nafisa din ke yi, fatanta dai ya zama ba ciki ba ne.
Ta murda kofar ta shiga da sallama. Babu kowa a falon, sai da ta kare ma ko’ina kallo, a ranta ta ce, ‘Ashe itama an zuba Naira itama dai kujeru saiti biyu ne, sai dai na Amna sun fi tsada.
Ta kalli gurin Dining, ashe itama dai tana da su, ta taba baki, sannan tayi sallama. Can Kasa Nafisa ta jiyo sallamar, ta tashi ta fito. Ganin Aliya sai ta hade ranta tam!
Aliyar ta ce, “Ina kwana, ya jiki?” Nafisa ta ce, “Wa ya ce bani da lafiya?” Aliya ta ce, “Mijinki da ya zo ya karya a gurina, ya ce baki jin dadi shi ne nazo in ga ko zan iya taimaka miki da taimakon farko.
Ran Nafisa yafi na da baci, ta ce “Fitar min a daki, kun ji dai da gulmarku ke da shi, kya fadi gaskiyar abin da ku ka tattauna, za ki zo kina wani wai kin zo duba ni, ja gulmarki ki fita.”
Aliya ta fito jiki babu kwari, sai dai da taje daki ta nutsu tana nazarin maganganun Nafisar, ana ta tunanin Nafisar tana da cikin tabbas, kila bata son ya fada ne take zargin ko ya fada. Kila shima ta fada masa bata son a ji ne shi
yasa ya ce kar taje ta gaida ta. Ran Aliya yayi
matukar baci, in zarginta ya tabbata lallai shirinta zai rushe.
Ta dauki wayarta ta shiga kiran Aisha. Ta daga tare da fadin, “Uwargidan Shatima, mai mulkin zuciyar Shatima da iyalanshi.” Aliya cikin sanyin jiki ta ce, “Hmm! Kawata ai wannan mukamin yana nema ya kufce min.”
Aisha ta ce, “Da aka yi me?” Ta ce, “Nafisa, wannan ‘yar uwar tashi ciki gare ta. Aisha ta ce, “Ke fa?” Aliya ta ce, “Shiru, kuma duk ranar da
yake dakina sai mun yi mu’amala da shi.” Aisha ta ce, “Abin Allah ke nan, to yanzun ke ya za kiyi?” Ta ce, “Shi ne na kira ki in ji ko da wata shawara.” Ta ce, “Kin sha kwayoyin nan masu
daurayo mahaifa? Suna taimakawa kin sani.” Aliya ta ce, “Duk wata kwaya da na san zata taimaka min na siya nasha. Maigadi na rubuta na ba ya siyo min, don shima da ya gani sai dai na ce masa su ne ni ke sha.in cikina yana ciwo don nayi masa karyar ciwon ciki.”
Aisha ta ce, “To ki jira kila nan gaba kadan ke ma ki samu. Ki dai yi kokari ne ki ga cewa kimarki bata girgiza ba a gurinshi.”
Aliya cikin damuwa ta ce, “Ai na so ‘ya’yana su zama sune manya, dadin rike gida ke nan.” Aisha ta ce “Ba ki san in mace ta koma gurin miji yafi komai dadi ba, ko ‘ya’yanki ne kanana sai ki ga suna juya manyan don kaunarki ce zata shafe
su, kuma dole a zauna haka. Dubi gidan Hajiya Rayya mana Maman kawarmu Sa’ida, ita ce ta biyu, amma dubi yanda
