SALON SO COMPLETE NOVEL

SALON SO COMPLETE NOVEL


Bari mu waiwayi Kausar don muga wace rayuwa take y ne.”
Kausar tun ranar da ta bar gidan Haidar ta sauka a
gidansu Abuja.
Iyayenta sun tare ta da murna amma ganinta da
shirmin akwatuna sai jikinsu ya yi sanyi suka shiga
tambayarta da lafiya? Kausar ta gaya musu karya da gaskiya na ciwon
Haidar sannan ta mika musu takardar sakin da ya yi
mata. Ba su ji wani zafin sakin da ya yi mata ba don
su a ganinsu gwanda hakan da ‘yarsu ta takura,
‘yan aikinta suka shiga gyara mata wajen zama.
Kwanaki kalilan a tsakani mahaifanta suka tura kano gidan Haidar don kwaso kayan Kausar suka
tarar da gida a kulle sai megida ne yake yi musu
bayanin ai ba kasar, sai gidan su Haidar din suka je
suka yi wa Anty bayanin zasu kwashi kaya.
Anty ta yiwa Yaya Abba waya yazo ta bashi
mukullayen ta ce ya je ya bude musu gidan ya tsaya su kwashi iya kayansu.
Haka kuwa aka yi, ya je ya bude musu ya jira suka
gama kwasar kayansu ko tsinke basu bari ba,
bayan yin iddar Kausar ta bude shafin zawarci in da
manema kuwa suka yo mata ca! Ganin ta fito daga
gidan mekudi ga ta kuma ‘yar mekudi. Kausar abinka da goggiyar tuni ta kuma wanke
fata ta tsunduma cikin zawarci. Manema da yawa
sun firfito mata sai dai rashin sa’ar da ta yi, duk
cikinsu babu saurayi, daga me mata daya sai me
mata biyu.
Hakan ne yasa ta riki Bomboy dinta. in da ya fito ya kawo
kudin aurenta ba dadewa ba aka sa ranar biki an
sha shagali da casu kamar na budurwa.
Ta tare a gidan ta dake nan K/Maiyaki. Bomboy dai ya dauki matar sa kauthar kamar wata sarauniyaba abin da be ajiye mata ba na jin dadin rayuwar
dan Adam. Ba ruwanta da girkin gidan kullum sai
dai ya dauke ta zuwa hotal su ci abin da ransu yake
so, ruwa sai da na roba wato swan.
Kowanne lokaci firji dinta cike yake da kalolin
abincin gwangwani da kalolin lemummuka. Tuni Kausar ta kara gogewa jin dadi da hutu ya
kara samun mazauni kome sai dai ‘yan aikinta su yi
mata bata katabus koda yaushe aikinta kwanciya
ko ci.
Ana cikin haka ne aiki ya kuma mayar da iyayen
Kausar kasar America. A lokacin kuwa Kausar da Bomboy ba sa kasar don haka bata sani ba
don iyayen nata sun ta lalubenta a wayarta ba su
same ta ba, sai sallahu suka bar mata gun ‘yan
aikinta suka daga zuwa America.
.
(((((( SALON SO ))))))
:
KARSHE!
PART 42.
.
Ranar da Bomboy da Kausar suka dawo da
ga tafiya, ‘yan aikinta suka gabatar mata da sakon
iyayenta. Kausar har kuka ta yi don bakin ciki gashi wayarta da lambobin iyayen nata suke ciki ta fadi a
wannan tafiyar da ta yi, don haka ba wata hanya
da zata ji su ba damar ta yi musu waya kenan, ko
su yi mata?
Ga shi bata san address din su a American ba, bare
wata rana ta kai musu ziyara dole ta dauki dangana da hakuri ta na me fatan Allah sa su zo nan kusa
don ta ji cikakken address dinsu ko ta bisu su tafi
tare. Ba dadewa Kausar ta gama da laulayin ciki me
wahalar gaske bata iya cin abinci sosai ga azabar
ciwon ciki da ciwon kai. Hankalin Bomboy
ya tashi da ganin rashin lafiyartata. Ya kwashe ta suka nufi asibiti akayi mata tes da
gwaje gwaje daga karshe likitan ya dauki fitsarinta
ya ce, gobe a dawo a karbi ruzol suka taho a hanya
ya yi mata siyayya fal irin na marasa lafiya ya dawo
da ita gida.
