TAKUN SAAKA COMPLETE HAUSA NOVEL

TAKUN SAAKA 12

 *_Typing????_**_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

_________________________

*_Chapter Twelve_*

…………..Oho su bama su san sunai ba. Dan koda suka fice a gidan babu wanda yay koda ambatar sunansu Abba ne balle su nuna sun damu da al’amarinsu. Asibiti suka nufa kansu tsaye. Inda sukai tozali da sanyin idaniyarsu da ke zaman jiran isowarsu. 

        Cike da ɗunbin farin ciki duk suka baibayeta kowa na jera mata tambayoyi game da jikinta da yanda takeji kuma. Komai bata iya ce musuba. Sai murmushi da take musu hannun Hibbah da Ammar a cikin nata tana kallon ciwukan jikin Ammar din. Da sauri ya ce,

        “Karki damu Ummi naji sauƙi. Kema ALLAH ya baki lafiya ki cigaba da mana tuwon dawarnan naki da bama son ci”.

      A tare suka kyaƙyale da dariya, Murmushin Ummi ma ya sake faɗaɗa ta kai hannu ta shafa fuskarsa. Hannun Hibbah ta kamo ta maida saman tata fuskar. “Ummi nice auta ni zaki shafama fuska ba wannan garjejen mutumin ba”.

     Ranƙwashi Ammar ya bata akai. Ta dafe kan da sauri tana sakin karamar ƙara. Ammar ya mike da ga inda yake zaune yana mata gwalo.

       “Yaya Umar ka ganshi ko?”.

Harar Ammar Yaya Umar yayi. “Kai wai miyasa baka rabo da zalunci ne. Ko wannan rankwashin da kake mata ma ya hana girma ai taita zama kamar ƴar cilikowa tana addabar mutane da ɗaukar magana”.

       Dariya duk suka tuntsure da shi baki ɗaya. Ransu fes da farin cikin tashin Umminsu. gashi doctor ma ya sanar musu nan da kwana uku zasu sallameta taje gida ta cigaba da shan magunguna. Dan dama irin aikin nata mai sauƙi ne inhar an dace da yinsa bisa nasara.

         Su suka taimakawa Ummin ta tashi suka jingina mata filo. a tare suka haɗu su duka suka ringa bata abinci duk da Hibbah na isarsu da rigima da rinto. Dan a layi aka dinga bi har Ummi tai musu nuni data ƙoshi. Sai da tasha maganinta sannan sukai mata sallama domin tafiya wajen aiki aka bar mata Hibba da Ammar. Dan su sai ƙura ta lafa zasu koma school musamman ma Hibbah.

       Kafin su wuce sun biya office ɗin doctor daya bukaci ganinsu. Bayan sun sake gaisuwa da shi da nuna jin daɗinsu akan nasarar jikin na Ummi ya shiga musu bayani akan wani bawan ALLAH yazo ya biya kuɗin aikin Ummi ɗin duka. Dan haka zai dawo musu da nasu kuɗaɗen insha ALLAH.

      Cikin mamaki suke tambyarsa wanene hakan?. Ya sanar musu shima dai bai sani ba kai tsaye. Dan ansha irin wannan taimakon batare da sunsan ainahin wanene ba. Amma kuma bayan hakan ma wani ma ya sake bada kaso ɗaya bisa uku na kuɗin aikin harma ya shiga ya duba Ummi. shima kuma dama yakanyi hakan a wasu lokutan. Yasan kuma zasu gansa suma kafin a sallami Ummi ɗin dan ya fahimci a yau kawai kamar har sabo ya shiga tsakaninsa da Ummi ɗin.

      Sosai abubuwan suka basu mamaki, amma sai suka watsar da mamakin sukacema doctor a maida musu kuɗin su da kansu insha ALLAH zasu biya kuɗin aikin mahaifiyar tasu basa buƙatar kowa. Cikin nasiha ya nuna musu hakan ba daidai bane. Sam babu ƙyau maida alkairi baya musamman irin wannan. Suma bawai sun biya bane domin sunga sun gaza. 

      Dole suka hakura suka amsa tare da yin addu’a ga masu biyan. Da ga haka suka fito domin nufar wajen aikinsu……..

_________________________________

            A ɓangaren yaran master kam, tun suna zuba idon zaman jiran dawowarsa har suka fidda rai. Dan sun fahimci dai yayi nisan kiwo. Badan sun so ba dole suka tashi sukai shirin barci duk suka kwanta kowa ransa da addu’ar ALLAH ya dawo musu da shi lafiya.