take baza iko, ‘ya’yanta suna wadaka.” Aliya ta saki ranta har tayi ‘yar shewa, “Kuma fa haka ne. Su Sa’ida muna gama Secondary a ka
kai su Umra, amma Tahir babban wansu an kasa biya masa kudin Makaranta.
Aisha ta ce, “To ai yanzun shagon saida waya da gyaran waya ya bude. Su ko su Sa’ida suna Ghana, şun jima suna hira kafin daga baya suka yi sallama da cewa tayi ta addu’a.
Nafisa tana kwance, tana jiyo sallar Azahar ana kira. Har zuwa yanzun bata karya ba, bakin ciki ta rasa inda zata saka kanta ace wai da miji ma ba ka da sirri, komai sai yaje ya fada ma kishiyoyi.
Sallama ta sake ji da bugun kofa, tsaki taja tareda fadin “Wace munafukar ce kuma oho!” Tayi banza da bugun. Sai da ta jiyo an shigo falon ana sallama. Ta dauki muryar Anty Maimuna kanwar Mamansu da ke aure a cikin Jaji (Barikin Sojoji), mijinta soja ne.
Cikin sauri ta fito da murna tana fadin, “Haba! Ni naji kamar muryar Anty, Anty sai yau?” Ta sauke ‘yar da ke hannunta, Nafisa ta dauke ta ta nufi cikin uwar daki tana fadin Anty shigo ciki kawai.
Kan gado ta sauke yarinyar tana kallonta tare da tambayar “Ina su Hisham?” Antyn ta ce, “Yana Makaranta, ko ba Makaranta ba zan zo da ita ba. Nasrin din ma don dai taki zama ne.
Nafisa ta ce “Gara ma da ki ka zo da ita na ganta.” Ta mike ta kawo mata ruwa da lemon roba. Ta ce, “Bari in dora abinci Anty, ina nan kwance ko karyawa ban yi ba.”
Anty Maimuna ta ce, “A kan me za ki zauna da yunwa ga fuskarki ma duk a kumbure sai ka ce kin ci kuka?” Nafisa tayi rau-rau tare da fadin “Hmm! Bari Anty Maimuna, wallahi ina cikin wani hali a gidannan. Sai da nayi ta yiwa Mama mita a kan wannan auren ta ce ba haka ba, gashi yanzun tun ba a je ko’ina ba bakin ciki zai kashe ni.”
Anty Maimuna ta zaro ido, “Fada min abin da ke faruwa don Allah, ke da mijin ko ke da kishiyoyi?” Nafisa ta soma kuka, “In su ne akwai wadda zan daga ma kafa ne? shi ne da kansa. kullum in dai yana dakina to fa sai sanda yaga dama zai dawo, in yi kwalliya in ta jiransa a banza.
Karfe shida fa yake dawowa, amma ni jiya sai sha dayan dare. Nayi magana ya shiga fada min maganganu, har da yin yaji yana kwana a falo.
Kuma gashi babu sirri, da safe yaje ya barbada ma matansa komai.” Ran Anty Maimuna ya baci, ta ce “To mene ne na zuwa ya fada musu don yaja miki raini?”
[8/18, 17:44] Ummi Tandama????: _____
*????️RANA DAYA BOOK 2????️*


