SAMEEHA A

_????SÂMÊÊHÂ????_*
*_(A)_*
*_ÑÂ_*
*_(Mâmâñ Dr.@ff@ñ)_*
“”Gafara dai hatsabibi Uban hatsabibai,gaisuwa gareka sarkin hatsabibai tare da neman izinin ganawa,ta nemi gefe guda ta tsuguna,cigaba tayi da,, tsafi yadafa maka hatsabibi uban hatsabibai na iso gareka isowarka nake tsimaya mai biyawa dukkan Wanda yazo gareka buqatarsa cikin sauqi,gani na iso akan lokaci batare da sa6a maka ba ya uban hatsabibai,,dariya aka sheqe da ita wace ta mammaye sassan wajan gaba daya banda amsa amo da ke tashi gabas yamma kudu arewa bakajin sautin komai awajan sai kadawar isaka dake daukar kakkausar muryar tana yawo, kusan mintina (3 xuwa 5)aka dauka dariya bata daukeba chan wani siririn mutum baqi mai qaton Kai da yalwar gashin kai dana fuska ya bayana zaune bisa kan wata tukunyar qasa ‘yar qarama wace ko qafa ka dora zaka iya rantsewa fashewa zatai asakan
(1:),gumtse dariyarsa yai lokaci guda yamurtike fuska kamar bai ta6a dariya adoran qasa ba yamiqa siririn hannunsa sama nan take wani Dan qaramin kwado mai launin qasa qasa ya bayana akan tafin hannunsa na hagu da wasu layu guda biyu da aka rufe da fatar baqin maciji, ahankali yasauke hannun tare da karkatoshi zuwa ga inda Matar ke tsugune kamar mai Neman gafara,cikin kakkausar muryarsa Mara dadin sauraro yace.
“”Ki samu inda kika san ido ko hannu bazasu ta6a kaiwaba ki adana kwadon nan Kamar yanda kika ganshi zaune cikin tukunyar waje daya haka zaki juya jariran biyu batare da daya yayi miki gardama ba har sai kin basu izinin tsale,ma’ana (tashi),duk abinda zasiyi saida umarninki sai sun isar dake koda zasu rasa rayukansa,zasu dinga jin tsoranki akodayaushe ko wuta kika hura kika basu umarin dasu fada to lalai babu shakka zasu fada ciki batare da musu ko gardama ba,wannan layun kuma ki tabbata an bunnesu cikin tsakiyar dakin da suke kwana ki tabbata akansu zasu kwanta,,murmushin jin dadi Matar tayi hade da.
Umm nace idan na ajiye bisa tukunyar ya za’ayi kuma,sarin hatsabibai yace,,buqatarmu kadai a ajiye inda ido bazaijeba hannu bazai kaiba ki adanashi kamar yanda kike Adana kanki mudin ido yagani hannu yata6a to lalai babu shakka zaki rasa abu (3).
Na (1) Zaki dena gani na (2) zaki dena ji na (3) kuma zaki dena magana har abada don babu wani magani dazai iya warkar dake har tsawon rayuwarki Zaki zauna cikin makanta da rashin ji da Kuma gani,,cikin tsoro da firgici mara misali matar ta zaro ido hade da gyara tsugunan datayi saboda qafafuwanta duk sun gaza tace.
Sarkin hatsabibai ba wata dabaran da za’ayii na barshi anan ko a bunneshi kowama ya huta,Sam aikinmu bai ce haka ba yanda muka umarceki dayi hakan shine hanya mafi sauqi da ransa muke buqatarsa idan har aka bunneshi suma jariran biyu zasu zama bunnanu adoran qasa,,,a a abarshi arayan hakan zaifi amma nace cima fa, bai shafekiba kedai kiyi abinda aka umarceki dashi kawai,atsorace tasake cewa,ummm nahhhh……karki kuskura ki tanka idan bazaki iya ba ki 6ace mun dagani ban kawo kiba,ban kumayi miki dole ba ya furta a fusace, jiki na 6ari tace,, zan iya sarkin hatsabibai ko meye ribar aikinnaka,abinda kika sabayi,sarkin hatsabibai yabata amsa ataqaice ya 6ace kamar ba ayishi agunba hannu tasa ta zaro Jakarta ta bude bandir din ‘yan dubu dubu bugun Abuja ta Dora bisa kan wata tukunya dake gefanta ta dauki kwadon dake cikin wata tukunya qarama ta kwashi layun guda biyu ta miqe dabaya dabaya har ta fito daga cikin dutsan ta dauki hanyar da moto dinta yake da zuwa tasaka key tabude mukulin motar ahankali ta zira tukunyar dake rufe da Jan qyale tashiga ta zauna,, hanya ta dauka ranta fall da saqe saqen abubuwa da sama..
