HAUSA NOVELSURBAJO Complete Hausa Novel

SURBAJO Complete Hausa Novel

suko sauran jamaar dake gurin tafi kawai suke musu masu daukarsu hoto nayi har suka karasa gurin zamansu zaunar da surbajo yafarayi sannan shima yazauna
surbajo kara rufe fuskarta tayi da mayafinta sabida tasha kunya daukota da alameen yayi daurewa kawai tayi tabarshi yadaukota dan tasan intace dakanta zata tafi faduwa zatayi

nanfa aka shiga gabatar da abinda yakaisu gurin inda MC yabukaci da ango yabude fuskar amarya batare da Bata lokaciba yabude fuskar surbajo

innalillahi wainna ilaihirrajuun itace kalmar da aisha ke furtawa dan ta gigice da ganin kyau irinna surbajo hawayene suka fara biyo fuskarta na bakin ciki dasauri Zuly tasharemata gudun kar wasu sugani rarrashinta suka shigayi amma kosu Sun jinjina dakyau irinna surbajo

hankalinta besake tashiba seda taji ana Kiran ango da Amarya sufito su yanka cake

duk abinda ake fadi da turanci akeyi kuma surbajo batajin turancin alameen ne yamike sannan yakamo hannu surbajo yamikar da ita suka nufi gurin cake din dakyar surbajo take tafiya sabida gudun karta sha kasa duk da de rabin jikinta na jikin alameen
tafiyar Tata seta karamata kyau dan wasu dauka sukayi yanga takeyi harsuka karasa gurin cake din alameen besaketaba koda suka tsaya zagayo da hannunsa yayi ta kugunta yariketa ahaka suka yanka cake din aka tafa musu MC yace Amarya taba ango abaki cikin harshen turanci
surbajo batajiba alameen ne yaradamata akunne waigowa tayi tana harararsa akan yace tabashi abaki shikuma yana murmushi wayyo jamaa zokuga yadda wannan kallo da surbajo tayi yakoma na so da kauna ga alameen yanata murmushi

yanko cake din surbajo tayi tanufi bakin alameen kara rungumeta alameen yayi ta kwantar da kanta a kirjinshi ahaka tasa mishi cake din abaki huuuuu kawai mutane ke fadi dan wasu liki suka fara zuwa suna musu agurin dankoni Sun burgeni
shima alameen ahakan yabata cake din tana kwance ajikinshi

bayan sunkoma gurin zamansune aka bukaci ango yayi Godiya ga jamaar dasuka taru dominsu nan alameen yayi jawabin cikin harshen turanci bayan yagama aka bukaci Amarya tayi itama alameen ne yafada mata abinda MC yace yakara dacewa tayi da hausa kuma don Allah karta dunga sako aradu à maganar murmushi tamasa Wanda yadauki hankalinsa sannan taamshi loudspeaker tafara magana cikin harshen filatanci
wow bakaramin burge mutane tayiba danko babu Wanda yayi zaton batajin turanci
bayan tagama ne akabukaci ango da Amarya su fito fili su taka
alameen ne yarukota suka fito filin yana rungume da ita aka samusu wakar da Sani slowly yamusu ta auransu suka fara takawa a hankali nanfa kowa yamike yafara yiwa ango da Amarya liki

aisha kuka take harda majina n’a bakinciki da sauri aminanta suka fitar da ita daga cikin hall din gudun karsuyi abin kunya
kai tsaye gida suka nufa da ita suna bata hakuri itako fadi take wayyo Allah alameen yakasheni yacuceni yarasa wacce ze auromin amatsayin kishiya se wannan gogaggiyar Yar bokon???? nabani ni aisha
sude hakuri suke ta bata

acanko ango da Amarya ne keta cashewa
baa tashi ataronba se goma nadare

suna dawowa aka sa surbajo tayi wanka aka shiryata cikin shigar alfarma aka nufi gidan mijin[truncated by WhatsApp]
????????????????????????????????????
*SURBAJO*
????????????????????????????????????

Zahra Muhammad mahmud

Zahramuhammadmahmud.blogspot.com

*page 31-32*

Ankai amarya Lfy inda dangin mahaifiyarta suka kara yimata nasiha game da zaman gidan miji itade surbajo se kuka takeyi

Kamin goma nadare kowa yawatse anbarta ita kadai Bilkisu ce tace mata takulle kofarta karta bude se intaji alameen ne ayko haka tayi kulle kofar tayi duk da bata iyaba seda bilkisun takoyamata

Gefen gado tasamu tazauna tadunga bin dakin da kallo irinna kauyanci komai yamata kyau sede ita wasu abunma batasan menene shiba