           CHAPTER 11 



*BY HALIMA ABDULLAHI K/MASHI*


*Wannan littafin na kudi ne akan farashin 300,idan kuna bukata zaku turo kudin ku ta wannan account number????????*

ACT<<0700549935
Halima Abdullahi Access bank sai ku turo shidar biya ta wannan number 09028485925“`

Ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427 Ga masu son Audio na littafin RANA DAYA shima muna dashi cmplt ku turo kudin ku ta account number din da muka bada can sama????????????????ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427 idan baki shirya siya ba ki bari sai kin shirya sai kiyi magana

Masu son tallata masu hajar su suyi magana ta wannan number 09068032427 zamuyi maku cikin sauki

Mun tsaya

yunwa ga fuskarki ma duk a kumbure sai ka ce kin ci kuka?” Nafisa tayi rau-rau tare da fadin “Hmm! Bari Anty Maimuna, wallahi ina cikin wani hali a gidannan. Sai da nayi ta yiwa Mama mita a kan wannan auren ta ce ba haka ba, gashi yanzun tun ba a je ko’ina ba bakin ciki zai kashe ni.”
Anty Maimuna ta zaro ido, “Fada min abin da ke faruwa don Allah, ke da mijin ko ke da kishiyoyi?” Nafisa ta soma kuka, “In su ne akwai wadda zan daga ma kafa ne? shi ne da kansa. kullum in dai yana dakina to fa sai sanda yaga dama zai dawo, in yi kwalliya in ta jiransa a banza.
Karfe shida fa yake dawowa, amma ni jiya sai sha dayan dare. Nayi magana ya shiga fada min maganganu, har da yin yaji yana kwana a falo.
Kuma gashi babu sirri, da safe yaje ya barbada ma matansa komai.” Ran Anty Maimuna ya baci, ta ce “To mene ne na zuwa ya fada musu don yaja miki raini?”

Nafisa ta ce, “Hmm! Ni yanzun ban san ma me zan yi ba wallahi.” Anty Maimuna ta ce, “Muje kicin din.” Suna girkin tare tana ci gaba da karanto korafinta.
Anty Maimuna ta ce, “Gashi can nazo miki da wasu sirrika na mata, wata ke kawo wa barikinmu daga Maradi (Nijar). Kayanta masu kyau ne sosai, don akwai wata kusa da mu, mijinta kwallon dan neman mata ne na gaske, gata da yara biyu, amma baya ba su abin kirki, ba fa karamin Soja ba ne.
Ai ko da na hada ta da matar nan, kin san Allah yanzu baya wannan yawon, kuma duk hakkinsu da ke wuyanshi yanzun yana saukewa, har da mota ya sai mata yanzu.”