Da gari ya waye Bomboy da kansa ya je ya karbo sakamakon gwajin da aka yi mata hankalin
Bomboy yayi fari da ganin wannan sakamakon
Murna a gun shi da Kausar kuwa kamar su hadiye
juna don murnar samun ciki Kausar ta fara
kawowa Bomboy tsarabe-tsarabe, ta ce
wannan ta ce wannan haka Bomboy zai je ya kwaso mata. **** **** *
Sannu sannu rayuwa ta juya ta juyawa
Bomboybaya domin kudin hannunsa tas sun kare
‘yan aikinta wuya ta ishe su duk sun gudu sun
barsu, sai ga Kausar ta je ta na rokon matan yayun
Bomboy da su taimaka su rinka sammata abincinsu, su kuma suka ce muddin tana so ta
rinka cin abincinsu sai dai ta fito ta rinka girkawa
don babu bawanta da zai rinka dafawa yana bata
tana ci.
Dole Kausar ta fito tana girkawa da safe koko ne
za’ayi shi tsilulu saboda babu wadatacciyar gasara, rafin kofi ake rabawa kokon ga ba kosai da rana a
jika garin kwaki a yayyafa a kasan roba yaro ma
baya koshi bare babba.
Da daddare datsar dawa za a tuka bakikkirin da
koriyar miyar kuka wadda daga daddawa sai
barkono a ciki. Kausar ga fama da ciwo ga shi yanzu cikin nata ya
kai wata shida ya yanzu cin abinci ne da ita saboda
cikin yana sata masifaffiyar yunwa. Ga abincin da
ake bata baya isarta, ga rashin dadi haka take
hakura ta tattura, ga shi duk ta yi baki ta rame ta
kanjame ke ba kya ce ‘yar hutu Kausar din da ba ce.
Duk ta bushe sai kashin wuya da tsinin ciki gashi
bata iya yin tuwon ba duk ranar da ta yi sai yai
danye ko ya yi gudaji.
Ga matan yayye da ‘yansu si yi mata masifa sun
dungure mata kai suna yi mata ba la’i, dole ta jure ta hakura take zaune don bata da gurin zuwa in ma
ta fita ga iyayenta har yau bata samu labarin su ba,
to ina zata samu kudi xuwa American ma bare ta
binciko in da suke.
Don kayan dakinta kaf ta sai da su ta ci abinci
duniya kenan me juyi juyi. **** ****** ****** Jawahir watanta biyar kenan da haihuwa ita da ‘ya
‘yanta sun kara kiba da haske sun yi kyau jajir da
su kamar ‘ya ‘yan Turawa. Kowa ya kalle su sai ya
yi sha’awar cewa da ma dai iyalinsa ne.
Haidar arziki ya ci uban na da, ya tanfatsa musu
wani tsantsareren gida na gani na fada wanda duk wanda yaje gidan kallo abinda yake fadan shi ne
aljannar duniya.
Gidan ya
tsaru iya haduwa ya hadu, yanda Haidar ya
hadewa jawahir falonta da dakunanta ko na
sarauniyar indiya albarka Dakin ‘yan uku kuwa ke kya ce kamfani ne
tsadadde na kayan wasan yara saboda kayan alatu
da suke ciki, Haidar ya kara girman da murjewa ya
zama Alhaji me tsananin kyau da kwarjini.
Jawahir ta zama big madam cikakkiyar mace ga
kyau ga hutu ga kwarjini ‘yan ‘ya’yayansu guda uku abin sha’awa tubarkalla, bul bul da su jajir da
su gashinsu akanannade kamar ‘ya’yan turawa.
Mijinta ya sakar mata naira sosai don duk wasu
takaddun kamfanoninsa da gidajensa da filayensa
da duk wasu kadarorinsa suna hannunta. Baya yi
mata geji akan komai duk wani abu daya kamata ya yi na game da biyan ma’,aikatansa
albashi na kamfanoninsa zuwa na gidajensu, ya ce
Abbansa ya kwanta ya huta shi yake komai na
gidansu.
Jawahir ta kasance me taimakon talakawa da
kaskantattu wadanta basu da watada, don haka gidan nasu kullum yake cike da ‘yan neman
alfarma.
‘Yan uku suna da shekara daidai ta yaye su sun yi
girma sunyi wayo gudunsu suke yi ko ina ga
surutu kamar Aku. Suma hadadden falonsu duk
sun ci kwalliya kamar masu shirin zuwa fati, Haidar yana ta wasa da ‘ya
‘yansa ya ta da kai da cinyar jawahir Salim da Sadat
shiga iri daya akayi musu ta jins da T shirt fara da
aka yi rubutu da ruwan gwal a gaban rigar.