★★★
Wani madai daicin gida na hango dake cike taf da mata sai zirga² zirga ake dagani wani sha’anin ake shirin tafkawa aguje na runtuma ina maida numfashi da qyar Dan kar ayi bani,,,ciki na kutsa kai ina jifa ido kamar mara gaskiya na hango wani falo dake cike da mata sai shiryawa suke suna nishadi wasu na tsukanar junna da alama yaran matane dan kowace ta dau magana wato (kwalliya)???? sanyi suke da dogayen riguna (Abaya) kai yadau (rolling) fuska tasha makeup kamar larabawan (Sudan????).
‘Yar kallon kallo nakoma sai binsu nake da ido wannan taci u……..wannan wachan ta kere wachan kowace fuska ta dau magana????duk ba mai muni ciki aradu kamar ‘yartsanoni nace ummm kamfanin (Founditon)na aiki lokaci daya ke chanja baqi ya koma fari fari ya koma baqi kai wani lokacin har jajja,jajja ake komawa,,ga wata jagira mai sifar gatari datashi lanqwasa kai abun dai ba’a magana sai Wanda yagani nidai nayi likimo????Ina qarewa kowa kallo????,,garin kallon naji.
Wata muguwar bangaza da sauran qiris yarage biron danake boyewa a hammata ya fado qasa gashi na basar irin ni dinma a (Family) nake???? da sauri nakai masa wawa????gudin kar nai abin kunya nakoyi sa’a na dafe abina????,,ai tini hankalina yai saurin dawowa ga inda nasha bangazar ai kan kace me na runtuma asitin bayan wace ta bangajeni daganinta kasan dakwai matsala fuskarta Sam ba walwala sai tsagwaran tashin hankali nayi kasaqe ina jiran mai zata furta na antayo muku duk da hararar datake sambado min na basar????.
“””Moona!!,moona,naji matar na Kira da qarfinta charaf wata matashiyar budurwa ta amsa da.
Na’am ya jummai.
Ina *_SÂMÊÊHA_* take?,ai tun dazu suka tafi gidan me Makeup, amma ki kira wayarta mana,nakira kusan (10miss call)bata dagaba,yanzu haka tana jakarta kinsan hankalin duk yakoma wajan kwalliya musamman da lokaci ya qarato amma ki kira qawarta Zee mana ko zaki sameta,kin ko kawo shawara yarinya bani number zainabun muga,ya jumma ta furta tana mai fidda wayarta number Moona ta bata ta saka hade da danna kira ringin biyu zee ta dauka.
Zainabu ya jummai ce ina Sameeha.
Gata nan ana mata kwalliya ya jummai.
Shine naketa kiran wayarta bata dagaba ina ta aje wayar Dan sakarci.
Ajaka ta barta kuma bamuji qaranbane lokacin tana (slnt).
Maza maza ki bata wayar.
Kwalliya ake mata ya jummai.
Ke dan ubanki nace ki bata wayar dani da kwalliyar wayafi mahimmanci iskancin banza Dana wofi,ba zee ba har moona da sauran ‘yan matan dake dakin baki suka bude gaba daya Action dinsu yadawo kan ya jummai sidai ba mai iya tankawa sai binta da ido kadai,,zee kuwa miqawa Sameeha wayar tayi tabita da kallo.
Amsa Sameeha tayi hade da sallamar da tini ya jummai ta katseta da.
Maza² maza ki hanzarta kiran SÂMÊÊR ki fada masa mu ba qananun yara bane bakuma sa’anninsa bane da za’adinga yimana yawo da hankali Ana Raina Mana wayo ki kirashi Sameeha ya fada miki gidan da zamukai kayanki Dan rashin mutunci yabada key yace ga inda za’akai kaya sai bayan munje muga gida agarqame an chanja mukuli shin meyake nufi damu tun kan haqurina ya qare ki sanar masa mu ba yara bane kinjini,naji ya jummai zan Kuma kira shi insha Allah,ke yanzu zakifa kira ba anjima ba danni jira nake naga iskancin nasu ina zai qare wallahi inbaki kirashiba zan wanke sayyadata nayi gidansu (drt) ba abinda ya shafan,,wallahi zan kirashi ya jummai yanzun nan ma kuwa,,nasan halinki ne da shegiyar kunyar dazata cuceki Sameeha kinsan nawa halin dai ko basai anfada miki ba,Allah zan kirashin,dif ya jummai ta kashe wayar ta juyawa ta fuce daga dakin,safgarsu ‘yan matan sukacigaba dayi saboda sanin halin masifa irinta ya jummai abu Dan qarami zata maidashi babba ba Wanda yakawo wani abu har Sameeha dake kiran Sameer ahalain yanzu.