Nafisa cikin fara’a ta ce, “Ai ko zan ansa.”
Anty ta ce “Amma fa suna da tsada, Allah Yasa
dai kina da kudi.” Nafisa ta tabe baki, “Ina zan ga
kudi? Kin san Allah sisi bai bani ba, ban san suba”
Ta ce, “Zan biya miki wannan, gaba na san za ki zo da kudinki.” Nafisa ta ce, “Nawa ne kudin?” Tayi dariya tare da fadin “Kyaji in lokaci ya yi.’ Nafisa taji duk kuncin da ke ranta ya kau, sannan taji tana jin yunwa, dama dai burinta ta zama ‘yar gaba-gaba a gurinsa.
Daidai wannan lokacin Salma ta fito gurin Maigadi zata bashi sako. Tana jin kunyar aiken dattijon wanda tasan zai haifi mijinta ma bare ita. Ta risina.
“Baba dama sako ne zan baka.” Ya ce,
“Alhajin ya fada min. Ta mika mishi dubu daya, “Kubewa danya ni ke so da kuma nama.” Ya ce, “Kubewa ta nawa?” Salma ta dan yi shiru, bata san ta nawa zata isheta ba, don haka sai ta ce bari in tambayo Anty.”
Ta samu Aliya tana kallo, ta ce “Anty kubewar nawa zata ishe mu ni da Yaya?’ Aliya ta ce, “Ta dari daya ma kacal ta isa, yau kuma tuwo za ki yi?”
Ta ce, “Ya ce yana son cin tuwo ne in yi
mishi.” Aliya ta ce, “Lallai kuwa, sai ki dage kiyi
shi me kyau yanda zai ci.’ Salma cike da wauta ta
ce, “Hala ya fada miki bai taba cin abincina ba?”
Aliya ta ce, “Ya fada min wai ba ki iya girki ba.” Ta fada cike da son tura ma Salma haushi. Salma ta saki dariyar wauta. “Ai yau zan bashi mamaki, zan yi tuwon da zai yi santi.
Aliya ta taba baki, a ranta ta ce, “Wannan sokuwa ce, to sai ya ci tuwon in gani.” Ta ce, “In
ko haka kike so sai ki sa kifi, kubewa danya tafi dadi da kifi.”
Salma ta ce, “Haba?” Aliya ta ce, “Allah kuwa.” Salma ta ce, “Dama na gaji da cin nama. Kullum sai na sa kilo daya a dan abincina, kuma baya ci.” Aliya ta ce, “Ai gashi nan kin soma kyau.”
Salma ta ce, “To bari in je in sa ya siyo min da kifin.” Aliya ta saki dariya bayan tafiyar Salma ta ce, “Shashasha. In ni ce ke bani da da, bakina ni kadai kullum a bani dubu daya ta kilon nama ai tarawa zan.
Bai zama dole in ci ma nama kullum ba. Amma ba zan fada mata ba tayi ta dirkar namanta. Ta ba Maigadi kudi, ya siyo mata kifi da kuɓewa.
Da ya dawo sai ya kawo mata kifi busasshe da kubewa, ya kuma bata canjin dari uku. Ya ce, ta ce kayi na mota Baba. Ya ce, “Eh har ma na sai goro na ashirin in nayi canji zan ba ki.” Ta sake daukar Naira dari ta ce, “gashi Baba ka kara, wancan ma ka bar shi.”
Ya ce “To na gode.” Ya amsa. Har zata wuce ya ce, “Hajiya za ki ga na siyo miki kifi busasshe, Maigidan naku ba ya son danye. Domin waccan satin , Hajiya din nan ta karshe.”
“Bani in sai mata.” Sai Alhaji ya ce, “Kada tayi abinci da danyen kifi don ba ya so.
Salma ta ce, “To’na gode Baba.” Ta wuce ciki ta koma aikinta. Ta nutsu sosai ta zauna a gaban girkinta, ta gama ta kwashe a bakar leda guda biyu ta sa a kula.
Sai ta saka sauran ta kai wa Maigadi, don kullum ita ce kadai ke kai mishi abinci, sannan ta dumama abincin ta na jiya ta taci.
Da yamma tayi wankan ta tasa leshinta na akwati, don sabbin kayan ta ke ta mirtsika tunda ba a sako mata kayanta na gida ba, dama sun tsufa.
Sai da yayi Ishsha ya shigo gidan don yaje yayi aski. Yana shigowa ya wuce wanka. Da jallabiya ya zo ya zauna zaman cin tuwo, tana budewa ta juye a plate. Ya ce, “Iye! Lallai yau zan ci tuwo.”
