Lu’u Lu’u 12

*12*

 

*Ayam* na komawa b’angarensu d’akin baccinsu ta shiga, kayanta ya cire tz d’aura towel ta shiga wanka, sa’ilin da ruwan ke sauka kan ta ta samu damar rufe ido, a lokacin tunanin mafarkinta ya dawo mata wanda su Deeyam su ka katse mata shi a daren jiya, haka kuma ta had’e abun ta ba tare data yarda kowa ya ji ba, d’an gashinta daya had’e da juna ta shiga murzawa tana mayar da shi bayanta tana gumtsar ruwa a bakinta tana tofowa, idonta a rufe suke k’am ta shiga fad’a a ran ta “Me mafarkin ke nufi? Ko dai mafarki ne kamar kowane? To amma me yasa matar ba tayi kama da wanda na tab’a sani ba?”

Da sauri ta bud’a idonta sakamakon jin motsi a d’akin, amma sai ta share ta ci gaba da wankanta kawai, dan tunaninta su Deeyam ne.

A tsanake ta k’arasa wankanta ta d’auro towel, hannun k’ofar ban d’akin ta kama dan bud’ewa, tana zuro k’afa d’aya ta fito ta k’arasa fito da k’afar d’aya tana fad’in “Ke! Me ya kawoki n…”

Wani duka aka mata a kai ba tare da imani ko tausayawa ba, ko shurawa ba tayi ba ta fad’i gure a sume inda kan ta ya b’alle da jini a k’eyarta, cike da jin dad’i da farin cikin zata cika burinta a kan ga Zafreen ta kece da dariya ta mik’e tsaye tana kallon k’akk’arfan matashin da suka saka ya musu wannan aikin, wanda saida suka jadadda mishi ya mata dukan da zata suma.

Tafa mi shi tayi da murna tace “Aikinka na kyau, nagode sosai.”

Laika dake gefenta ne tace “Gaskiya ne, ni ma ki min godiya.”

A wulak’ance ta kalleta tace “A kan wane dalili?”

Shiru Laika tayi saida Zafreen ta juya bayanta ta maida hankali ga Ayam dake yashe kwance, bata ankara ba Laika ta d’auki hoton dake aje gefen gadon Sabrine na ita da danginta, sai kuwa ta fasawa Zafreen shi a kai har saida madubin ya mutu a kan ta, take ita ma ta zube bayan ta dafe kanta tana k’ok’arin juyawa ta kalli Laika.

Kallon juna sukayi Laika ta ciro wata k’aramar waya a cikin rigar mamanta ta danna wasu lambobi ta d’ora a kunne, a tak’aice tace “Angama.”

Tana aje wayar sai kuwa wata irin kara ta gauraye makarantar an danna na’urar dake nuni da idan wani had’ari ya samu musamman ma gobara, ai kuwa tuni hatsaniya ta kaure a makarantar dan kuwa sauran munafukan da ke tare da su Laika ne sukayi nasarar tashin zanga zanga a ciki, sai gashi sun fara farfasa abubuwa har da motocin malamai da ofisoshinsu.

Makaranta ta hautsine, duk jami’an sun yi iya k’ok’arinsu amma abun da gaske fin k’arfinsu aka yi, ana cikin hatsaniyar nan aka fitar da Ay da Zafreen ta bayan makaranta inda jirgi ya d’aukesu, Laika ma da tawagarta sulalewa sukayi suka bar makarantar, inda suka bar wanda basu ji basu gani ba a hannun jami’an makarantar suna son hukuntasu da laifin tayar da tarzoma.

Tunda ya doso ya ga wannan hayaniya da tashin hankali jikinshi ya bashi babu lafiya, yana fitowa daga dalleliyar ferrarin nan da gudu ya nufi inda yake tunanin samunta, bai damu da kowa ba da kuma abinda kowa zai fad’a.

Yana zuwa b’angarensu yayi sa’ar kicib’is da su Sabrine sun fito da gudu zasu fita, hannun Deeyam ya rik’o da sauri yace “Tana ina?”

Girgiza kai tayi tace “Mu ma ita muke nema, mun shiga d’aki amma bamu sameta ba.”

“Shiiit!” Ya fad’a yana sake zubawa a guje ya juyo ya sake tambayar “Ina d’akin?”