Siket da rigane ajikinta nawani material purple colour semayafin data rufa dashi fari takalmin kafarta ma farine kanta ba dankwali sede farin ribom daaka kama mata gashi dashi
Mikewa tayi tacire mayafin dan tagaji tunda aka fara bikinta take rufa mayafi to itade yau tagaji shiyasa tacire

Falonta tadawo tazauna akan two sitter sanyin AC naratsata komai na falon yaburgeta

zamanta bajimawa taji ana nurking din kofar mikewa tayi taleka ta ramin da Bilkisu tace tadunga lekawa
Alameen tagani tsaye shikadai bude kofar tayi takoma gurin zamanta tazauna
Da sallamarsa yashigo
Suman tsaye yayi lokacin dayayi arba da surbajo tamasa kyau sosai musamman gashinta daya zuba har gadon bayanta bakikkirin se shining yakeyi

Ledar daya shigo da ita yaajiye sannan yasami daya daga cikin kujerun yazauna

surbajo amare kallonshi kawai takeyi ba um ba umum shima itadin yake kallo murmushi yayi yace baby na babu ko gaisuwa irin wannan shan kamshi haka konayi laifi ne
murguda baki tayi tace yoto shikenan sokake insaki baki inta zuba agabanka kaidin daba kunyace gareka ishashshiyaba yanzu kace zaka daukeni kamar wata yarka to aradu kakiyayeni kajide nafadamaka tafadi Tana Kara daure fuska ita ala dole batason raini
dariya zancannata yabashi babu abinda yake burgeshi da ita irin son girmanta

mikewa yayi yakoma kujerar datake kai dasauri tamike tana shirin barin gurin cikin zafin nama yarikota tafado kanshi
Riketa yayi tayadda bazata kwaceba sannan yace baby na Wlh bakida kunya ke kodan irin kukannan da amare keyi in antafi anbarsu bakiyiba Dan mayafin dasuke rufe fuskarsu dashi shima bakiyiba kin yiwa ango magana dawuri se ansiyi baki shima duka bakiyiba se rashin kunya kikemin to ki kiyayeni ko yanxu nayi Maganin rashin kunyar taki yafadi yana shafo gashin kanta
Surbajo kokarin mikewa takeyi Amman yahanata ayko budar bakinta se cewa tayi hddijan amma aradu kado akwai raini yo inbanda abunka ko kukan nakeyi aka kawoni gidannan me shegen kyau ay aradu nadena kukan kuma wannan kayan kyalekyalen duniyar inna rufe idona ay bazan gansu da kyauba kuma dakake cewa nayi magana da wuri badole inmaka magana da wuriba gudun kar kace zaka lashemin bakina kamar tsohon Maye ni wallah narasa mekakeji acikin lashewa mutane baki kallonshi tayi sannan tace Don Allah kado mekakeji inkana tsotsewa mutane baki batagama fadin mezata fadaba yahada bakinta danashi yashiga kissing besaketaba seda yaji dakyar take numfashi kallonta yayi yaga jikinta yamutu murmushi yayi yace baby to kinji abinda nakeji inna lashewa mutane bakin

surbajo baki yamutu mikar da ita yayi suka shiga kitchen dinta dake falonta yadauko plate da cup suka dawo falon ledar daya shigo da ita yadauko yajuye naman kaza a plate din sannan ya tsiyayamusu fresh milk a cup yamatso dasu gabanta wayyo surbajo idonki idon nama ay tuni ta watsake daga kasalar da yasamata takai hannu zata dauki naman caraf yarike hannunta yace au ci zakiyi batare danamiki tayiba wani kallon banza tawatsamasa sannan tace aa kallonshi zanyi kamar yadda kaima naga kanayi
murmushi yayi yace inde zakici namannan to akwai sharadi inde kikaci sekin biyani ko ajikinta tace inde biyane me saukine zanbiya koma menene bani naci murmushi yayi sannan yamikamata

seda taji takoshi over sannan tahakura da naman sannan tashanye cup biyu na fresh milk din

mikewa alameen yayi sannan yamika mata hannu takama yadagata toilet suka nufa brush yadauko yamiko mata bayan yasa maclean kallonshi tatsayayi danbatasan amfaninshiba mamakine yakama alameen ganin surbajo batasan brush ba Amman bakinta baya wari kwatantamata yadda zatayi yayi wayyo shazumamu aytana gogawa taji zakin maclean tas tashanye kumfan hankalinta kwance tamika masa brush din yakaro mata wani
Kobe tambayaba yasan shanyewa tayi dariya yashiga Yi sannan yasamata wani yacemata inde tasake hadiyewa mutuwa zatayi Dan yaganota mutuwace kawai kebata tsoro ayko bata sha dinba duk da ranta naso haka tadunga zubarwa har suka gama suka dauro alwala suka fito

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button