      Sukan damu idan yay fitar dare. Saboda sunsan shi sam bayasan yawon dare. Ko su duk aikin da zai sakasu inhar magrib tayi ya haƙura kenan. Sai ko idan ya zama dolen dole. Amma da anyi sallar isha’i basa ƙara fita sai ta lalura.

      Koda suka tashi sallar asuba ma basuji motsinsa ba, haka sukai alwala suka fita, dan sunsan duk inda massallacin da ya tadasu yake zasu ganosa a layin insha ALLAH. Sai ga shi fitowar tasu ma ta sakasu fahimtar a ina suke. Ashe bayan layin gidan da suka baro jiya ne. Har cikin ransu suna jinjinama boss ɗinsu, saboda matuƙar wayonsa da basirar iya takun rayuwa. Komai babu wanda ya faɗa suka adana a zukatansu har sukaje salla suka dawo. Sanin yace ƙarfe bakwai da rabi zasu bar gidan yasa basu kwanta ba suka tattare abinda suka ɓata.

         Suna tsaka da kimtsawar ne kusan 6:43 sai gashi ya dawo. Kallon mamakin ta inda ya shigo suka shiga masa. Dan sudai basuji alamar buɗe ƙofar gidan ba. Hasalima sakata suka saka mata ta ciki, dole ne sai yayi musu knocking sunzo sun buɗe masa.

       Sarai ya fahimci ma’anar kallon da suke masa, amma sai ya basar abinsa. Hakan yasa suka shiga gaishesa da masa barka da dawowa bayan Musbahu ya tashi ya amshi bag ɗin hannunsa. 

            Hannu kawai ya ɗaga musu, kafin ya fara magana a taƙaice yana nuna bag ɗin da ya shigo da ita, “Gaba ɗayanku zakuyi amfani da kayan cikinta ne, dan a wannan gaɓar magana ake ta kuɗin baƙine ango ya kawo ku kwana anan”. 

         Cikin girmamawa suka shiga amsa masa suna murmushi. Yayinda shi kuma yay shigewarsa ciki. Zaidu ne ya fara kwashewa da dariya yana faɗin, “Abokan ango waye angon to a cikinku?”.

        Salis ya nuna kansa yana wani buɗe hannaye irin eh????????. Hararsa Habib yay da taɓe baki. “Banza. Kana ɗan yahoo ubanwa zai baka ƴarsa, wataran shima ka yashe masa asusunsa”.

      Sanin boss na gidan ya sakasu fara dariya suna tarewa da hannu. Salis da ke harar Habib ya ce, “Da yake ma talle bataima audi gori duk tafiyar ɗaya ce. Ta wani fanninma gwara ni. Kuma tunda kace haka kwanan nan zakaji na zama ango ɗan baƙin ciki yahoo boy”.

         Duka Habib ya kaima Salis ɗin ya kauce yana masa gwalo. Rabi’u yace, “Kai kai ku tsaya kuji. Ni fa da boss yay maganar ɗaurin auren nan sai naji inama irin shine za’a ɗaurama auren. ALLAH na ƙagu naga mai tsaurin idon da zatai wuff da master”.

        Dungure masa ƙeya Musbahu yayi da saurin cewa, “Wanan saɓon naka banajin zai tabbata a gidan nan. Inko ya tabbata to lallai sai mun yashe asusun tsohonta tas inaga abiya sadaki da kuɗin auren nata”. 

     Duk yanda sukaso matse dariyarsu hakan ta gagara, tuni suka shiga ƙyalƙyalewa harda masu faɗowa ƙasa da ga kujera. Khalid ne ya fara farga da Master da tun dariyarsu ta farko ya fito. Tsaye yake a jikin ƙofar ya harɗe ƙafafu da hannayensa a ƙirji kawai ya zuba musu idanu. Da sauri Khalid ya zunguri Rabi’u da ke kusa da shi, babu shiri shima ya gimtse tasa dariya yana zungurin Zaid. Shima Zaid da sauri ya haɗiye tasa yana mintsinin kafar Idris da ke kusa da shi. Musbahu da shima idonsa ya kai yay azamar haɗiye tasa yana rarrafawa zai ɓoye bayan kujera. Habib da Salis da basusan anayi ba kam sai ƙara tuntsurawa suke. Salis yace, “Ni why bana tunanin boss zai wani iya soyayya, dan ita tayi yamma shi yayi gabas. Inagama sai munyi karo-karo wajen badashi sadak……”

1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button