Salma ma tana sanye da dan jins dinta da ‘yar riga,
kunnanta da wuyanta yana sanye da yari da sarka kirar daimond ‘yar xire, kanta ya sha kananan
kalba da kanan ribon a jiki yaran sun yi kyau
kamar ‘ya ‘yan turawa.
Gaba daya yaran suna kan Haidar suna ta tsalle
tsallensu a jikinsa, wayar ku sa da jawahir ta yi kara
ta daga ta kara a kunnenta, “Hello yauwa Anty jawahir wallahi wata bakuwa ce tazo ta kafe lallai
tana son ganinki.
Jawahir ta ce “Okey ba damuwa kawo ta muna
falon sama
Ta dire wayar, bakuwar da tun shigowarta ta saki
baki tana ta kalle kalle a cikin gidan babu abin da ya fi kayatar da ita irin tsantsara tsantsaran falon da
suka rinka wuce su, jikinta bai kara yin sanyi ba, sai
da suka shiga wani tsantsareren falo wanda ya
hadu da kayan kyale kyale sai wata hadaddiyar
matattatakalar bene wadda aka yi ta kamar da
ruwan gwal. Kasan matattakalar shimfide yake da kafet, suka
hau suka yi sallama falon suka shiga.
Jawahir ta dago kai tare da amsa sallamar ta zuba
wa matar ido, tana tunanin ina ta santa. Matar ta
zube a gabansu tana kuka Haidar kuwa yana ta
wasa da ‘ya ‘yansa be ma dago kai ba bare yasan wacece.
Jawahir ta ce a’a baiwar Allah me kuma yake
faruwa daga zuwa sai kuka ba tare da kin yi wani
bayani ba.”
Ta kwanto yan kwananniyar’yarta daga baya
wadda shimi ce kawai a jikinta saboda rashin sutura matar kuma atamfa da take jikinta duk ta
kode ta jeme ga hadin baki a jiki matar ta ce “Ban yi
mamakin yanda baku gane ni ba ni ce Kausar.
Jawahir ta
yi zumbur ta mike tana rike da baki cikin mamaki ta
ce “Kausar ke ce rayuwa ta maida ki haka me ya faru dake Kausar ina iyayenki da mijinki.?”
Kausar ta goge hawayenta ta shiga basu labarin
iyayenta da halin da take ci, ta juya tana kuka tana
rokon Haidar gafara Haidar ya ce “Ni wallahi ba
komai don rabuwa da ke alheri ya zamar min don
da ina tare da ke da ban sami zaman lafiya da kwanciyyar hankali haka ba.” Ya mike goye da
Salma ya dauki Salim da Sadat a kafadarsa ya shige
ciki.
Kausar ta bisu da kallo tana me sha’awarsu shi da
‘ya ‘yansa da matarsa da ta yi hakuri da yanzu
itama tana cikin wannan daular. Jawahir ta girgiza kai zuciyarta cike da tausayin
halin da ta ga Kausar. Lallai duniya zancan banza ce
kana takama kai wani ne lokaci daya sai Ubangiji
ya mayar da kai ba komai ba.
Jawahir ta ce Kausar “Ki yi hakuri lamarin duniya
kenan don haka ba a son daukan duniya da zafi. Ta mike ta shiga daki ta debo sababbin riguna kala
takwas da turamen atamfofi kala hudu da
dinkakku kwance kala shida, da kudi naira dubu
hamsin ta kawo mata ungo wa’yannan kije ki yi
amfani da su zan kuma sa abinciko min koda
lambar wayar iyayen naki ne kin ji ko.” Kausar ta rissina ta rinka godiya tana kukan murna.
Jawahir sai da ta sa aka hada mata kayan abinci fal
bayan but din mota tasa direba ya kaita har gida.
Kausar tana komawa ta sai rishonta ta sai kananzir
galan guda ta kai dakinta take girkinta ita kadai ita
da mijinta suna ci ta daina kula abincin gidan Nan fa matan gidan da ‘ya’yan gidan suka tusa ta
agaba da habaici da bakaken maganganu ita dai
bata kula kowa sai ta rinka kulle wajenta ma ta
daina sauraronsu.
Sati biyu a tsakani jawahir ta ba wa direbanta waya
sabuwa da kudi dubu goma a ciki da lambar wayar iyayen Kausar ta ce ya kai wa Kausar.
Direba ya kama hanya ya kai wa Kausar ta rinka
murna tana kwarara wa direba godiya ta ce ya
mika mata godiya wajen jawahir din kafin tazo.