Ta ce, “Naga kullum nama shi ne nasa maka kifi.” Cikin sauri ya ce, “Kifi?” Ta ce, “Bushasshe ne fa.” Ya ce, “Amma miyar bata yi karni ba dai ko?” Ta ce, “Har citta nasa don kada tayi karni.” Ta bude jikinta a sanyaye.
“Ci kaji kuma.” Ya shaki kamshin, bai ji karni ba, don haka ya ce “To ba ni cokali.” Shi kanshi ya ji mamakin tuwon da ya ci. Tare suka ci da Salma har da suka rage ya ce tayi masa dumame da safe
Ta ce, “Dama kana cin dumame?” Ya ce, “Ni da dumame nasan dadin tuwo ma, gidan Kaka in na kwana lokacin ina dan makaranta Kaka take yi min, sai ta ce dumamen gata, tasa min man shanu har da yaji.”
Salma tayi ta dariya “Nima ina son manshanu. Ya ce, “To zai siyo muku.” Ta ce, “Ka ce zamu yi maganar zuwanmu Zariya.” Ya ce, “Bari in kira Auwal ya kai ma Inna ku gaisa, shi kenan?”
Ta ce, “Allah Sarki, ka ce min zan je.” Ya ce”Ban ce haka ba fa, na ce ne in na dawo zamu yi maganar. Ta ce, “To yaushe za ni?” Cikin shagwaba take yin maganar. Ya ce “Sai kin yi kiba tukuna.” Ta ce, “Don Allah Yaya ina son ganin Yaya Hadiza ma.” Ya ce, “To ki bari sai kin kara kyau.
Ta ce, “Ya za ka gane na kara kyau?” Ya ce, “Ai ina kallonki kullum.” Ta ce, “Me na kara?” Yace “Haske kadai ki ka kara, sai fatar ki da ta soma murjewa, Ta tashi ta dauko dari biyun ta ce, “Gashi canjin ka na tuwon.” Ya ce “Har da canji?” Ta ce, “Eh.” Ya ce, “To ki aje min.” Ta ce, “To.” Ta tashi taje ta aje.
Baccin Amna ya soma damun Shatima, domin yau da ya ke dakinta ma baccin take kwasa babu alamun zasu yi wata hira, shi kuma yana da bukatarta.
Yayi ta tashinta da kyar ta tashi zaune tana zuga hamma. Ya ce, “Amna!” Ta dube shi idanu lumshe, ta ce “Umm, don Allah Honey bacci nake ji.” Ya ce, “Amna, ki tashi don Allah.”
Ta kara cewa “Please, ka bar ni mana.” Ya ce, “Allah sai kin tashi.” Ya girgizata. Ta tashi, “Honey kaina ciwo yake yi, in ban yi bacci ba.” Ya ce, “To kin ci abinci?” Ta ce, “Bana jin yunwa, sai bacci.”
Ya ce, “Kai ki tashi muje asibiti.” Ta ce, “Ni
lafiyata lau, bacci ne kawai matsalata.” Ya bar ta
yazo ya gama duk abin da zai yi kafin ya kwanta.
Sannan yaje ya jata jikinshi ya kwantar suka ci
gaba da bacci.
Da kyar yasa ta tayi sallar Asubahi, don haka ya soma tunanin lallai babu lafiya. Ya kira Aliya a waya da safen yana tambayarta me yake saka mace yawan bacci? Aliya ta ce, “Dalilai da dama, ciki har da shigar ciki.”
Ta ce “Wacece?” Ya ce, “Amna ce, yanzun ya za ayi a gane?” Ta ce, “Gwajin fitsari, tayi a wani abu ka kawo in gwada.”
Da yake ranar Asabar ce ba shi da aiki, bai ko fito gaida saura ba, yana dakin ya sata gaba yana kallo “An ce tana da ciki.” Sha daya ta farka da yunwa, ya ce tayi wanka taji karfin jikinta. Ya ce”Me za ta ci?” Kafin ta fito yasa me aikin ta tanadar mata. tana ci zuba mata ido yayi. Ta ce, “In za ka ci muci mana.” Ya ce, “A’a ki ba babyna ya koshi.” Ta saki dariyar da ta sa ta ta kusan kwarewa.
Ta cc, “In ji wa?” Ya ce, “In ji masu ilimin abin. Yanzun ma fitsari za ki bani in kai a gwada. Ta ce, “Wa zai gwada?” Ya ce, “Aliya kin san Nurse ce. Ta ce, “Wace ce Aliya kuma?” Ya ce, “Ta dakin farko.”
Ta tabe baki “Oh, dama a nan gidan take? Ya ce, “Eh.” Ta ce, “Cikin matanka?” Ya ce, “Eh.” Ta girgiza kai “Ba wadda zan ba fitsarina, don ni ba tsararsu ba ce. Kuma bana dauke da wani ciki domin lokacin al’adata bai yi ba bare in tabbatar. Abin da na sani bacci lafiya ce, ina rama baccin da ban yi ba ne a baya lokacin ina Makaranta, da kuma lokacin biki.”