Nuna masa tayi da hannu, bai jira komai ba ya bangaji k’ofar ta bud’e ya shige, turus ya tsaya kallon d’akin, da gudu ya k’arasa gaban tagar daya gani bud’e ya lek’a, tabbas ko ma su wanene ta nan suka fita da ita, ga alamu nan ya nuna har da sawayen takalmi.

Dafe gaban goshinshi yayi yace “Ya Allah! Su waye kuma yanzu?”

Wayarshi ya ciro da sauri ya shiga daddanawa ya d’ora a kunne, jim kad’an Haman ya d’aga, cikin tashin hankali ya nufi hanyar fita a d’akin yana fad’in “Haman kana ina? Akwai matsala fa.”

Shi ma hankali tashe yace “Matsala kuma? Me ya faru?”

Da azama yace “Kai dai ka fad’a min inda ka ke zan zo na sameka.”

Da sauri shi ma yace “Ina nan masauki na dana fad’a maka.”

K’itt! Ya yanke kiran ya shiga takawa da sauri har ya k’arasa ga motarshi ya shiga ya sake barin harabar makarantar.

*Egypt*

Babban masaukin daya tanada dan wannan ranar yasa aka sauke mishi su, ya kashe kud’i masu azababben yawa dan kawai ya k’awata mata wannan gida, Zafreen ce ta fara bud’a idonta a hankali da suka mata nauyi har suka d’an fara kumbura, a hankali ta zura hannunta ta dafe k’eyarta saboda tuna abinda ya faru, a sanyaye ta furta “Wash!”

Muskutawa tayi ta tashi zaune sai kuma ta zabura da k’arfi saboda ganin Ayam kusanta kwance ita ma, juyawa tayi dan son ganin ko akwai wani kusansu, sai kawai ta ga kan ta a madubin drower da Bukhatir ya shak’ewa Ayam kaya da ita, saboda a bazata ta ga kanta sai ta saki yar k’arar data saka Ayam motsawa ita ma, tana bud’a ido ta sauke akan kwalliyar rufin d’akin wacce aka yi kamar da gwal aka yi ta.

Ganin Zafreen yasa ta yunk’ura da sauri ta tashi zaune, za ta yi magana sai kuma ta dafe kan ta da ta ji yana mata ciwo sosai, d’an kallon kanta tayi sai ta ga daga ita har Zafreen an nad’e musu kai da bandeji fari, kallon Zafreen tayi tace “Ina ne kika kawo ni nan? Ke ba fa na son iskanci kin ji ko, ki fita a harkata kafin na sake b’ata miki rai.”

K’wafa tayi ta mik’e tsaye tana k’arewa kanta kallo ta madubin, towel d’in jikinta shi ne dai har yanzu, Zafreen ma mik’ewa tayi tace “Ke kinsan wacece ni? To ni ma ina son sanin inda nake.”

Tsaki Ayam tayi ta nufi inda ta ga k’ofa da niyyar fita, kafin ta isa bakin k’ofar aka bud’o aka shigo, kallon kallo suka shiga yi da k’ akk’arfan matashin dake cikin shiga ta alfarma, had’e fuska Ayam tayi ta dafe k’ugu tace” Wannan wane irin rashin mutumci ne? Ina ne nan kuka kawomu?”

Wani sanyayyar murmushi ya saki ya bud’e hannayenshi zai

rumgume ta, da sauri ta ja baya tace” A’a, kai mahaukaci ina ne? Waye kai?”

Ba tare daya d’auke murmushin dake kan fuskarshi ba yace” *Pr茅cieux*, embrasse moi, tu sais combien da temps je passe a attendre ce jour (mai daraja, rumgume ni mana, kinsan lokacin dana d’auka ina jiran wannan ranar)?”

Nunashi tayi da yatsa tace” Zan wanka maka mari idan ka kuskura ka tab’a ni.”

Murmushi ya kuma saki ya juya ya kalli wasu matasa guda biyu dake gefenshi ya nuna musu Zafreen yace” Ku d’auke wannan daga nan ku kai ta b’angaren bak’i, wannan b’angaren na gimbiya ta Zafeera ne.”

1 2 3 4Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button