Direba yana tafiya, Kausar ta kulle dakinta ta buga
wayar bugu uku ana hudu aka dauka. Muryar babanta ta ji ta fashe da kuka, “Dady, Dady
nice Kausar kun gudu kum barni cikin halin kunci
da wahala.
Tana kuka tana gaya masa halin da ta ke ciki da ita
da mijinta tace yanzu mijinta bashi da komai suna
cikin kuncin rayuwa hatta lokacin da ta haihu bai yi mata komai ba, da yunwar da ta sha da bautar
girkin da take yiwa matan gidan da irin tsangwama
da cin mutuncin da ake yi mata har kawo irin
taimakon da jawahir take yi mata da binkicen da
jawahir ta yi ta samo mata lambarsu ta kawo mata
sabuwar waya da kati na dubu goma a ciki duk ta gama gaya masa.
Hankalin
babanta ya tashi ransa ya damu ya ce mata kiyi
hakuri da man kwanan nan muke son mu zo mu
duba ki ganin mun shekara daya da baro Nigeria.
Amma kisa idonmu a cikin satin nan muna tafe.” Hankalin babarta da ‘yan uwarta ya yi masifar tashi
da jin halin da Kausar ta ke ciki, ai basu iya hakuri
ba kwanakin ba cikin kwana uku suka dira a
Nigeria.
Iyayenta da ‘yan uwanta har kuka suka yi jin halin
da Kausar ta shiga, nan fa aka shiga bata kashi tsakanin Bomboy da iyayen Kausar da kyar
suka samu ya sake ta.
Bayan ya sake ta ne, ya shiga daki yai ta kuka har
da ihu shi ya shiga uku. Yanzu yaya za ayi ya kuma
wani auren?” Da kyar su Amal Junior da Jauhar M.
Nas suka rarrasheshi. Suka zo suka ta yiwa jawahir godiya tare da sa
mata albarka.
Suka roki kuma Haidar gafara a bisa abin da Kausar
ta yi masa ya ce “Ba komai ai ya yafe mata.
Nan fa kyakkyawar alaka da zumunci ya kullu
tsakanin jawahir da Kausar da kuma iyayensu. Satinsu uku a Nigeria suka daga da Kausar da
‘yarta da iyayenta zuwa America.
Cikin lokaci kankani Kausar ta murmure ta murje ita
da ‘yarta ssuka shiga shafe shafen da ya bayyanar
masu da kyansu. Bata dade da gama idda ba
manema suka fito mata in da ta sake auren wani mai mata daya da ‘ya’ya uku.
Ya riki kausar da ‘yarta cikin gaskiya da amana in
da suke zaman lafiya da abokiyar zamanta.
Haidar da jawahir linkafa ta ci gaba sun zamo abin
kwatance da sha awa a Nigeria suna da ‘ya’ya biyar
kenan ‘yan uku Salma, Sadat, Salim sai Nana khadija da Mohammad auta.
Rayuwarsu me burgewa da ban sha awa kowa ya
shiga gidan baya son fita don ganin irin
rantsattsiyar SALON SO, ya yarda suke shimfidawa a
gidan. KASH DAMA ANCE LAIFIN DADI KAREWA.
DUKKAN YABO DA GODIYA SUN TABBATA GA UBANGIJI DA YA BANI DAMAR KAMMALA KAWO
WANNAN LITTAFI KAMAR YADDA MUKA FARA.
TSIRA DA AMINCI SU KARA TABBATA GA SHUGABA
ANNABIN RAHMA (S.A.W), ALAYEN SA DA
SAHABBAN SA. DA FATAN MUN KARU DA DARUSSAN
DA MUKA GANI A CIKIN WANGA LITTAFI, ALLAH YASA MUYI KOYI DA MASU KYAWAWAN HALAYEN
DAKE CIKIN SA YA KUMA TSARE MU DAGA AIKATA
MUNANAN AYYUKA MAKAMANTAN NA WASU DA
MUKA JI A CIKI. TOHHH!!! INA FATAN NIMA XAKU
TAYA NI ADDU’AN SAMUN WATA MATAR TUNDA
MAFARKI NA TA SUBUCE MIN WATO KAUSAR. SAI MUN HADE A WANI SABON LITTAFIN INSHA ALLAH..
MU NA GODIYA KWARAI GA MARUBUCIYAR LITTAFIN WATO,
HADEEZA SALISU SHAREEF
SAI NI DA NA KAWO MU KU,
SULAIMAN BOMBOY
NA KE MU KU,
WASSALAM.

Previous page 1 2

Leave a Reply

Back to top button