Yayi murmushi, “Shi kenan muje asibiti.” Ta ce, “Wane irin asibiti, ba zan je ba.” Ya ce “Shi ke nan.
Aliya tayi ta damuwa tana son jin me ake ciki da batun cikin Amna, ga na Nafisa. Koda ta kira Shatima cewa taji shiru bai kawo fitsari ba. Ya ce, “Ashe babu komai ta bar shi kawai.”
Suna cikin hira ta gama cin abinci, sai taji zuciyarta na tashi. Ta ce, “Honey zuciya tana tashi, naci abinci da yawa.” Ya ce, “To kin taba jin haka?”
Ta ce, “A’a sai a ‘yan kwanakin nan. Abin kamar wasa Amna ta shiga bandakinta tana sheka amai. Nan fa Shatima ya ce sai sun je asibiti. Ita kuma ta dage ai taji daidai da ta yi amai din.
Yayi ta lallashinta amma ta ki. Ya kira Hajiayrshi ya kai mata kara. Nan take ta kira layin Amna, cikin sigar lallashi ta ce, “Amna ta yarda taje a dubata.” Ta ce, “To Hajiya.” Ta dube shi, “Ka ci albarkacin Hajiya.”
Sai da suka yi sallar Azahar sannan suka shirya zuwa asibiti, doguwar riga ta saka da dan mayafinta, shi kuma yasha kananan kaya. Sun yi kyau abin su sosai
A kan idon Nafisa da Aliya suka wuce. Kowaccansu da abin da ta kisima a zuciyarta. Cikin gari suka shiga, in da ya kaita wani asibitin kudi gwajin nan take kala biyu suka yi mata.
Cikin sati uku da kwanaki ya bayyana. A gaban Likitan Shatima ya rungume Amna. A nan ya kira Hajiyarshi ya fesa mata. suna hanyar dawowa a mota Hajiyar ta kira shi.
Ta nuna matukar murnarta da samun cikin, kuma ta ba ta shawarwari matsayinta na uwa. Amnar tayi godiya, suka yi sallama. Har suka kai gida Shatima na yiwa Amna sannu da zaran sun hada ido.
Da ya tsaya da mota kuma bayan sun kawo gida, cikin shagwaɓa ta ce sai dai ya dauke ta. Ya ce, “In kullum ki ke son in dauke ki wannan abu ne mai sauki.” Kafin ta ce da wasa take yi har ta ji ta caraf a hannunshi ya yi sama da ita, yasa kafa ya rufe motar.
Bai dire ta ko’ina ba sai a kan gadonta. Ya kira Aliya a waya ya fesa mata. Tayi murna sosai a wayar amma a can kasan zuciyarta takaici ne da damuwa.
Ranar yana dakin har bayan Isha’i, sai da suka yi sallah yaga ta dan ci wani abu sannan ya
lallabata tayi bacci, sannan ya fita bayan ya fada ma mai aikinta cewa ta kula da ita saboda dare.
Dakin Nafisa ya nufa dama can yake, in san
ranshi ne yaje ya duba Salma don bata da wayar da
zai ji laifiyarta, amma baya son mitar Nafisa. Lokacin da ya shiga gurinta ba ta falo, dakin shi ya shige don ya yi wanka, bai neme ta ba ne don yasan yanda suka rabu.
Haka ko ya shigo dubata a ranakun da ba ya dakinta gaisuwa ke hada su. To bai san irin tarbar da zata yi masa ba yau. Ya fito daure da Tawul ya ganta cikin kwalliya ta aje masa goran ruwa da kofi a gefen gado kamar yanda aka saba.
Ya kalle ta cikin murmushi, a ransa ya ce, “Yau da akwai abin arziki.” Ta miko masa kayan baccinsa yasa, ya dube ta. “Turarenki yayi min kamshi sosai.” Ta fadada fara’arta. “Haba?” Ya ce, “Sosai ma, za ki sammin?”
Ta ce, “A’a, za dai ka dinga shakar sa a jikina.” Yayi ‘yar dariya. “Hakan ma na gode.” Ta ce, “Muje ka ci abinci ko? Kus-kus ne nayi maka da fa-dukan shi, yayi dadi.” Ya ce, “Lallai kuwa kin ce yau in ci har in kasa tashi.” Suka yi dariya gaba daya.
[8/18, 17:54] Ummi Tandama????: _
????️RANA DAYA BOOK 2????️

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button